ABDUL JALAL PART 2

ABDUL JALAL PART 2

Hajiya Salma tace “nima dai haka nagani, tunda muka taho bata da lafiya, Amma yaron na ko ta kanta bebi ba, balle in sa ran ya duba ta, ya mata sannu” da sauri yace “bata da lafiya kuma? Me yasa me ta?”
Hajiya Salma tace “ban sani ba” mikewa yayi ya kalli Husna yace
“ina ne dakinta”?
“tana upstairs kusa da ďakina” ta bashi amsa, be kuma bi takansu Anty ba ya haura saman.
Kai tsaye ya bude dakin ya shiga, ya sameta ta dukunkune a cikin bargo, a hankali ya karasa gaban gadon nata ya kai hannu ya janye bargon.

Wata sleeping dress a jikinta blue me matukar kyau, kanta babu dan kwali, dukda tayi parking din gashin nata amma gashin ya hargitse, bacci takeyi sosai, Amma tayi rama a baccin ma se ajiyar zuciya take.

Ya kura mata ido fatarta se sheki take, a hankali ta motsa ta mike hannyen ta wajen kirjinsa, hannayenta sun sha ado da jan lalle, hannunsa yasa a nataa ya rike yana kuma kallon fuskarta, bacci take amma tayi kyau sosai. Ya bata lokaci sosai yana kallon ta. A hankali ya saki hannunta
Ya dakko wata ‘yar takarda a Aljihinsa da biro yayi rubutu ya ajiye mata akar kashin pillow dinta, ya mayar mata da hannun ta kan gado ya lullube ta ya fice.
Koda ya sakko bekuma ce musu uffan ba yayi waje abunsa.

Anty tace “kinga danki ko?”
Hajiya Salma tace “ai bari kawai, Jalal Akwai taurin kai, suna son juna amma taurin kai neke damun su, se nunawa suke kaman basu damu da juna ba, Allah shi yabarwa kansa sanin dalilin dayasa ya hadasu, Amma wannan zaman Auren nasu da kallo”

“hakane amma zamu cigaba da yi musu Addu’a, zasu dai daita, bari kiga sukoma gidansu da zama, bazaki sake jin kansu ba”

“hakane Allah ya tabattar da alkhairi, Amma bazata koma kano yanzu ba, sonake hankalin ta ya kwanta ta sake nustuwa, daga nan ma waccan jarababbiyar watakila ta sakko”

Anty tace “tab haba sister Salma, kin manta wacece khadija kenan, ai babu batun ta sakko yanzu, kawai dai mu tayasu da Addu’a” haka suka cigaba da hirarakin su.

Koda Jalila ta tashi ji tayi gaba daya dakin ya gauraye da kamshin Jalal, dan tabe baki tayi ta shiga toilet tayi wanka ta sa kaya, tazo tana kokarin gyara gadon tana cire bedsheet din taga takadda ta fado, ta dauka ta bude, wani tsararren handwriting tagani a jiki.

Am going back to lagos, get well soon
ABDUL JALAL se signing dinsa da date

Juya takaddar tayi ta jefar da ita a gurin tayi tsaki, “kwana nawa bani da lafiya, tunda aka daura auren ko ta kaina bebi ba, se yanzu ze wani rubuta min wata banzar takadda, ya tafi abunda yafi lagos ma ni be shafe ni ba, kuma maimakon ya ajiyemin wayata amma yakuma tafiya da ita sekace tasa.
Haka Jalila ta cigaba da mita, har ta gama gyaran gadon.

Parlour ta fito dan ta gaji da zaman dakin ga shi ba waya a hannunta balle ta debe mata kewa.
Anty na ganin Jalila tayi murmushi tace “Jalila kin fito? Ya jikin naki kuwa?”
“naji sauki Anty”
“to Allah yakara sauki, dazu Mijinki ya shiga dubaki ai”
Dan tabe baki Jalila tayi tai shiru.
Tundaga Ranar kullum cikin turara Jalila suke da samfurin turaruka daban2, a rana se ayiwa kayan sawa turare kusan sau hudu, banda wanda ake tuarar mata jikinta, hatta ruwan wankan Jalila akwai turaren da’ake zubawa, sabulun wankan ta ma na musamman ne aka hada mata, ga mayukan shafawa dana kai, nan da nan Jalila jikin Jalila yara canzawa, duk inda ta gifta kamshi take, duk rashin son kitson Jalila wani na tsufa me kitso take zuwa tayi mata wani, hakama lalle, gaba ďaya wannan gidan sun maida Amfani da turaruka kamar ibada, babu wani aiki da takeyi sedai taci ta kwanta, ko ta yunkura zatayi aiki se a hanata, ga kyan gyra da’ake bata dan haka har wani kiba tayi abunta tai kalau da ita. Jalila idan tana son yin waya sedai ta ari ta Anty tayi, ta mata magana akan wayarta tace tabari Jalal yazo.
Tunda Jalal yazo ko a waya be kuma neman inda Jalila take ba itama ba ta nemi jin inda yake ba.

Mummy ta cigaba da tayarwa da Daddy hankali akan maganar Auren Jalal, amma sam yaki saurararta, ya tattara ya koma Dubai, duk abun nan da ake Ilham bata sani ba.

Daddare Ilham na kwance tana chatting, ta shiga Twitter kamar wadda aka saka ta shiga profile din Jalal Alhamdilillah got married to Jalila Aliyu Imam shine abunda Ilham ta gani zumbur ta tashi Zaune tana kuma mutsukke ido, Amma still taga ba mafarki take ba.
Da sauri ta kira layin Nana, Amma bata shiga, se lokacin ta tuna ai Nana Mahmud ta aura, a England zasu zauna.
Fitowa tayi da sauri ta tafi ďakin Mummy tana kwala mata kira
“ke lafiya kuwa kike min wannan kiram, meya faru ne?”
Nunawa Mummy wayar tayi, mummy tace “me zan gani?”
“Mummy wai dagaske ne Jalal yayi Aure”
Ajiyar zuciya Mummy tayi tace “tun satin da Daddy yaje daurin auren Jawwad, ya hada baki da ‘yan uwansa suka masa Aure, nayi2 ya gayamin wacece yaki”
Innalillahi wa inna ilaihi raji un, Mummy kin san wacece kuwa? Jalila ce fa, kalli Abunda ya rubuta ita ya aura Mummy, na shiga uku, Mummy ki kashe Auren nan kafin sun tare, Wallahi idan suka tare na kade, zan rasa komai, komai nawa ya rushe”
Gaba ďaya Mummy tsayawa tayi tana kallon Ilham
“dolene in kashe Auren nan, baze yuwu ba, wallahi ko yana so koba ya so sena kashe auren nan, ni Hajiya zainab zata munafunta, a hada kai da ita a Aurawa ďana wannan makirar yarinyar, in abun gaskiyane ta aurawa nata ďan mana, indai nina haifi Jalal seya saketa, a ďaura masa Aure ko ya nemi inda nake, rabona da shi wata biyar kenan, baze yuwu ba wallahi”

Share please
I want comments not stickers or just thanks
Daga alkalamin Aysher cool
????️????️????️????️????️????️????️????️????️????️

What’s app only 07063065680.
Follow me onWatpad @Ayshercool7724
???????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????? ????

              *ABDUL JALAL*

         _Story, writing and edited _

                        By
              AISHA HUMAIRA
              ( _Daddy's girl_) 

PERFECT WRITER’S
ASSOCIATION????

(???????? ????????ℕ’???? ℙ????ℝ????????ℂ???? ???????????? ????????’ℝ???? ????????????????????????, ????ℝ????????ℕ???? ????????ℝ ???????????????? ???????? ???????????????????????????????? ????ℕ???? ????ℕ????????ℝ????????????ℕ ????????ℝ ℝ????????????????ℝ????????)

/https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/

P.W.A✍️

        PART 2         
                      _PAGE 5️⃣1️⃣ 104

Bismillahirrahmanirrahim, da sunan Allah me rahama me jinkai, Allah yakara tsira da aminci ga shugabanmu Annabi muhammadu salallahu alaihi wassalam.
Bayan haka bazan gajiba da mika gaisuwata da godiya ga yan uwa da abokan arziki ba, bayan haka
Banyarda a juyamin littafi ba ko amfani da wani bangare ba tareda izinina ba.
Domin gyara, shawara ko sharhi, za a iya tuntubata akan what’s app number dina
07063065680
Or email address @ www.humaira17@gmail.com
Watpad @Ayshercool7724

         _MY FIRST NOVEL _

Tunda aka gama biki Maama bata dawo ba, seda takuma kwana goma a Bauchi, taji dadin zaman garin sosai, gashi mutane ne masu karamci da son ‘yan uwa, Abba ne yazo ya dauketa suka koma gida kanon dabo.

Bangaren Angwaye da Amare da sukayi Auren soyayya Se shan soyayya da kauna suke, tsakanin su banda Jalila da Jalal da babu wanda yake neman wani a tsakanin su,
Jalila ita wannan zaman hutun ya isheta, ita dama kano suka batta tayi zamanta a gurin Maama ya fiye mata wanna zaman.
Tana ta zancen zuci ne Husna ‘yar gidan Anty ta shigo da waya ta mikowa Jalila, Jalila tasa hannu ta karba, video Call ne ta ďaga wayar tana ďagawa taga fuskar Jawwad cikin sauri ta mike zaune

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122 123 124 125 126 127 128 129Next page

Leave a Reply

Back to top button