ABDUL JALAL PART 2

ABDUL JALAL PART 2

Salma tana gabaan dressing mirror tana shafa mai, ta kalli envelope din invitations da Habib ya ajiye mata tsaki tayi ta ture envelope din invitations din suka zube kasa, a hankali ta kai hannu ta dakko na daurin Aure tana dubawa
Duf! Duf!! Duf!!! Taji kirjinta yana bugawa
Khadija Munir yakasai tunani take ina tasan wannan sunan, take sunan Saudat ya fado mata Saudat Munir Yakasai, taduba inda za’ayi daurin Aure unguwar su Saudat ne layinsa
Ji tayi kaman numfashinta ze dauke, wayarta ta laluba ta nemo lambar Saudat, jikinta na bari, Saudat ta daga sama2 Salma take jawo Numfashi tace
“Saudat waye ze Auri khadija?”
Cikin rashin fahimta Saudat tace “lafiya kuwa Salma?”
“ki gayamin wa khadija zata Aura?”
Takuma tambayar cikin karaji
Saudat tace “nima bansaniba amma naji tace sunanshi Habib”
“INNALILLAHI WA INNA ILAIHI RAJI UN!!!!!! “
Salma ta furta da karfi

A ko yaushe ina alfahari daku masoya wannan Novel ina godiya da addu ‘oinku
Sannaan masu rokon adinga posting a Facebook insha Allah za’ a fara posting din Littafin ABDUL JALAL Facebook tundaga farko
Insha Allah, za’afara posting a group din
AISHA HUMAIRA NOVEL FANS (Daddy’s girl) dakuma sauran groups nagode sosai ❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️

Share please
I want comments not stickers or just thanks
Daga alkalamin Aysher cool
????️????️????️????️????️????️????️????️????️????️
What’s app only 07063065680
????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????

          _ABDUL JALAL (2020)_

   _Story and written by_
  AISHA HUMAIRA (daddy's girl) 

PART 2
_PAGE 2️⃣0️⃣73

Bismillahirrahmanirrahim, da sunan Allah me rahama me jinkai, Allah yakara tsira da aminci ga shugabanmu Annabi muhammadu salallahu alaihi wassalam.
Bayan haka bazan gajiba da mika gaisuwata da godiya ga yan uwa da abokan arziki ba, bayan haka
Banyarda a juyamin littafi ba ko amfani da wani bangare ba tareda izinina ba.
Domin gyara, shawara ko sharhi, za a iya tuntubata akan what’s app number dina
07063065680
Or email address @ www.humaira17@gmail.com

          _MY FIRST NOVEL_

Da sauri Saudat tace “Salma lafiya kuwa? Wai meya faru ne?”
Cikin kuka tace “dole kicemin meyafaru Saudat, kuncuceni ina zaman lafiya da mijina, amma ku yaudareni keda yar uwakki wallahi bazan yafe muku ba Saudat, kije da Allah nabarku da Allah daga ke har khadija” cikin rashin fahimta Saudat tace “bangane me kike nufiba Salma, dan Allah kimin bayani”
“Au saboda baki da kunya har bayani kike nema inmiki, Azzalumai kawai, wallahi bazan yafe muku ba na yadda dake kun hada kai da yar uwakki kun cutar dani cuta mafi muni kuda Allah” ta kashe wayarta, ta dora hannu akai ta fashe da wani irin matsanancin kuka me tsuma zuciya
“Na shiga uku ni Salma, menamuku kuka kwacemin miji, mijina mafi soyuwa a gareni shi zaku auremun Habibin nawa, shi zaku auremun na shiga uku ni Salma, meyasa nasanki Saudat” haka tacigaba da kuka tana surutai.

A salube Saudat ta sauke wayar, takasa gane inda maganganun Salma suka dosa, meye alakarsu da Auren mijin Salma. Tana cikin wannan tunanine taji ana shelar ankai lefen khadija gidan kanin babansu, akwati ashirin da hudu, gida ya dau sowa da hayaniya
“Akwati ashirin da hudu”? , Saudat ta maimaita, “itakuwa khadija ina tasamo Attajirin mutum haka? Waye wannan ze Auri khadija haka, shiyasa take boye shi, to tabbas idan har bansamu Auren Habib ba, sena shiga na fita naraba khadija da Auren nan koda tayishi, dan bazeyuwu tayi Aure tasamu Attajiri haka, nikuma ina gararanba ba”
Tafito tsakar gida yan gida nata surutu, wasu na san barka wasu na kushewa, suna agarin kwashe2 kil dan yankan kaine, inbahakaba akwati ashirin da hudu sekace wata yar gwal, yayinda bakin mahaifiyar khadija yaki rufuwa dan murna.
Khadija bata gida dan sedare ta dawo, yauma Saudat gurin khadija ta tafi
“Khadija nikam dan Allah ki gayamin waye mijin nan ko a hoto ki nunamin shi, akwati ashirin da hudu dozen biyu fa, sana’ar meyake haka”
“mekike ci na baka na zuba, har gidan nan zezo ranar daurin Aure kijira zaki ganshi ai, koma sana’ar meyake ni ina ruwana”
“sewani Boyeshi kike kaman ciwo, zamu ganshi dai muga meye ake boye mana, nace wai yazakiyi da kabir ne”?
Tsaki khadija tayi “Kabir din banza, nabashi katin daurin Aurena, yagama zage zagensa da kumfar baki, uwassa ma tayi tagama, nace yaje yai duk abunda yaga ze iya”
“hmm khadija manya, amma Kabir be cancanci haka daga gareki ba, ya miki wahala be kamata ku rabu baran baran ba”
“to ko zaku daidaitane keda shi?”
“Allah ya kiyaye ke ki auri me kudi nikuma ki hadani da matsiyaci Allah ya kiyaye”
“yo kuma ni sekiga laifina”
“to abar wannan zancen dazu tela ya aiko miki da dinkinki”
“Aiko ya kyauta, dama nagama biyansa kudinsa”
“Khadija munyi waya fa da Salma dazu” wani mummunar faduwar gaba ta ziyarci khadija amma ta dake tace “Allah sarki”
“Amma wasu magamganu ta dingayi da bangane musu ba”
“kamar ya kenan”
“ni kaina ban gane me take nufiba, Amma zankuma kiranta, yadda take maganar tana cikin damuwa”
“Saudat duk wanda za’ayiwa kishiya ai dole yashiga damuwa, mussaman bw san da wacce kishiyar zata shigo ba, kibata shawara cewa ta mike tayi tsaye, dan duk wata mace a yanzu musamman wadda zata shiga gidan me mata toda shirinta take zuwa”
“bata tsaya ta saurareniba balle in bata wata shawara, bari dai ayi bikinki agama, nikuma zan mike inyi fafatuka nima inshiga a ta uku” dariya sosai khadija ta dingayi mata “lallai Saudat yakamata kema seki dage Allah yabawa me rabo sa’a”
Yau Habib yadawo daga tafiyar da yayi, dan satin biki yakama, dan gidansu khadija har sunfara wasu events din da mamakinsa koda yadawo Salma bata gida, yakira wayarta amma taki dagawa. Yasan bata da wasu kawaye ko gurin zuwa a kano dan haka a ranar ya shirya ya nufi maiduguri, aikuwa yanazuwa tana can gidansu gaba daya bata hayyacinta banda aikin kuka babu abunda takeyi, dayake shima gidansu ne be jira amma sa isoba ya shiga gidan ba kowa se ita kadai a palour a kwance akan doguwar kujera idonta duk ya kumbura saboda kuka
“Salma meyasa kika taho kekadai baki gayamin ba, inata kiran wayarki kinki ki dauka hankalina ya tashifa”
Banza tayi masa ta dauke kanta, “haba Salam meyake faruwa ne?”
“dan Allah ka rabu dani Habib karshen wulakanci kayimin shi, karasa wadda zaka Aura se yayar kawata duk matan dake garin nan, bakasan wacece khadija ba, amma ka rubuta ka ajiye sekayi danasanin wannan auren kuma bazan koma gidanka ba nagama Aurenka Habib, am really disappointed on you ” mikewa tayi zata bar palourn ya riko hannunta amma ta fizge ta wuce dakinta ta kulle kofa, jiki a sanyaye yanemi guri ya zauna ya dafe kansa a gurin, Salma tanada mahimmanci a rayuwarsa baze taba bari kishinta ya rufemata ido ta rabu dashi ba, amma me take nufi daze auri yayar kawatta dama tasan khadija ne? Mikewa yayi ya nufi part din mahaifin Salma.
Amma yana zuwa ya tarar yanada baki dan haka yajira ya gama sannan yashiga, mahaifin Salma na ganinshi yafara murmushi “Ango kasha kanshi, saukar yaushe haka ba Labari” dan sosa kai Habib yayi ya samu guri ya zauna yace “Abba dan Allah ka tayani bawa Salma hakuri, duk na rasa gane kanta, munyi sallama lafiya na tafi na dawo na tarar bata gida ta taho nan, nace tazo mukoma tace bazata koma gidana ba” Ajiyar zuciya mahaifin Salma yayi sannan yace “Mata se addu’a, ni na dauka kasani kai ka batta tazo ai, kuma mahaifiyarta batacemin yaji tayo ba, tashi muje yaudin nan zaku koma kano tare Insha Allah”
Suka mike suka tafi dakin Salma, Abba yace ta bude masa shine, haka ta taso ta bude,
Nan ya dirar mata da fada ta inda yashiga bata nan yake fita ba, yaimata kaca2
Cikin kuka tace “Abba kayi hakuri amma yayar kawatace fa, meyasa yaya Habib zemun haka”
“ko kawartaki ce aiba haramun bane ba, kuma daba’a Aure daba a Aureki ba” daga nan ya yakoma yimata nasiha da rarrashi, ya hadasu gaba daya yai musu nasiha yai musu Addu’a, Abba be bari maman Salma ta dawo ba yace ta shirya tabi Habib sukoma Kano.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122 123 124 125 126 127 128 129Next page

Leave a Reply

Back to top button