FAMILY DOCTORS HAUSA NOVEL

FAMILY DOCTORS HAUSA NOVEL 1

Murmushi sosai Baffa yake yi sakamakon jin zantukan ta, tsaban farin cikin jin kalman so a wajen ta, be san sanda ya janyo ta ya rungume ta ba; duk da kuwa ba yau ya soma jin hakan a wajen ta ba

Sosai Ɗahira ta zaro ido da ganin abinda be taɓa faruwa da ita ba, tayi saurin jan jikin ta tana matsawa da sauri

Sai shima a nan ne ya gane abinda ya aikata, yayi saurin saka hannu yana sosa kai cike da murmushi a face ɗin sa yace, “I’m so sorry Ƙanwata, wlh na manta ne”.

Murmushi tayi kawai tana kallon sa, sai kuma ta gyaɗa masa kai

Hakan sai yasa yaji daɗi sosai, don be yi tunani hakan daga gare ta ba, a kullum faɗa masa take yi ba ta ƙaunar irin wannan rayuwan, duk da shi a wajen sa ya saba sosai ga friends ɗin sa da yayi school tare da su, irin wannan rayuwan wayewan shi ne Baffa ya taso dashi, babu ruwan sa don ya rungume mace, amma tun sanda Ɗahira ta soma taka masa birki shima ya rage yi, duk wani halayen sa mara su kyau da yasan za su ɓata mata rai, ya dena su, duk sabida farin cikin ta, shiyasa a kullum sake ji yake yi ƙaunar ta na ƙara wanzuwa a cikin ƙalbin sa, idan har ya same ta a matsayin matar sa kuwa; to, tabbas ya gama dace a rayuwan sa, ita ɗin haske ne cikin rayuwan sa, zai so ya kasance da ita har abada a duniyar sa..

“Yaya mu je kar muyi late”. Tayi maganar tana kallon Wrest watch ɗin dake ɗaure a hannun ta

Murmushi yayi kafin yace, “tom dear”.

A tare suka fita daga gidan.

⚫⚫⚫⚫⚫⚫⚫⚫⚫⚫

    Washe gari aka wayi gari Kaka be da lafiya, zazzafan zazzaɓi ya tashi dashi, sosai hankalin iyalan gidan ya tashi, nan da nan aka ɗunguma aka yi asibiti dashi

Su Ɗahira suna can labari ya riske su, ai nan ko wannen su ya kiɗime, domin ba ƙaramin ƙaunar Kaka suke yi ba, ko kaɗan ba sa son abinda zai taɓa sa, duk da kuwa ya tsufa amma suna matuƙar ƙaunar sa; ba sa son su rasa sa, ga shi be cika ciwo ba shiyasa hankalin su ya tashi da ganin yanda jikin sa yayi mugun zafi.

Gaba ɗaya iyalan gidan sun hallara a bakin ƙofar ɗakin da aka shiga da Kaka, kowa hankalin sa a matuƙar tashe, da yawan su sun kasa zama sai zagaye suke yi, irin su Ɗahira kuwa sun kasa jure wa sai sharan hawaye suke yi.



Su Abbu na ciki su ne masu duba shi, su kansu hankalin su ya gaza kwanciya, sabida halin da suka ga Kaka ya shiga, sun kasa shawo matsalar sai faman zufa suke yi.

[5/31, 12:56 PM] Oummu Ɗahirah: ????????????????????????????????????????
FAMILY DOCTOR’S
????
????????????????????????????????????????

????????????????????????????
NAFEESAT RETURN
????????????????????????????

MALLAKAR:
NAFISAT ISMA’IL LAWAL.

بسم الله الرحمن الرحيم


???????????????????????? ????????????????????????’???? ????????????????????*
®Ɗ???????????? ???????????????????????? ???????? ????????????????????✓

???????????????????? ???????????????????????? ????????✍️

????????????????????????????: ????????????????????????????????????????????????

     \????.????.????????/

????????????????????????????????????????
???????? ???????????????????????????????? ???????? ???????????????????????? ???????? ???????????????? ɗ????????????. ????????????????’???? ????????????????????????.

          *NASIHA*

Sallah tana maganin duk cututtukan da suke samun zuciya. Ita ce haske mai kawar da duhu da zunubai. Abu Huraira ya ce, “Na ji Manzon Allah yana cewa:
“Ku duba nan; idan ɗaya daga cikin ku yana da rafi a bakin ƙofar sa kuma yana wanka cikin sa sau biyar kullum, shin wata ƙazanta tasa za ta yi saura?” Sai suka ce, “Ba wata ƙazantar sa da za tayi saura”. Sai ya ce, “Wannan kamar salloli biyar ɗin nan ne waɗanda da su ne Allah yake wanke zunuban mu”.
A sallah ne ake ganin tahƙiƙanin daidaituwa da adalci. Lokacin da Ladan ya yi kira da cewa: “ku yi gaggawa zuwa Sallah, ku yi gaggawa zuwa ga falala. Duk waɗanda sallar ta rataya a kansu, masu arziƙi da faƙirai, manya da yara, sarakuna da talakawa – dukan su za su taru a sahu guda ba wani bambanci tsakanin su, dukan su bayin Allah ne. Za su taru a bisa aƙida guda a ɗakin Allah, suna tuna Allah kaɗai, suna tawali’u gare shi.

    *EPISODE Twenty Two*


     Wajen awanni biyu da shigar da Kaka, kafin su Abbu su fito, sai dai basu ba ma kowa damar ganin sa ba, sabida a time ɗin sun yi masa alluran barci; yana cikin barci, domin ba sa son ayi hayaniya da zai ja har ya farka daga wannan barcin.



 Gaba ɗaya iyalan gidan sun kasa kataɓus a ranan, ko jirgawa sun kasa yi a baƙin ƙofar, sai da su Big Dady suka yi musu magana ne, akan "su tafi gida," sannan ne su Hajiya suka koma gida, yayinda su Ɗahira kuma suka koma bakin aikin su, but jefi-jefi suna kewayo wa ko Kaka ya farka.



 Har dare be farka ba, haka ilayan Doctor Al'ameen suka kwana a cikin wani hali a wannan ranan, sai washe gari aka samu ya farka, sai dai sosai suka shiga farin ciki a ranan, sabida Kaka ya samu sauƙi tamkar ba shi ba, babu wanda yayi tunanin zai tashi da lafiya haka, sai ga shi har magana yana iya yi, kuma yana iya yin sallan sa, domin tunda ya tashi ya buƙaci a kai sa yayi alwala, sai da ya gabatar da sallolin da ake bin sa, sannan ya samu yaci abinci daƙyar, aka ba shi magani ya sake komawa barci, sakamakon alluran da aka sake mishi, sabida ana son ya sake samun hutu sosai.



  A ranan haka mutane sukai ta zuwa duba sa, gaskiya Kaka na mutane ne, ba ga talakawan ba; ba ga attajiran ba, manyan mutane kama daga ko wani gari duk ana ta zuwa gaishe shi, har mutanen Maiduguri dangin su duk sun zo wasu daga ciki duba sa, su Hajiya Ikram, Hajiya Laila tun a ranan suka shigo Kaduna.


 Kwanan sa biyar a asibitin yana samun kulawa daga ƴaƴan sa da jikokin sa, ya samu sauƙi sosai, sai dai sun hana a mayar dashi gida dole sai ya ƙara samun sauƙi

Shi da kansa ya matsa musu dole suka sallame sa ya koma gida, a ranan sun ga mutanen anguwa, suna ta ɓulɓulowa gaishe da Kaka, da waɗanda suka je asibiti, da waɗanda ma basu je ba duk sun biyo sa gida.

 Bayan kwana uku da sallamo sa ne, wanda ta kama ranan Lahadi, ya saka aka tattaro masa iyalan gidan

Bayan kowa ya hallara ya soma musu jawabi akan abinda ya sa ya tara su, ba komi bane illa maganar aure

“Fodio da takwara na da ku zan so ma, har yanzu shiru ban ji kun kawo min maganar wacce kuke so ba?” Yayi maganar idanun sa a kan su

Shiru suka yi ko wannen su, don basu yi zaton akan hakan ya tara su ba. Sai da Abba yayi musu magana kafin Baffa ya buɗi baki yace, “Kaka Ni dai har yanzu bamu gama daidaitawa da wacce nake so ba, but I will bring it to you in a short time, Calm down baza ka mutu ba insha Allahu sai ka ga auren mu”.

Sosai maganar Baffa ya ba wa waɗansu dariya, sabida yanda yayi maganar cikin barkwanci

Abba kuma daƙuwa yayi masa yace, “ka ga naka Baba na, ba maganar wasa ne ya tara mu anan ba kaji ko?”

Duƙar da kai Baffa yayi yana sosa ƙeya yana murmushi

Haka zalika ma Kaka murmushin yayi yace, “to takwara na Allah ya kawo ta lafiya, sai dai a wannan gaɓar lokaci zan ba ku, sabida ina so nan da wata ɗaya kacal ayi auren ku mu huta, ba wai ku kaɗai ba, ina nufin har ƴan matan, gaba ɗayan ku zaku fid do da miji ayi muku aure”.

Sosai maganar Kaka ya razana Ɗahira dake kusa dashi, dasauri ta ɗago kai ta zuba masa manyan idanuwan ta, kamar an tsikare ta kuma tace, “Kaka, do you mean us?”

Kallon ta yayi yana murmushi yace, “Yes, my wife, I hope all of you will be married in just one month, domin tabbas na san ba zan jima ba a duniyar nan, wannan ciwon ya ɗaga min hankali, shiyasa na yanke shawaran gaba ɗayan ku; ku fitar da mazajen aure sai a haɗa dana yayyin ku, zuwa nan da sati ɗaya na ba ku ko wacce sai ta turo wanda zata aura, kun ji ko?”

Gaba ɗaya amsa mishi suka yi, ban da Ɗahira da tunanin ta ma ya bar duniyar

Sai kuma Usman da tun sanda Kaka ya soma zancen, ya ɗaure fuskar sa tamau, ko ɗago kai ya ƙi yayi, bare kuma yasa baki.

Daga haka Kaka ya sallami kowa taron ya tashi

Ai kamar jira Ɗahira take yi tuni ta bar parlour’n, sabida ruɗewa har so tayi ta bangaji Usman da yazo ficewa shima, Allah ya tsare hakan be faru ba ta dawo hayyacin ta

Wani banzan kallo ya watsa mata yayi hanyar Part ɗin su hannayen sa biyu cikin aljihu.

  Ɗahira bata bi ta kansa ba, tunda ba ta shi take yi ba, yanzu hankalin ta duk a tashe yake, burin ta kawai ta ƙebe tayi tunani, "shin ita wa take dashi ne da zata kawo a matsayin miji? Wannan tunanin shi ne yayi matuƙar wargaza mata duk wani walwalan ta da nutsuwar ta.


   Tana shiga Part ɗin su, ta shige ɗakin su ta yaɗa zango a kan gadon ta, buga tagumi kawai tayi ta hau tunanin mafita, bata ankara ba sai ga hawaye

“Innallillahi wa’inna ilaihi raji’un! What is going to happen to me? By the time I get married no one has ever said he loves me, so who will I choose as my husband?” Tayi maganar a cikin zuciya tana me share hawayen da bayan hannun ta

Sai kuma ta saka hannu ta ɗauki wayan ta ta hau lalubo Numban Masoyin ta na ɓoye, wanda tayi serving Numban sa da My LOVE. Shiru tayi tana tunanin me zata yi, sai kuma ta soma kiran Numban, sai dai a kashe yake, wani yawu me ɗaci ta haɗiye cike da baƙin cikin da taji ya tokare mata maƙoshi, bata taɓa jin haushi irin na yau ba a duk sanda tayi yunƙurin kiran sa, amma wayan a kashe. wannan maganar me muhimmanci ne shiyasa ba ta so suyi sa a text message, tafi son ta Kira sa suna jin muryan juna, sannan ta faɗa masa abinda take so ta sanar masa.

Sai dai babu yanda ta iya haka ta tura masa text message kamar haka:

“Now everything is over between us. If you really want me, then I need you to explain yourself to me at this time. I don’t want you to talk to me again unless you do what I need you to do.”

Abinda ta rubuta kenan ta tura masa, sai ta kwanta tana lumshe idanun ta, tare da zaman jiran reply ɗin sa.

   Bata fi mintuna goma da tura saƙon ba, sai ga reply ɗin sa ya shigo

Da sauri ta tashi zaune ta janyo wayan tana duba wa, sosai tayi farin ciki da amsar da ya bata, murmushi kawai take saki tana karanta wa

“I am also waiting for this day to be beautiful, insha Allahu zuwa gobe zan bayyana miki kaina, just choose me when I come to you.”

Take tayi mishi sending ɗin time ɗin da zai zo, ƙarfe 03:00pm. Tana tura masa ta kwanta tana zuba murmushi, tunanin kawai yanda haɗuwar na su zai kaya take yi, take ta lumshe idanuwan ta tana sake dulmiya a kogin tunanin masoyin nata.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56Next page

Leave a Reply

Back to top button