ABDUL JALAL PART 2

ABDUL JALAL PART 2

Koda Jalal ya shiga gida, part din Daddy ya tafi, yana zuwa kaman wani karamin yaro ya tarar da daddy yana aiki akan system, Mummy na gefe suna hira, yana zuwa ba tareda ya cewa kowa komai ba ya zauna kusa da daddy ya kwanta akan cinyar sa yayi shiru kaman mara lafiya.
Daddy yace “Jalal lafiya kuwa?”
Jalal yace “daddy Anmin screening da interview, an turani Lagos zanyi wata uku acan, Jawwad ze tafi nasa gurin Aikin next week Monday “
Daddy yace “Eyya shiyasa ka damu haka? Kayi hakuri kaji yaron kirki, yasa haka shine mafi Alkhairi a gareku”
Mummy tace “nifa gaskiya bana son wannan aikin da zeyi, meya nema ya rasa da ze tafi wani yawo daban”
Mikewa Jalal yayi tareda yin tsaki yabar dakin, ya koma Part dinsa, koda ya koma ya sauya kaya ya kwanta domin yayi bacci amma abu ya ga gara, juyi kawai yakeyi idonsa ya bushe, ta shi yayi zaune ya kurawa teddy dinta da carbin da ta bashi ido, abubuwa da dama na masa yawo a kwakwalwa, Espicially lokutan da sukeyi tare, yana kallon teddy ya tuna lokacin da take rike da teddy ga sweet abakinta tana dariya, yana tuna tsiwarta, kwarin gwiwa, tausayinta, nasiha da murmushinta, ya tuno maganganun Abba dazu wai za’a Aurar da ita ga wani AHMAD!!! gaba daya yaji kansa yana juyawa, yazama dole ya nisanta kansa da duk wani abu da zazesa ya dinga tunata, Baze manta Alkhairan ta ba, tunani yakasa barinsa dan haka ya mike ya fice daga gidan gaba daya.

Jalila ma juyi ta dingayi tana tunani da tausayin Jalal, tabbas Jalal abun tausayi ne, yana bukatar me jansa a jiki musamman yanzu da Jawwad zeyi nesa dashi, tana fargabar yakoma shaye2 kamar da, Amma a yanzu bazata iyayi masa komai ba, dan gudun kuma fadawa mummunan zargin da mahaifiyarsa ke mata. A takaice se gefin Asuba bacci ya dauke ta

Jalal be dawo gida ba se Asuba, yaje club ya kwana yana shan giya, seda yayi mankas, da Asubar ma bata sake shi gaba daya ba ya dawo gida cike da maye.

Yau tun bayan da Jalila ta dawo daga school, tayi waya da Ahmad ya gaya mata yau zezo, dan haka se shiri take domin tarbarsa.

Jalal tunda giyar ta sake shi, yai wanka ya shirya kayansa daze bukata a Akwati, yaje cikin gida yai sallama da Daddy, yaita saka masa Albarka tareda fatan Nasara, tunda Ilham taji batun yasamu Aiki ta hanyar Jalila, kuma zeyi wannan tafiyar akan Aikin, hankalin ta ya tashi, wai se yayi wata uku acan, to in baya nan tayaya zata cigaba da gudanar da aikinta akansa?.

Karfe biyar yagama shirinsa, saboda Jawwad ne ze kai shi Airport, ya sa hannu ya dauki teddyn Jalila da Alqur’anin nan da kuma carbin data bashi, ya nufi gidan su Jawwad, saboda so yake ya nesanta kanshi da dukkan wani abu daya shafe ta.

Amma abunda yayi tozali dashi bayan ya shiga gidanne yasa yaji tamkar jijiyoyinsa sun dena harba jini yadda yakamata.
Autar Ummi wato Jalila ya gani tayi kwalliya cikin wani dankareren leshi, tayi kyau matuka suna hira da Ahmad, kai da gani suna cikin shaukin soyayya, Jalal yaji wani Abu ya tsarga masa tun daga kansa zuwa tafin kafarsa, kirjinsa yai masa nauyi matuka A hankali yafara jan kafarsa dayake ji tamkar ba nasa ba ya nufi inda suke.
Idonsa Akan Jalila har ya karasa inda suke, Jalila ce tafara daga kai tana kallon sa, gani tayi kamar ya danyi rama, yana zuwa Ahmad ya miko masa hannu da nufin su gaisa, kawai Jalal ya daga masa hannu, ya zubawa Jalila idanunsa da sukayi jawurr wanda yasa hantar cikinta kadawa,
Ya ajiye mata Alqur’anin, a gabanta da teddyn, ya juya ya nufi hanyar fita

Masu kirana a waya please am sorry, ku dinga min magana ta what’s App, ina kokarin duba messages, amma kira musamman idan ina aiki, bana samun daga bakuwar lamba am sorry.
Ina godiya da kulawa.

Share please
I want comments not stickers or just thanks
Daga alkalamin Aysher cool
????️????️????️????️????️????️????️????️????️????️

What’s app only 07063065680.
Watpad @Ayshercool7724

????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????

              *ABDUL JALAL*

         _Story, writing and edited _

                        By
              AISHA HUMAIRA
              ( _Daddy's girl_) 

PERFECT WRITER’S
ASSOCIATION????

(???????? ????????ℕ’???? ℙ????ℝ????????ℂ???? ???????????? ????????’ℝ???? ????????????????????????, ????ℝ????????ℕ???? ????????ℝ ???????????????? ???????? ???????????????????????????????? ????ℕ???? ????ℕ????????ℝ????????????ℕ ????????ℝ ℝ????????????????ℝ????????)

/https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/

P.W.A✍️

        PART 2         
                      _PAGE  4️⃣4️⃣97

Bismillahirrahmanirrahim, da sunan Allah me rahama me jinkai, Allah yakara tsira da aminci ga shugabanmu Annabi muhammadu salallahu alaihi wassalam.
Bayan haka bazan gajiba da mika gaisuwata da godiya ga yan uwa da abokan arziki ba, bayan haka
Banyarda a juyamin littafi ba ko amfani da wani bangare ba tareda izinina ba.
Domin gyara, shawara ko sharhi, za a iya tuntubata akan what’s app number dina
07063065680
Or email address @ www.humaira17@gmail.com
Watpad @Ayshercool7724

         _MY FIRST NOVEL _

Shiru Jalila tayi ta kalli kayan daya ajiye mata sannan tabi bayansa da kallo har ya fice daga gate, din shiru tayi ta tafi tunani, Ahmad yace
“my queen, meya farune?”
Da sauri ta dawo hayyacinta tace “bakomai fa”
“Amma waye wanan?” ya tambayeta yana me kureta da ido, ta dan sauke numfashi tace “Yaya na ne”
“Yayanki queen, ba Jawwad ne kawai Yayanki ba?”
“Abokin Yaya Jawwad ne, dan haka Yayana ne kawai”
“Amma babu wani abu a tsakanin ku kuwa?”
“Meyasa kake min wannan tambayar? Ko baka yadda dani bane?”
“Ahh haba waneni ince ban yadda da gimbiyata ba, ina so ne in tabattar da abunda ke tsakaninku, dan da idonsa yana shaye2”
Ba karamin haushi maganar Ahmad ta bata ba, kenan shima yanayi, in ba yanayi ba, ba abunda idon Jalal yayi dayake nuna yana shaye2, dan haka tace
“baya shan komai, kawai bashi da son magana ne, baya kula mutane”
Kyaleta Ahmad yayi yaga alamar bata son zancen suka cigaba da hira, Jawwad ne ya fito ze wuce su Jalila ya tsaya suka kuma gaisawa da Ahmad dayake dazu sun gaisa, Jawwad yace “to sirikina zan iya ce maka se anjima, ni zan tafi kai Jalal airport ne”
Da sauri Jalila tace “Ina zashi?”
Jawwad yayi murmushi yace “Aiki mana, an tura shi Lagos, se lokacin biki inaga ze dawo, bari inje karyai ta jirana, kin san baya son jira, se anjimanku” Sukayi sallama da Ahmad ya fita.
Ahmad ya maida idonsa kan Jalila yace “Gimbiya naso a haďa bikin nan hada namu, na kagu in mallakeki”
Murmushi kawai tayi amma hankalinta baya kansa, tanata zancen zuci ne, dayaga haka yace “queen naga kaman Akwai abunda yake damunki, bari in tafi semunyi waya”
Ta mike ta rakashi har bakin gate sannan ta dawo ta zauna akan kujerun tana nazari
“At least yakamata ace sunyi sallama da Jalal, tayi masa nasiha, Amma bata tunanin zata iya kuma rabarsa ba saboda mahaifiyarsa.

Jawwad ya ga sam fuskar Jalal a daure take, babu alamar walwala ko fara’a, Jawwad yai masa magana yafi a kirga, amma ko daya be bashi amsa ba, dan haka ya kyleshi suka cigaba da tafiya a haka kaman kurame.

Gajiya Jalila tayi da zaman tunanin ta mike ta tafi cikin gida, Nana tana zaune a palour suna waya da Mahmud,
“Nana waike dan Allah ba kya gajiya da wannan wayar ne? Kuyita surutu tun ana fadar gaskiya se an koma fadan karya”
Nana taki kula ta seda ta gama wayarta sannnan tace
“waike Baby an gaya miki kowa irin kine me tsarin tsiya, ke yadda ba kya son yawan waya kowa ma hakane, ai a rana inji muryar Mahmud sau hamsin bazan gajiba, musamman mu da muke distance relationship, ai Ahmad din nan ma ban wani yadda kina sonsa ba”
“Inasonshi sosai, amma hakan bashi ke nufin a dinga uzzuramin da surutu ba”
“Hajiya Jalila, kyaji da shi dai”
Hanan ca ta kira Jalila a waya, ta daga tasa a kunnenta
“hello Baby, ‘yar uwata rabin jikina ashe Family dinmu daya Baby? Narasa inda zan sa kaina dan farinciki, dazu Abba yake gayamin kuma wai an kawo kudin Aurena da Haidar, Baby na rasa me zanyi dan farinciki”
Murmushi Jalila tayi tace “na riga ki ji ai, kiyi Azumi ki godewa Allah”
“queen na rasa inda zan saka raina dan farinciki, daddy yace zasuzo karbar kudin Nana, narasa yadda zanyi dan murna”
“haka Al’amarin ubangiji yake Hanan, yana juya komai yadda ya so”
“Hakane Queen, amma naji haushi da baza’a hada da nakiba, ni ina Jalal ne ma?”
“yaje interview din nan ai, an turashi lagos zeyi wata uku”
“Allah sarki bawan Allah, wallahi Jalila bana kaunar Aurenki da Abokin Yaya Yusuf din nan, in duniya da gaskiya Jalal ya kamata ki Aura”
Wani dogon tsaki Jalila tayi ta kashe wayarta, dan bata son Hanan ta bata mata rai.
Jalila ta mike har zata bar palourn taga Maama tazo ta wuce kitchen, gaba daya Jalila bata jin dadin yadda kowa ya fita harkar Maama, dukda abubuwan da Maaman tayi mata, Akwai lokutan da ta kyautata mata, dan haka taga be dace ta mata hukunci da laifin da take mata ba, dan haka tabita kitchen din, Maama na kokarin kunna gas Jalila tayi maza taje ta karbi lighter tace “Maama kawo in kunna miki, me zaki dafa?”
“barmin Abina zanyi”
“A’a Maama, tunda ba abunda nake ki barshi in dora miki”
Jalila ta karbi lighter ta kunna gas, dan jimm Maama tayi tana Kallon Jalila, yadda Jalilan ke Acting kaman Maama bata taba yi mata wani abu na bacin rai ba.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122 123 124 125 126 127 128 129Next page

Leave a Reply

Back to top button