ABDUL JALAL PART 2

ABDUL JALAL PART 2

Daddy yakasa samun sukunibda abunda ya faru, gaba daya hankalin sa yaki daidaituwa, yarasa maganar wa zebi, ta Jalila kokuma ta Wannan yarinyar, Amma yakasa bawa kansa amsar wani tabacci Jalila take da shi akan Jalal, Mummy ta lura da yadda daddy ya dami kansa dan haka tace

“Ni dai a ganina wannan yarinyar da gaske take, ba’a shedar mutum, shiyasa nake son mu aurar da Jalal, shekarunsa ya kai ya ajiye iyali, ita kuma wannan yarinyar da tazo da wannan maganar, indai da gaske take, a lallabata abata kudi tayi hakuri”

“bana tunanin Jalal ze aikata haka, kuma tunda Jalila ta bada sheda akan Jalal, abun dubawa ne, amma yazama dole in bincika, lamarin yaron nan na ma rasa yazanyi, Allah ya shiryamana zuri’a”
Dadd yasa hannu ya dau wayarsa ya kira Jalal a waya, seda ta kusa katsewa sannan Jalal ya daga, koda ya daga ma beyi magana ba, shiru ya gudana na wani dan lokaci sannan daddy yace “Jalal kana jina?”
“Ina jinka daddy”
“ya kake ya aikin kuma?”
“lafiya kalau Alhamdilillah daddy, kana Nigeria kenan?”
“Eh ina nan, nakira ka ne, ina so muyi magana”
“ina jinka”
“Wace ce Hannah?”
Gaba daya Jalal ya manta da wata Hannah a rayuwarsa, Amma ya maze yace “Ban Santa ba”
“Jalal ban sanka da karya ba, wannan yarinyar itace kwanaki tazo min da waccan maganar, wannan karon tazo min da maganar wai tana dauke da ciki kuma nakane, Amma Jalila ta karyata ta, sannan tacemin Yarinyar tana da matukar hatsari ga rayuwarka, kamin bayani “
Ba abunda ya farantawa Jalal rai sama da jin batun Jalila ta kare shi, duk da furucin da tayi na bashi ba ita, daddy yace” Jalal ya naji kayi shiru? “
“to me zance maka daddy? Duk hukuncin daka ga dauka akaina dai2 ne, inma ka yadda gaske ne ko karya, dan Allah ni ku kyaleni hankali na ya kwanta, ina jin dadin zamana a inda nake karku daga min hankali”
“Amma Jalal meye hadinka da yarinyar nan har take bibiyar ka? Tana ikrarin zata kai kararka”
“Daddy in dai har bana nan, a bayan idona yarinyar data tsaneni zata bada shedar kirki akaina me kake so ince maka, kana so inta rantsuwa ne seka yadda dani? Kasan ba haka nake ba, Idan bata kai karata ba ni zan dau mataki akanta”

“Amma meye hatsarin yarinyar ga Rayuwar ka? Kamar yadda Jalila ta fada?”
“ka tambaye ta mana, tunda a bakinta kaji”
“Jalal yaushe zaka dawo?”
“ba yanzu ba, se nan gaba, nifa zamana anan yafi min zaman gidan nan, da za’adinga takura min”
“to shikenan tunda haka kace”
Haka sukayi sallama ya kashe wayar.

Mummy tace “wai nifa nakasa gane wannan maganar, ita Jalila wacece dinsa da za ta fadi abu ka yadda, ya akayi tasan abunda mu bamu sani ba akan danmu, haka akeyi?”
Murmushi daddy yayi ya dan kashe mata ido yace “haba deejat to meye a ciki? Kin samu me kulamiki da son, you have to thank her, har gida tazo dan kare shi”
Kara kunna Mummy yayi, dan haka ta tashi fuuu ta bar masa dakin.

Ilham tayi safa da marwa yafi sau Ashirin a dakinta, tana son ta tabbatar da Hannah dagaske take koda wasa, yanzu abun ya kuma kwabe mata, da ta manta da batun Hannah, amma yanzu yakin ya kuma zame mata biyu, ga Jalila ga Hannah, da tana tunanin tayi maganin Jalila, tunda tayi mata makirci a gurin Mummy, “Amma Jalila nan naci ne da ita bata da zuciya, shegiya se nayi maganin ta, sena kuma kunna mata wata wutar, to amma in dagaske Jalal yayiwa Hannah ciki fa? Da sauri tace” kai karyane, da Jalila yayiwa Hannah ciki da yanzu wani zancen ake ba wannan ba, karya takeyi”
Ilham ta fito daga dakinta har tana tuntube ta tafi daki Mummy, tana zuwa ta tarar Mummy ta cika tayi fam, fuskarta sam babu walwala, Ilham taje ta zauna a kusa da Mummy tace
“Mummy lafiya kuwa?”
“ke rabu dani, ni zancen wannan yarinyar mana, gaba daya daga Jalal din har ubansa naga hankalin su ya karkata kan wannan yarinyar Jalila, ga itama wannan wadda tazo din da wannan maganar cikin”
“mhmm wallahi Mummy in bakiyi wasa ba yarinyar nan se ta hana Jalal din ma shigowa gurinki, ta ne Santa shi dake, meye nata na sawa anema masa aiki a nesa? Kuma ga daddy yafara biyewa maganganun ta, wallahi Mummy da sannu zata janye miki shi gaba daya”
Mummy ta numfasa tace “ni Ilham gaba daya kaina ya kwance akan lamarin Yaron nan, narasa yadda zanyi”
“to Mummy kiyiwa daddy maganar, ayi mana Auren mana, saboda ayi maganin abun, tunda har ya fara bin mata”

A fusace Mummy tace” Ke dan Allah ki rabu dani, kina gani ba irin kokarin da banyi ba, Amma abu ya ga gara, ni ki kyaleni nace ki bani lokaci, sena fara shawo kan matsalar, ni na miki alkawarin Auren nan, ki karamin lokaci in gama da wannan matsalar mana”
Ilham ba tace komai ba ta mike ta bar dakin, tana fita tayi kwafa tace “Wallahi zaki gane kuskuren ki Mummy, zanyi maganinki, sena Auri Jalal din na mallake shi, ke da shi sedai kallo”

Amin Afuwa nayi busy sosai,
Gashi nan ba editing

????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????

              *ABDUL JALAL*

         _Story, writing and edited _

                        By
              AISHA HUMAIRA
              ( _Daddy's girl_) 

PERFECT WRITER’S
ASSOCIATION????

(???????? ????????ℕ’???? ℙ????ℝ????????ℂ???? ???????????? ????????’ℝ???? ????????????????????????, ????ℝ????????ℕ???? ????????ℝ ???????????????? ???????? ???????????????????????????????? ????ℕ???? ????ℕ????????ℝ????????????ℕ ????????ℝ ℝ????????????????ℝ????????)

/https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/

P.W.A✍️

        PART 2         
                      _PAGE  4️⃣4️⃣97

Bismillahirrahmanirrahim, da sunan Allah me rahama me jinkai, Allah yakara tsira da aminci ga shugabanmu Annabi muhammadu salallahu alaihi wassalam.
Bayan haka bazan gajiba da mika gaisuwata da godiya ga yan uwa da abokan arziki ba, bayan haka
Banyarda a juyamin littafi ba ko amfani da wani bangare ba tareda izinina ba.
Domin gyara, shawara ko sharhi, za a iya tuntubata akan what’s app number dina
07063065680
Or email address @ www.humaira17@gmail.com
Watpad @Ayshercool7724

         _MY FIRST NOVEL _

Shiru Jalila tayi ta kalli kayan daya ajiye mata sannan tabi bayansa da kallo har ya fice daga gate, din shiru tayi ta tafi tunani, Ahmad yace
“my queen, meya farune?”
Da sauri ta dawo hayyacinta tace “bakomai fa”
“Amma waye wanan?” ya tambayeta yana me kureta da ido, ta dan sauke numfashi tace “Yaya na ne”
“Yayanki queen, ba Jawwad ne kawai Yayanki ba?”
“Abokin Yaya Jawwad ne, dan haka Yayana ne kawai”
“Amma babu wani abu a tsakanin ku kuwa?”
“Meyasa kake min wannan tambayar? Ko baka yadda dani bane?”
“Ahh haba waneni ince ban yadda da gimbiyata ba, ina so ne in tabattar da abunda ke tsakaninku, dan da idonsa yana shaye2”
Ba karamin haushi maganar Ahmad ta bata ba, kenan shima yanayi, in ba yanayi ba, ba abunda idon Jalal yayi dayake nuna yana shaye2, dan haka tace
“baya shan komai, kawai bashi da son magana ne, baya kula mutane”
Kyaleta Ahmad yayi yaga alamar bata son zancen suka cigaba da hira, Jawwad ne ya fito ze wuce su Jalila ya tsaya suka kuma gaisawa da Ahmad dayake dazu sun gaisa, Jawwad yace “to sirikina zan iya ce maka se anjima, ni zan tafi kai Jalal airport ne”
Da sauri Jalila tace “Ina zashi?”
Jawwad yayi murmushi yace “Aiki mana, an tura shi Lagos, se lokacin biki inaga ze dawo, bari inje karyai ta jirana, kin san baya son jira, se anjimanku” Sukayi sallama da Ahmad ya fita.
Ahmad ya maida idonsa kan Jalila yace “Gimbiya naso a haďa bikin nan hada namu, na kagu in mallakeki”
Murmushi kawai tayi amma hankalinta baya kansa, tanata zancen zuci ne, dayaga haka yace “queen naga kaman Akwai abunda yake damunki, bari in tafi semunyi waya”
Ta mike ta rakashi har bakin gate sannan ta dawo ta zauna akan kujerun tana nazari
“At least yakamata ace sunyi sallama da Jalal, tayi masa nasiha, Amma bata tunanin zata iya kuma rabarsa ba saboda mahaifiyarsa.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122 123 124 125 126 127 128 129Next page

Leave a Reply

Back to top button