FAMILY DOCTORS HAUSA NOVEL

FAMILY DOCTORS HAUSA NOVEL 1

“Eh Abbu, nazo ganin ka ne sai mu wuce tare”.

Murmushi yayi yace, “Mamana kenan ai ban tashi ba, ina ga yanzu sai zuwa 04:00pm.”.

Gyara zaman ta tayi tace, “to Abbu bari in jira ka sai mu tafi tare”.

“A’a tashi kije gida ki huta Mamana ba na son ki zauna nan, kin ma ci abinci?”

“A’a Abbu”.

Coolarn dake kan desk ɗinsa ya turo mata yace, “ɗauka ki ci”.

Duk da ba ta jin yunwa bata yi masa musu ba ta ɗauka ta soma ci, kaɗan taci ta tsame hannun ta ta shiga Toilet ɗinsa ta wanko hannu ta dawo

Lokacin ne Abbu ya ɗago kai daga rubutun da yake yi yace, “Kin ƙoshi kenan?”.

Gyaɗa masa kai tayi sai kuma tace, “Abbu ko ma ban ƙoshi ba idan na koma gidan zan sake ci ai”.

“To shikenan Allah ya miki albarka ki kula kinji”.

“To Abbu byee”.

Ta ɗaga masa hannu sannan ta fice tana murmusa wa, tana fita haraban asibitin ta shige motan ta taja tayi gida, bayan tayi parcking ta fito ta nufi Part ɗin su, sai da ta soma shiga ɗakin Mamanta ta sanar mata dawowar ta sannan ta nufi ɗakin su, wanka ta soma yi ta shirya cikin wata koriyar atamfa ɗinkin Buba ta ɗaura ɗankwalin shi, eyeglasses ɗin ta tasanya ta fito ta nufi kichen, abinci ta ɗiba ɗan kaɗan ta fito parlour ta zauna tana ci, lokacin ne itama Fadila ta dawo

Ɗahira amsa mata sallaman ta kawai tayi taci gaba da cin abincin ta idanuwan ta na kan t.v, bayan ta gama ta tashi tamayar da plate ɗin kana ta wuce ɗakin Mamanta, tana tura ƙofan da sallama Aunty Amarya ta ɗago kanta daga karatun Hisnul Muslim da take yi, ta kalle ta tana amsa mata sallaman

“Mama bari inje wajen Kaka”.

Gyaɗa mata kai kawai Maman tayi ta maida hankalin ta kan littafin ta, ita kuma Ɗahira ta fice.
[5/23, 3:55 PM] Oummu Ɗahirah: ????????????????????????????????????????
FAMILY DOCTORS
????
????????????????????????????????????????

????????????????????????????
NAFEESAT RETURN
????????????????????????????

MALLAKAR:
NAFISAT ISMA’IL LAWAL

بسم الله الرحمن الرحيم


FEENAH WRITER’S ASSO????
”’®Ɗaya tamkar da Dubu????✓”’

JIKAR LAWALI CE✍️

Wattpad: UmmuDahirah????

     *\F.W.A????/*

SADAUKARWA
Na sadaukar ga Family na gaba ɗaya. GOMA’S FAMILY

      *NASIHA*

Sallar natsatstsu ba ta samuwa sai an kare sallar daga duk wani abu mai shagaltar wa, a kuma yi ta cikin lokatai waɗanda ba su hana yin Sallah da zuciya ɗaya kuma ba su zama shamaki tsakanin zuciyar sa daga kome ban da tunanin Allah, sai Allah ya haskaka masa zuciyar sa, ya sami basira ya ji daɗin saduwa da Ubangiji. Daga nan sai ka ga Bawa kullum yana mayar da hankali sosai ga wanda yake ganawa da shi. Wannan ma ya fi ƙarfi cikin sujada domin kuwa Bawa ya fi kusa da mahaliccin sa lokacin da yake cikin wannan hali. Don more wa shi wannan muƙami an ji Manzon Allah yana cewa, “Bawa ya fi kusanta ga Ubangiji. Saboda haka ya yawaita addu’a.”

.

    *EPISODE Nine*

. Cikin siririyan muryan ta tayi sallama tana shiga ciki

Kaka dake zaune saman Wheel chair ɗin sa yana karatun jarida ya ɗago yana kallon ta, sannan ya’amsa mata sallaman yana cewa, “Maraba lale da matata abar ƙaunata, yau ga matata ta zo gare Ni”.

Murmushi me burgewa Ɗahira ta saki tana takowa wajen sa ta zauna a gefen gadon sa tana cewa, “Kakus kenan baka rabo da tsokana ta, sai kace ka daɗe rabon da ka ganni”.

Smile yayi yace, “Matata kenan ke baki san yanda nake ji dake bane, yau gaba ɗaya ba na jin daɗin rasa ki kusa dani, Allah da ba don kar in so kaina da yawa ba, da sai ince ki zauna a gida abinki ba sai kinyi aiki ba, tunda gani Mijin ki Ina son ki kusa dani”.

Dariya sosai Ɗahira tayi kana tace, “Kaka kenan hmm Mijin kwali ko, don dai a kan ka dai bazan iya ajiye aiki na inzo in tare a wajen ka ba”.

Zaro idanu yayi yace, “au kina nufin ban kai matsayin da zan iya auren ki bane na zama na ƙarfen?”.

Sai kuma ya girgiza kansa yana dariya yace, “to bari kiji Ni ɗin Ni ne dai Mijin ki da zaki yi alfahari dashi nan gaba don babu wanda zai so ki fiye da yanda nake ƙaunar ki, har da wanda kike son min gori akan sa”.

In ban da dariya babu abinda Ɗahira take tiƙawa, sosai Kaka yake ba ta dariya idan suna zancen nan, kuma sai ya fuske tamkar da gaske ne maganar tasa

“Hmm ci gaba da min dariya, ban da abinki ma ni fa taimakon ki zan yi, kin san Real Matata tafi ki komi baza ki haɗa kanki da ita ba”.

Wannan karon murmushi tayi tace, “Kakus nawa Ni kaɗai, kaima ban da abun ka me zan yi da tsoho irin ka, idan har matarka ta fi ni komi ai nima Mijina ya fi ka komi, kuma idan kace ƙarya zan kawo maka shi ka ganshi”.

Cike da jin daɗi Kakan yace, “yauwa Jabun Matata ki kawo min shi dama na daɗe ina burin ganin sa, kin ga sai a gwada aga wanda yafi kyau cikin mu, ke kaɗai ce dama ban san saurayin ki ba, amma kin ga su rasa kunya ɓeran tanka duk sun kawo min su na gani”.

Numfashi Ɗahira taja tana kallon sa don ita bata san ma me zata ce mishi ba, ita da bata taɓa yin saurayi ba taya zata kawo masa wanda zata aura?

“You are silent my wife? I love to see who you will marry more than the other children. Burina kenan inga Mijin ki inga wanda zai iya riƙe min ƴar ƙwai na da amana”. Kaka ya ƙarike maganar tasa yana kallon ta da alamun dagaske yake yi

Hannu ta saka ta dafa Wheel chair ɗin sa tana kallon sa, cikin murmushi tace, “to karka damu Kaka, idan ma tsoro kake ji karka mutu baka ga aure na ba ka kwantar da hankalin ka, zan roƙa maka Allah ya barka da ranka har zuwa ranan da zaka ga aure na, me kake ci na baka na zuba Tsoho na?”

Kaka dariya yayi yana jan hancin ta yace, “ja’ira kin ganki”.

dariya tayi itama tana kai hannun ta kan hancin nata

“To ki nuna min shi ko a hoto ne mana”.

Zaro idanu tayi tace, “kaiii Kaka is so expensive, wannan dalilin ya saka na hana sa yin hoto kar ma wata ta mallaki hoton a rashin sani, don shi ɗin yafi ƙarfin ko wace mace idan ba Ni ba, but idan kana son in ɓurɓusa maka wani abu daga cikin labarin sa nima sai ka bani labari me daɗi ta yanda zanji daɗin baka labarin shi”.

“To shikenan yanzu bari in Baki labarin Matata abar alfahari na”.

Murmusawa Ɗahira tayi ta gyara zaman ta da kyau har da buga tagumi tace, “to ina ji bani nasha”.

Sai da yayi dariya kafin yace, “to tashi ki buɗe drowern can ki ɗauko min jakan ciki, ga ɗan mukullin acikin locker”.

Yayi mata nuni da Lockern dressing mirror

Ɗahira da har ta tashi tsaye tanufi wajen ta buɗe ta ɗauko keeys ta kawo masa, shi ya cire mata na drowern ta’amsa taje ta buɗe ta ɗauko masa jakan ta dawo

Zuge jakan yayi hotuna ne da yawa aciki, ya zaro ɗaya daga ciki ya nuna mata

“You see this”.

Amsa tayi tana kallo, shi ne tare da Baby a manne da juna, ga duk kan alamu anyi hoton ne lokacin da ake party, murmusawa tayi tana shafa hoton ta ɗago kai tana kallon sa tace, “Wow Kaka gaskiya kun yi kyau sanda kuke Matasa”.

Murmushi yayi yace, “ke ma kin faɗa ai, mun yi hoton nan ne lokacin da ake Dinnern bikin mu, hmm bazan taɓa manta wannan lokacin ba, Matata har yanzu na kasa manta ta har yanzu kuma ƙaunar ta na nan daram cikin raina batare da ko ɗigo ya fita ba duk da kuwa ba ta a raye, kin san kowa da irin ƙaddaran da Allah yake jarabtan bawan sa dashi, to Ni soyayyarta shine ƙaddara ta, na so ta matuƙa fiye da tunanin mutum, haka zalika taso Ni fiye da tunanin me tunani, Allah Sarki Baby”.

Sai ya saki murmushi yana komar da hawayen idon sa

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56Next page

Leave a Reply

Back to top button