ABDUL JALAL PART 2

ABDUL JALAL PART 2

Yauma duk da tarin farinciki da Jalila ta tsinci kanta a ciki yau, amma bacci ya kauracewa idanuwanta, jikinta na bata Jalal yakoma shan giya, da kyar ta samu bacci ya dauke ta, amma mafarkin Jalal a cikin wani yanayi na shaye2, yasata farkawa, gabanta na wata irin mummunar faduwa, wayarta ta dakko ta duba karfe biyu da rabi na dare, ga shi ita ba lambar Jalal ce da ita ba, tarasa mema zatayi gallery dinta ta shiga tana dubawa, tsofaffin ajiyayyun hotunan ta take dubawa, hotunan da sukayi da Jalal tun wani zuwa da Hanan sukayi, haka taita kallon hotunan, a haka har ta kawo kan hotunan birthday dinsa, cin karo tayi da wani hoto da’akayi harda Hannah a ciki, take gaban Jalila ya fadi, dan sam ta manta da Hannah, kuma barin Hanna ba tareda daukar wani mataji ba tamkar kashe maciji ne ba’a sare kansa ba a rayuwar Jalal.
A hankali ta ajiye wayar, ta sakko daga kan gadon ta shiga toilet tayi alwala tazo ta tada salla.

Ranar litinin Jawwad shima yayi nasa shirin tsaf domin tafiya Gurin nasa aikin dake birnin tarayya, Abba yayi masa Nasiha sosai tareda sa masa Albarka, haka ma bangaren Maama, tayi masa Addu’a da sa Albarka, dukda marin da Maama tayi masa akan Naja, hakan besa ya nuna mata har yanzu yana fushi ba, Bangaren Jalila kuwa har kuka tayi, saboda zatayi kewar Yayan nata sosai
Abba yace “Jalila kina kuka dan zeyi tafiya, kuda kwanan nan zeyi Aure gaba daya zasu bar gidan, su barki seke kadai”
Kara fashewa da Kuka Jalila tayi, Nana tace “Abba ka gani ko? Wannan yar taka ta fiye shagwaba wallahi”
Jawwad yace “haba babyn Abba, sekace ba jaruma ba, zan dawo ai kidena kuka”
Sukayi ta tsokanarta ita kuwa dagaske take kukanta.
Haka sukayi sallama da Jawwad shima yakama hanyar tafiyar sa.

Jalal yana waya da daddyn sa sosai, sannan suna waya ds Jawwad, suna shirye2 yadda biki ze kasance a tsakanin su.
Abban su Jawwad yana kasuwanci ne a tsakanin Kano da lagos, dan haka in yaje suka haduwa da Jalal.

Jalila Nason sanin halin da Jalal yake ciki, amma babu wata hanya da zata san hakan, dan haka taketa kokarin boye damuwarta.

Maama Allah ya temaketa Abba ya sakko daga fushin dayake da ita, sannan tunda abun nan ya faru Su Yaya mairo ko a waya basu kara neman Maama ba, abun ya dameta sosai dan haka ta shirya da kanta taje gidan su.
Tunda tayi sallama suka amsa suka shareta suka ki kulata, ita tayiwa kanta gurin zama, ta gaida Yaya mairo amma taki kulata, seda ta bata ‘yan kayan data saba kaimusu, shine Yaya mairo ta dan saki rai suka gaisa, Naja ta gani a lullube tana bacci, Maama tace “Yaya, Naja ba lafiya ne?”
Kafin Yaya mairo ta amsa Naja ta fara magana cikin maye “Ni… Ni.. Ba… Wallahi baaaaani da…. Da lafiya, Shiyasa naiwa kaina caaajiii, baaaa danki yaki Aure na baaaaaa, wallahi….
Cikin tsawa Yaya mairo tace” yimin shiru dan ubanki, ciwon mara take, shine ta sha magani fiye da ka’ida”
Gaba daya jikin Maama yayi sanyi saboda babu tantama Naja maye takeyi. Shiru tayi takasa cewa komai, Naja ta cigaba da surutai, can kuma ta kwalla uwar kar, sega jini na gudu a tsakar dakin daga karkashin Naja.

Se bayan la’asar su Jalila suka gama lectures ta gaji matuka, haka kurum tun suna lectures takejin gabanta yana faduwa, da kyar ta tsaya aka gama lectures ta fito, danma manu direba ne yaje dakko ta daga school, abunda yabata mamaki be wuce ganin motar Hannah a gabansu ba, tana tsala gudun wuce sa’a, kuma da alama layinsu zata shiga, Jalila tasa Manu direba yayi parking a farkon layinsu, ta sauka ta shiga layin da kafarta, aikuwa tana zuwa taga Hannah tayi parking din motarta ta shiga gidansu Jalal, Jalila batayi shawarar komai ba ko tunani tabi bayan Hannah zuwa cikin gidan.

Masu kirana a waya please am sorry, ku dinga min magana ta what’s App, ina kokarin duba messages, amma kira musamman idan ina aiki, bana samun daga bakuwar lamba am sorry.
Ina godiya da kulawa.

Share please
I want comments not stickers or just thanks
Daga alkalamin Aysher cool
????️????️????️????️????️????️????️????️????️????️

What’s app only 07063065680.
Watpad @Ayshercool7724

.
????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????

              *ABDUL JALAL*

         _Story, writing and edited _

                        By
              AISHA HUMAIRA
              ( _Daddy's girl_) 

PERFECT WRITER’S
ASSOCIATION????

(???????? ????????ℕ’???? ℙ????ℝ????????ℂ???? ???????????? ????????’ℝ???? ????????????????????????, ????ℝ????????ℕ???? ????????ℝ ???????????????? ???????? ???????????????????????????????? ????ℕ???? ????ℕ????????ℝ????????????ℕ ????????ℝ ℝ????????????????ℝ????????)

/https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/

P.W.A✍️

        PART 2         
                      _PAGE  4️⃣6️⃣99

Bismillahirrahmanirrahim, da sunan Allah me rahama me jinkai, Allah yakara tsira da aminci ga shugabanmu Annabi muhammadu salallahu alaihi wassalam.
Bayan haka bazan gajiba da mika gaisuwata da godiya ga yan uwa da abokan arziki ba, bayan haka
Banyarda a juyamin littafi ba ko amfani da wani bangare ba tareda izinina ba.
Domin gyara, shawara ko sharhi, za a iya tuntubata akan what’s app number dina
07063065680
Or email address @ www.humaira17@gmail.com
Watpad @Ayshercool7724

         _MY FIRST NOVEL _

Hannah gaba daya kanta ya kwance bata taba tsammanin abubuwa zasu kwabe mata haka ba, wai me yakawo Jalila a gabar da takeso kulla wannan gadar Zaren, da komai ya tafi dai2, Jalal baze taba tsallake shirinta ba, wayarta ce ta fara ringing amma Hannah tayi biris da ita, an kirata ya kai sau shida sannan ta dauka a fusace tace
“dalla waye haka?”

“ke dalla zizo ne, za’a miki abun Arziki amma kina wa mutane hauka, ki tattara kayanki tun wuri kisan inda dare yayi miki wallahi”

“kamar yaya? Saboda me?”

“Allah ne yake sonki da rahama, Wallahi Jiya na raka wani me gidana Unguwa, ya tsaya gurin wani me gidansa dan sanda ne babba, naji me gidannan sa yana waya, bayan ya gama yake gayawa maigidana, wai wani yabada izinin a kamo masa wata yarinya a ajiye masa ita har seta haihu, ta yaye yaron ya shekara biyar sannan a saketa, idan kuma ba tada ciki aita ajiye ta kar a saketa, kuma yadda mutumin nan yake kwatantawa na gano kaman kece, ban gasgata hakan ba se jiya da naje palace, wallahi cikin dare ‘yan sada sukazo nemanki, dan haka in kin san da wata cakwakiyar da kika kulla tun wuri ki kama gabanki wallahi “

Hannah ta hadiyi wani mugun miyau ta ce
“Shikenan nagode sosai zizo”

Ta katse wayarta ta mike tsaye tareda fadin
“kan bala’i banga ta zama ba, ni Jalal zewa haka? Wallahi yadda ya fada din nan aka kamani kashina ya bushe, Amma wallahi in yasan besan wata besan wata ba, ni zesa akama, nizewa hauka? Banga ta zama ba”
Ta mike da sauri ta janyo Akwati tafara zuba kayanta tanayi tanayin surutai.

Jalila tattar komai ta ajiye a gefe ta maida hankali akan karatunta, dan yadda takeji in bata dena yawan damuwar nan ba zuciyarta zata iya bugawa, sosai Maama ta rage wannan gabar da takeyi da Jalila, tana dan sakewa da Jalila har suyi hira, suna shirye shiryen yadda biki ze kasance, Jalila bata taba nuna mata tana fushi da ita akan abubuwan da tayi mata a baya ba, Maama har mamaki takeyi, wani lokacin yanayin halinta daya da Jawwad, ka musu laifi amma su nuna basu san kanayi ba, ita kanta Nana tayi mamakin yadda Maama tayi saurin karaya da Al’amarin da yafaru.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122 123 124 125 126 127 128 129Next page

Leave a Reply

Back to top button