ABDUL JALAL PART 2

ABDUL JALAL PART 2

Jawwad suka isa airport yayiwa Jalal Sallama amma ya amsa masa a ciki, sam baya walwala, yasan halin Jalal baya son takura, tunda be niyyar gaya masa meke damunsa ba, ya ja Akwatinsa yayi gaba yabar Jawwad.
Haka Jawwad ya taho yanata tunanin me akayiwa Jalal yake wannan bacin ran haka?

Bayan Jalila ta gana yiwa Maama girki, ta koma daki, ta dauki Alqur’anin nan tana ta jujjuyawa, Kamshin turaren Jalal yakeyi, hakama dan teddyn ta, tasa hannu ta ta dinga duba Alqur’anin nan page by page, amma sam bata ga komai a ciki ba, kodai Jalal dama yana son raina mata hankali ne kawai?
Shiru tayi ta tuna yadda taga yana yinsa bayan ya gansu tareda Ahmad, Fuskar nan tasa a daure babu alamun sassauci, tayi shiru ta cigaba da zancen zuci, ;yanzu ze tafi lagos bashi da kowa a can, babu me kula dashi, Allah kadai yasan meze aikata,
“kinfi so in cigaba da shaye2 na ko? Ke Garkuwa ce a gareni” ire iren wannan maganganun nasa da Maganganun Antynsa da take gaya mata tabata amanar Jalal ne yasa take tunanin Anya hukuncin data yanke yayi dai2 kuwa?
To Amma nikuma mutuncina fa? ” gaba daya ta rasa me yakamata tayi? Yanzu tana gaya Hanan, tasan Hanan zata canza mata magana tafara kawo wani abu daban, dan haka tabar Abun a ranta ta cigaba da Yiwa Jalal Addu’a.

‘yan kwanakin nan sam Abba ya dena shiga harkar Maama, har gara Jawwad ma yana zuwa gaisheta, Nana kuwa seda Jalila tasata a gaba ta nuna mata be dace ba abunda take yiwa Maama, wannan abunda yafaru tsakanin ta da Abba ne da kuma’ yan uwan ta, sannan ta samu Nana ma take shiga sabgar Maaman, Abba ya gayawa Maama ranar Lahadi zasuyi baki, za’a kawo kudin Auren Nana, abakin su Nana taji batun haduwa da ‘yan uwan Abba a Bauchi, ba tayi mamaki sosai ba jin ance su Hanan’ yan uwansu Abba ne ba, sakamakon matukar kamannin dake tsakanin Jalila da Hanan, sedai taji haushin rashin sanar da ita da Abba beba.

Tun ranar Juma’a suke shirye2 domin bakin daza’ayi, Jalila ce jagorar girke2 da shirin yadda za’a karbi baki.
Gefe guda Jawwad yana ta shirye2 Ranar litinin shima ze tafi gurin nasa Aikin, ba karamin kulawa Hanan take bashi ba, da soyayya da kuma shagwabarta, yanayin yadda take nuna yarinta a wasu bangaren ba karamin birge shi yake ba.

Kamar yadda aka saka ranar lahadi daddyn Hanan yazo Kano aka karbi kudin Auren Nana, itama lokaci dayane dana Jawwad dakuma Abdallah Yayan Hanan, ranar har mutan bauchi seda sukazo garin kano karbar kudin, da kuma kara taya juna murnar haduwar su a matsayin ‘yan uwa. Jalila taji dadi da akazo hadda Hanan da Mummynta, Maama seda ta sha jinin jikinta ta raina kanta ganin manyan mutanen da sukazo gidan, Abun Arziki ya hadu dana Arziki, dangin Su Jawwad dana Su Jalal, Ranar anci ansha, kai ka dauka bikin Aure akeyi rana ce me matukar tarihi da wannan Ahali bazasu manta ba. Jalila sam bata samu kebewa da Hanan ba, saboda Hanan na manne da Jawwad, sam bata jin kunyar kowa take nuna masa soyayya.
Mummyn Hanan se mita take tace “Ni gaskiya naso a hada abun nan hada na Jalila, in aurar da ‘ya’ ya uku, amma in shirya da kyau, amma bakomai anata se nafi shiri ko Jalila?”
Ita dai Jalila sedai tayi murmushi ta sunkuyar da kai.
Duk yadda Maama take jin kanta take kuma jin haushin Auren Hanan da Jawwad boyewa tayi, Saboda sam bata da makusa, ‘yar dangi ce, kuma’ yar uwar dan tace, tana da kyau dai2 gwargwado kuma tana da Ilimi, yanayin kyau da gayun mahaifiyar Hanan ya isa ya nuna maka ‘yar ta ma hakan take. Koda ta hasko Naja seta ga abun se A hankali, kuma tun abun nan da sukayi mata ta tabattar da Ko Auren akayi Naja zata iya wulakanta ta.
Da ire iren wannan tunanin yasa ta ajiye duk wani bacin rai aka shiga hada2. Tareda tsara yadda suke ganin bikin ze kasance, Ba laifi Mummyn Hanan ta saki jiki Maama, Sunyi hira sosai kaman sun saba, sannan suka tattauna akan yadda harkar bikin yaran nasu ze kasance. Se la’asar Suka tafi, mutanen Bauchi suka tafi, Su Hanan ma a ranar suka juya kaduna saboda Su Hanan suna jarrabawa, su kuwa danginsu Mahmud, suna kawowa Mahmud kudin Aure sukaci Abinci suka juya Borno.

Wasa2 sosai tunanin Jalila ya hana Jalal sukuni, da yafara aiki in ya tuna da ita gaba daya se yaji duniyar tayi masa zafi, yarasa inda zesa kansa, meyasa Mummy tayi masa haka? Idan yaji abun ya dameshi se ya tafi club yaje ya cika cikinsabda giya, dukda wasu lokutan yana bawa aikin da yaje yi mahimmanci, Sam Jalal bashi da sakewa da mutane, dan haka be saba da kowa ba, sedai yana girmama shugabanninsa na gurin aiki, girmamasun da yake besa sunga alamar ze bari su taka shi ba, inda yake burgesu yana maida hankali akan aikinsa sosai.
Duk lokacin da yaje Club mata da suke damun sa ne ga kuma shigar tsirara da suke yasa shi dakatar da kansa ga zuwa Club, idan yaji ba yadda zeyi se yayi shaye2 se yayi abunsa a dakinsa na hotel da yake ciki.
Amma duk da haka yarasa dalilin da yasa mata ke binsa, sedai in baze fito ba.

Hannah ce zaune akan kujera tana kwalliya, Sa’ada na kwance akan gado tana danna waya, dan dakatawa da kwalliyar Hannah tayi ta dan kurawa madubi ido, sekuma can ta daki kan mirror tace “Impossible baze yuwu ba wallahi”
Sa’adah ta waigo ta Kalle ta tace “lafiya kuwa?”
“Akwai matsala Sa’ada” Hannah ta bata amsa
“matsalar me fa?”
“Sa’ada ki kalleni ki kara, kimin kallon tsaf tun daga sama har kasa, ki kalli yadda nake gara kan maza, in taka wanda naso in wanke wanda naso, amma a hakan har rububina wasu suke, in sauke Ajina in cewa Jalal idan ya Aureni zan dena bariki, Amma ya watsa min kasa a ido”
Wani dogon tsaki Sa’ada tayi tareda fadin “Nina dauka ma wani mutumin kirkin ne, A she akan wannan mashayin ne, ni ba wannaan ya dameni ba a yanzu”
Hannah tace “Mutumin kirki ne mana, ki kalleshi kallon tsaf Sa’ada Namiji ne irin wanda duk wata mace zatayi burin Aure, shaye2 ne kawai matsalar sa, da farko da nakewa su Jeje aiki, nna zata zan samo kansa ta sauki ya yadda dani, Amma duk wata dabara da kisisina ta matan bariki nayi amma yaki amincewa dani”
“to kibi wani mana, ko shine kawai namiji?”
“bazaki gane ba Sa’ada, bakiga irin kirar da Allah yayi masa bane, kuma da kike ganinsa a haka, dukiya ce dashi kaman abun banza”
“Ya akayi kika sani, nasan dai babansa yana da kudi, amma shikam ko aikinyi ba shida shi” Sa’ada tayi maganar tana yatsina fuska
“Hmm to wallahi har ki mutu in ba wani ikon Allah ba, kaf danginku daku da abunda kuka mallaka, bazaku kaishi dukiya ba, yana da kudi da mahaifinsa yasa ake juya masa, Jeje yaso ganin bayan dukiyar nan shida mai gidansa amma abun be yuwu ba suka kare a prison”
Sa’ada ta tashi zaune tace “to ke yanzu meye abunyi, ni ban taba sani ba, kin san ya taba kusa tonamin Asiri ina zuwa club agaban babarmu”
Dariya Hannah tayi tace “Abune mawuyaci ya tona miki Asiri, bar ganinsa a haka, yasan abunda yakeyi, naje har gidansu na dana masa tarko, amma ga dukkan alamu ya tsallake shi, wannan karon zan masa tarkon da zan rike shi a wuya, be isa ya kuma subuce min ba”
“Yakamata kam, Amma ni nan tunanin yadda zan huce abunda abokinsa Jawwad yayiwa Naja nake, kiri2 yafasa Auren ta, yarinyar nan duk ta shiga damuwa”
“Allah sarki, to wai ya’akayi aka fasa Auren? Waye yaje yai mata gulma a gurin baban nasa?”
“ya za’ayi in sani, Amma da nafi kyautata zaton wannan munafukar kanwar tasa ce”
“Wace kanwar tasa ya’akayi tasan abunda Naja take? Ko dai itama tana ta bawa?”
“Ke bari, wata yarinyace yadda kika san boka haka take, ni dai ban san tana wani biye biye ba, Amma kina zaune in taso seta nemo waye ubanki koda ke baki sani ba, wai ita Jalila makirace ta bala’i, idan tace bata san abu seta ga bayansa, tasa Jawwad ya fasa auren Naja se kawarta”
Jin an ambaci Jalila yasa Hannah zare ido tace
“Kan bala’i ai nasan wannan yarinyar, tabdijan ni zan gaya miki makira ce, ke wallahi keda kike bariki tafi ki iya rashin mutunci, ke zata iya yuwu wa ita tasa aka hana, bari in gayamiki yarinyar nan tafiki bala’i, dan koni tasa min ido akan Jalal, ita take rusa min komai “
Cikin mamaki Sa’ada ta kalli Hannah tace” wai kin santa ne? “
” Nikuwa na santa, kuma nasan illar ta, munyi Arranging da Jeje mun gama komai, zamu sace Jalal ranar birthday din sa, idonta na kanmu, muka bugar da shi da giya ta shammace mu tasa aka dauke shi daga gurin, ke ina jin kishin cewa ita tasa aka kama Oga KB”
Zaro ido Sa’ada tayi cike da mamaki tace “Ke haba dai? Shikuwa oga KB yana me,duk iya kuri da gadarar rashin mutuncin nasa, yarinya ce fa karama”
Hannah tace “hmm ke dai bari, mace kenan, kaidin wata yafi wata, irinsu kuma sa’a ce dasu a rayuwa, kibi a sannu kawai”
“Tabdijan amma babu kama, dan bakiga cin mutuncin da muke mata ba mu da babarmu, kin san uwarta tsohuwar arniya ce, bakiga cin mutuncin da muke mata ba”
Hannah tace “Yawwa kuma ga cin mutuncin da tayi muku nan, kuma ta gama daku ba”
“Sosai makuwa ta gama damu”
“shiyasa wannan karon shirina ita da Jalal ne, dan bana ta wannan Ilham din dan wannan ba mace bace, wannan tafi hatsari, baze tsallake wannan tarkon ba a yanzu, na duba mashayar da yake zuwa ba adadi amma ance ya dena zuwa, duk da haka zan nemoshi”

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122 123 124 125 126 127 128 129Next page

Leave a Reply

Back to top button