ABDUL JALAL PART 2

ABDUL JALAL PART 2

Share please
I want comments not stickers or just thanks
Daga alkalamin Aysher cool
????️????️????️????️????️????️????️????️????️????️
What’s app only 07063065680

????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????

          _ABDUL JALAL (2020)_

   _Story and written by_
  AISHA HUMAIRA (daddy's girl) 

PART 2
PAGE 1️⃣7️⃣70

Bismillahirrahmanirrahim, da sunan Allah me rahama me jinkai, Allah yakara tsira da aminci ga shugabanmu Annabi muhammadu salallahu alaihi wassalam.
Bayan haka bazan gajiba da mika gaisuwata da godiya ga yan uwa da abokan arziki ba, bayan haka
Banyarda a juyamin littafi ba ko amfani da wani bangare ba tareda izinina ba.
Domin gyara, shawara ko sharhi, za a iya tuntubata akan what’s app number dina
07063065680
Or email address @ www.humaira17@gmail.com

    _MY FIRST NOVEL _

Ta dafa kafadar saudat “bakida damuwa zanyi meyuwuwa inga burinmu yacika, amma kisani dole abu daya yafaru, ko kiyi nasara, kokuma akasin haka” “hakane amma ni nafi sa ran nasara dan kome zefaru sedai yafaru”
“gara kidinga sawa ranki nasara da akasin haka, yanzu dai macigaba anjima, inada abunyi yanzu”
“to shikenan bari zan dan fita dama, sena dawo”
Saudat nafita khadija tabi bayan saudat dawani mugun kallo, sannan tayi kwafa “gaskiya Saudat bakida hankali, kekin isa inso abu kema kice kinaso, zakiga tsiya dake zanyi tarkon cikar burina, ita kanta Salma seta barmin Habib” ta sakeyin kwafa ta nemi guri ta kwanta.
Sati daya da kai Salma gidan habib, Saudat ta shirya taje gidan Salma, ba karamin tsinkewa Saudat tayi ba da ganin aljannar duniyar dake gidan Salma, gidane na alfarma kaman ba a Nigeria ba, ga shi an kashe masa kudi da kayan alatu, haka Saudat ta sake taita kallo tana video gidan dan ta nunawa Khadija, bangaren kayan Abinci ba a magana, tasamu kyakyawar tarba daga salma, ta karramata da kayan Abinci sukayita hira Saudat tace “Salma kawo in turamiki hotunan da nadingayi miki lokacin biki” ba musu Salma tabawa Saudat wayarta, tana cikin yimata turi ta faki idonta ta dauki lambar Mijin Salma wato Habib, haka suka dinga hira se la’asar sannan saudat ta tafi, saudat taso taga habib amma bata ganshiba salma tagaya mata baya gari.
Tunda saudat taje gida tana rawar jiki taje tasamu khadija tadinga nuna mata video gidan salma, gaba daya khadija ta rikice da ganin aljannar duniya, tabbas habib shine mijin daya dace da ita,
Daga nan ta nuna mata ta samo lambar Habib “khadija ga lambarsa na samo ta ina yakamata in fara”
Hanzarin me kike ne, ba tace miki baya gari ba, kibari se kaman nan da sati daya mana maybe lokacin ya dawo”
“anya zan iya jira har sati kuwa, nifa banki ace ko a satin nan a daura aure ba dan ba karamim so nakeyiwa gayen ba, kokuma ince nakewa dukiyarsa ba”
Khadija ta jinjina kai tace “to wai yazakiyi da kawarkine, in ta gane zaki aurar mata miji” tsaki saudat tayi “wayake tawani matarsa, ai ranar biyan bukata rai ba a bakin komai yakeba, indai buri zecika, to babu batun kunya da cin amana, inma ta gane ita tasani nidai fatana in ganni a cikin wannan daukar” “hmm Gaskiyar ki yar uwata, Allah ya ida nufi”
“Ameen khadija, ammafa in Salma tagane ba karamin hauka zatayu ba, dan tana masifar son gayen nan, gata da kishi kamar bala’i, amma tasamu dai dai da ita indai nice” murmushi khadija tayi
“gaskiya zata taro match kishi da hajiya Saudat” sukayi shewa gaba daya.
Kwana biyu da zuwan saudat gidan Salma, khadija ta shirya tun safe ta fita ashe wayar saudat ta dauka tun dare ba wanda yasani, ta fita ta cire sim din saudat tasa a wayarta ta dauki lambar Habib, sannan ta kakkarya layikan saudat ta zuba a kwata, sannan ta jefar da wayar tai tafiyarta, bata koma gida ba se bayan magariba yaje ta tarar anata jimamin wai barawo yashigo gida jiya da daddare yasace wayar saudat, ta shiga sahu akaita jajantawa saudat, saudat tabiyo khadija dakinta kaman tai kuka tace “wallahi khadija ba batan wayatane yabani haushi ba, rasa lambar habib itace ta konamin rai”
“don’t panic dear, karki damu, inkika canza waya seki kuma samo lambartasa, aibawani abu a ciki”
“haba khadija kinsan da yadda nasamo lambar nan kuwa idan nakoma mezance mata inkuma karbar wayarta, kuma kwata2 yaushe naje gidanta dazan koma” ta karasa maganar kaman zatayi kuka
“haba saudat kefa kikace ranar biyan bukata raiba abakin komai yake ba, amma kibari kaman in akayi sati biyu sekikuma zuwa, kinga ba wanda ze zargin wani abu”
Saudat ta kalleta “haba khadija har sati biyu, anya kuwa zan iya jurewa”
“Saudat idan kikabari matarsa ta gane zaki aurar mata miji to tabbas bazata kyaleki ba, gara kibi komai a sannu in lokaci yayi taji”
Saudat tayi nannauyar ajiyar zuciya tace “kuma kinyi gaskiya khadija, shiyasa nakeson shawarwarinki nagode sosai, bari anjima Mukhtar zezo se in sashi yakawomin wata wayar”
“eh hakan ma yayi kyau”
“hakane nagode bari inje inyi salla” tana fita khadija tai murmushin mugunta.
Khadija tasa kabir yasiyo mata sabon waya, me madannai tayi saving lambar habib a ciki, kullum safiya da dare seta tura masa zazzafan text messages da addu’oi , hakama da daddare zata tura masa bata taba kiransa a waya ba, shima kuma betaba biyowaba balle yaji waye. Amma habib yana mamaki wacece take turomasa wannan messages haka, shidai yasan ba Salma bace bata da wannan lambar, kuma tunda sukayi aure bata yimasa tex kamana yadda take masa kafin suyi aure, amma bari ya tambayeta ko itace take turo masa, salma na gaban mirror tana taje kai, habib yana kan gado a kwance ya kalleta yace
“my sweet lambobinki nawane?” kallonsa tayi “meya farune??”
‘No bakomai na tambayeki ne dai”
“fadamin gaskiya ko watace take kiranka ka zata nice” gabansa ne ya fadi ya kalleta, amma yakasa magana a hankali ta tako tazo ta zauna a kusa dashi tace
“yanaga ka tsorata, nafada dai2 kenan”
“A’ a kam kinbani mamakine kawai, daga tambaya kin canzamin magana, kaman kina zargina”
Tayi Ajiyar zuciya “Habib kada Allah ya nunamin ranar da wata mace zata dinga kiranka, amatsayin budurwarka, inaga a wannan ranar se zuciyata tayi bindinga, bazan iya jure ranar dazanyi sharing dinka da wata mace, inasonka habibi da’iman” seda cikin habib ya duri ruwa, amma ya dake yace
“I love you too hibbaty, karki damu zuciyata kekadai ce a ciki, zan rayu dake har zuwa karshen rayuwata” yai mata murmushi tareda yin kissing dinta a goshi, ta dora kanta akan kirjinsa tanata ajiyar zuciya, message ne yashigo wayarsa, yasa hannu ya dauka ya bude message ne na nuna tsantsar soyayya da kauna da khadija ke turomasa, sauri yayi yasa lambar a blacklist, ba tareda salma ta dago ba tace “habiby waye ya turomaka message?”
“Alert ne, kayan dana siyar aka turomin kudin” har cikin ranta ta yadda da abunda yace.
Haka khadija takuma canza layi tacigaba da turawa habib messages baji ba gani, abunne yafara damun habib kar by mistake Saudat tagani, gashi layinsa ne dayakeso wanda huldodunsa na kasuwanci duk akai suke da se ya cire layin ya yar, besan mezece ma Salma idan taga wannan messages dinba, dan Yasan halinta da mugun kishi, yanzu se cibi yazama kari, ba dan haka ranar ya yanke shawarar yakira yaji kowacece, da safe wajen karfe goma khadija tana kwance tanata tunanin habib tana kallon hotunansa, karamar wayarta datake kiran habib da itane tafara ringing, ga mamakinta taga Habib ne nannauyar ajiyar zuciya tayi tareda yin murmushi ta rungume wayar a kirjinta tanajin ringing din wayar harcikin zuciyarta, wayar tayita ringin harta katse bata daga ba taitajira koze kuma kiranta amma be kirata ba. Kusan kwana uku bekuma kiranta ba itamuma tacigaba da turamasa, rana ta ukun da daddare yakuma kiran wayar khadija seda ta kusa tsinkewa, sannan khadija ta tattara duk wata nutsuwarta ta daga wayar, tana dagawa kafin tayi magana a fusace yace “wai dan Allah wacece haka, kina nema ki hadani fada da matata meye hakane, karki kara turomin wannan rubbish din nagaya miki” maganganunsa sunyimata zafi, amma ta dake tace “ohhh masha Allah, zanyi bacci irin wanda bantabayiba yau habib, naji muryarka Ina sonka, kayi bacci me dadi kaman yanda zanyi cike da farinciki” tunda tafara magana gaba daya jikinsa ya mutu yakasa cewa komai, itama bata jira meze ce ba ta kashe wayarta, tace “Lallai Habib bakasan wacece khadija ba bazaka taba kufcemin ba tunda kayi gangancin kirana” khadija bata taba gajiyawa ba gurin yi masa aiken zafafan kalaman soyayya.
Yau sati biyu cif tacika da zuwan saudat gidan Salma, tun karfe goma na safe ta shirya, tazo tayiwa khadija sallama cewar zataje gidan Salma, ita khadija ta manta ma cewar sunyi da khadija yau zata koma gidan Salma, khadija ta dake taimata fatan nasara, bayan ta fitane ta dinga mata dariya. Koda saudat taje gidan me gadi yasanar da ita cewa masu gidan basanan sun tafi Abuja karfe 2narana zasu bar Nigeria zasu wuce Dubai, Saudat jitayi kaman ta dora hannu akai tayi ihu, tacewa me gadin “dan Allah yayana kozaka temakamin da lambar me gidan?” zare ido yayi “lallai da alamu kina da tabin hankali yadda tsaro yayi karanci zakice abaki lambar megida, to ni kaina bani da lambarsa, seta PA dinsa, se in abun me mahimmanci ne sannan ya hadaki dashi kuyi magana, inkuma bame mahimmanci bane ba yakamaki yace bakida gaskiya, indai baya gari tokomenene hakura nake”dafe kai saudat tayi takuma cewa” dan Allah kabani lambar P. A dinnasa mana” “waike wace irin mayyace ne, bar kofar gidan nan ko inyi waya azo a tafi dake wallahi” “No yi hakuri zan tafi, insun dawo senazo” daga nan ta juya ta taho gida, tareda tsinewa barawon dayasaci wayarta albarka, tasamo lamba a bagas an sace wayara haka ta dawo gida jiki a sanyaye, kallo daya khadija tamata tagane babu alamun nasara, nan Saudat tabawa khadija labarin abunda yafaru taita rarrashinta tareda bata karfin gwiwa kaman gaske. Khadija takoma daki ta tsarawa Habib text

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122 123 124 125 126 127 128 129Next page

Leave a Reply

Back to top button