FAMILY DOCTORS HAUSA NOVEL

FAMILY DOCTORS HAUSA NOVEL 1

Da haka ne Ɗahira take samun sauƙi a cikin ranta, kasancewar ba ta zama ita kaɗai bare ta samu halin yin tunanin dake addabar ruhin ta, wuni suna tare da Aunty Amarya, ko aiki take yi sai ta kira ta ta taya ta, ko kuma Aunty Amarya tace mata “ta fito Parlour su zauna da Fadil su yi hira ko kallo,” dayake Fadil me surutu ne shiyasa yake addabar ta da surutun shi, ko bata so sai ta biye mishi, yayi ta saka ta magana, hakan yasa kaso mafi yawa cikin damuwar ta take gushe wa

Yanzu sallan dare shi ne abun yin ta, koda yaushe tana kai kukan ta wajen Allah ne, da zaran aka ce dare yayi, to bata da sukuni, damuwar ta gaba ɗaya zai dawo mata, ta dinga kuka kenan tana ibada tana kai kukan ta wajen rabbi, Wanda shi ne kawai zai fid da ita a halin da take ciki, a kuma kullum ranan duniya sake jin tsanar Usman take yi a ranta, tana sake jin tabbas idan ta aure sa tamkar ta gama rayuwar farin ciki ne a rayuwar ta. Amma kuma babu yanda zata yi tunda auren nasa shi ne ƙadddaran ta, baza ta iya bijire wa iyayen ta ba, haka Allah ya so.

⚫⚫⚫⚫⚫⚫⚫⚫⚫⚫

           Fannin Baffa kuwa, al’amarin sa yayi ƙamari, duk yanda ya so ya cire Ɗahira a cikin ransa ya gaza, damuwa sosai yake ciki, dole ya koma shan giyan sa, don gani yake yi wannan hanyar ne kaɗai zai bi don samun sukunin zuciya, kullum ranan duniya sai yaje mashaya ya sha, ko kuma ya siyo ya zuba a ɗakin sa ya ɓoye, idan dare yayi ya rufe ƙofan sa ya sha yayi tatul ya kwanta barci

Hakan sai ya soma saka Sa’adatu a cikin ƙunci, domin ko kaɗan yanzu Baffa ba ya da lokacin ta, ta rasa yanda zata yi, har ƙaran sa ta kai wajen Hajja, amma duk faɗan da Hajja tayi masa be fasa ba, yanzu ta kansa kawai yake yi, sai yaga dama yake kula Sa’adatu, shiyasa duk auren ma ya soma fita ranta, tunda yanzu be da time ɗin ta, da zaran dare yayi zai rufe ƙofan shi ya barta, kuma har yanzu bata san yana shaye-shaye ba.
????????????????????????????????????????
              FAMILY DOCTOR’S
                         ????
????????????????????????????????????????

????????????????????????????
   NAFEESAT RETURN
????????????????????????????

MALLAKAR:
                 NAFISAT ISMA’IL LAWAL

بسم الله الرحمن الرحيم


FEENAH WRITER’S ASSO????
”’®Ɗaya tamkar da Dubu”’????✓

JIKAR LAWALI CE✍️

Wattapad: UmmuDahirah????

         \F.W.A????/

SADAUKARWA
Na sadaukar ga Family na gaba ɗaya. GOMA’S FAMILY

Wannan shafin naki ne Shugaba adila, SAFNA ALIYU JAWABI Allah yaja da ranki ya kare ki daga sharrin maƙiya, Allah yasa kifi haka Amin ya allah. ????

.

        EPISODE Thirty Six

         Lokacin da Ayush ta samu labarin maganar auren Usman da Ɗahira, hankalin ta idan yayi dubu, to, ya tashi, domin gani take yi tabbas idan har Usman Ɗahira zai aura, to ta rasa shi, domin babu ta yanda za’a yi Usman ya saki Ɗahira ya aure ta, ya ma za’a yi a haɗa su? Ɗahira tafi ta komi da komi, kyawu, nasaba, kuɗi, da komi ma Ɗahira tafi ta, ko kaɗan bata kama ƙafan kyawun Ɗahira ba, class da komi tafi ta, tasan babu namijin da zai samu kamar Ɗahira ya so ya rabu da ita, dole hankalin Ayush yayi matsanancin tashi, ta samu Safra da maganar ta sanar mata komi

Dariya kawai Safra tayi tace, “yanzu mene ne zai baki tsoro Ayush? Ni kam zan so ganin Lucky Babe ɗin nan da har ta samu the Handsome Guy ɗin ki, ina ga itama ta haɗu gaskiya tunda har ya zaɓe ta matsayin mata”.

Ayush wayan ta ta ɗauka, ta lalubo pic ɗin Ɗahira, wanda suka ɗauka tun waliman da aka yi musu da za su fara aiki, ta nuna wa Safra tana cewa, “Look, kema kin san tunda a family ɗin su ta fito dole zata haɗu, wlh yarinyan nan muddin ta aure sa na rasa shi”.

Sosai Safra ta yaba da kyawun Ɗahira, bata taɓa tunanin zata ganta haka ba, babu abinda ya ƙara tafiya da hankalin ta ya shagaltar da ita irin Sky Green eyes ɗin ta, baki kawai ta riƙe tana faman faɗin, “Wow!”. Sai kuma ta kalli Ayush tace, “Truly the girl is Very Very beautiful! She is very close, ta burge Ni”. Ta ƙare maganar da shafa fuskar wayan tana murmushi. Sai kuma ta sake kallon Ayush tace, “amma kina ganin haɗa su aka yi? Ba soyayya suke yi ba?”

“I don’t know”. Ayush tafaɗa fuska cike da damuwa

Murmushi Safra tayi tace, “tabbas wannan sai aikin Malam, ba na tunanin Usman zai taɓa son ki idan har yana tare da wannan kyakykyawar yarinyan, abu ɗaya kawai zamu yi yanzu, kamar yanda na sanar miki, dole mu san yanda zamu yi mu ɓata ta wajen sa, i mean sharri da tuggu shi ne nasaran mu, duk hanyar da zamu bi sai mun raba su dole”.

“But how? Bayan kin san ƴar uwan sa ce, kuma ya san halin ta”. Ayush ta sake faɗar haka har a time ɗin zuciyar ta cinkushe da damuwa

Killer smaller Safra ta saki, kafin tace, “Let’s try, yanzu abinda zaki yi, ki nemo mana wanda zai yi mana aikin nan”.

Sai a lokacin itama Ayush ta saki murmushi tace, “I have someone to do the work for us.”

⚫⚫⚫⚫⚫⚫⚫⚫⚫⚫

            “Kai Aboki na, kasan kuwa cewa wannan Babe ɗin taka zata yi aure?” Cewar Dr. Sabo dake zaune gaban table ɗin Dr. Sa’id yana juyawa a kujeran

Ɗago kai Dr. Sa’id yayi daga rubutun da yake yi, ya bi sa da kallo yana cewa, “wa kenan?”

“Oh you don’t know? I’m surprised. I mean Dr. Ɗahira Mana, duk a tunani na kai zaka yi wuf da ita wlh, amma fa kayi rashin Sa’a wlh da ka bari ta suɓuce maka duk da Nasan halin ka”. Dr. Sabo ya ƙare maganar yana dariyan shaƙiyanci

Sosai maganar ta bugi zuciyar Dr. Sa’id, cikin wani irin yanayi yace, “Please are you serious or joking?”

“Haba wlh da gaske nake yi, her cousin will also marry Dr. Usman, magana ma har ta baza ko ina a Hospital ɗin nan”.

Shiru Dr. Sa’id yayi

Dr. Sabo yace, “yanzu haka ma two weeks ya rage Ina ga bikin, but wlh ina maka jaje da rashin samun ta, duk a tunani na tuni kun rigada kun daidaita, aure kawai ya rage, ashe ba haka ba”.

Ajiyan zuciya Dr. Sa’id ya saki, kana ya dube sa yace, “ba abinda ke raina ba kenan, in fact ma ban taɓa tunanin auren ta ba, sabida kasan halin matata, baza ta taɓa yarda na sake aure ba, but Ni dama da wata manufa nake son ta, Amma kuma ga shi ina ga Ina son rasa dama ta”.

Dariya Dr. Sabo yayi yace, “well Dama nasan abunda zaka ce kenan, but ban taɓa tunanin itama tana ɗaya daga cikin irin ƴan matan ka da zaka yi wannan rayuwan da ita ba, duba da yanda ita ba halin ta kenan ba, ashe dai kana nan kana target ɗin ta ne”.

Murmushi Dr. Sa’id yayi yana shafa sajen sa yace, “yarinyan ce ta wuce tunani na wlh, kallon farko da nayi mata nayi tunanin bazan sha wahala wajen samun ta a hannu ta zama nawa ba, but duk yanda na so tafi ƙarfi na, uhmmm yarinyan tayi ne Dr. That’s why nake son duk yanda za’a yi na ƙulla alaƙa da ita, koda kuwa bata saba ba, nayi alƙawarin sai na cika buri na akan ta, sai na maishe ta nawa, a kaina zata san daɗin rayuwa. Kuma auren ta ba yana nufin zan kasa cika burina bane”. Sai yayi shiru yana ɗago da kansa daga jikin kujeran, ya ɗaura hannayen sa biyu saman table ɗin yana ɗan buga wa yace, “yanzu ma aka soma, wlh idan har na cika Dr. Sa’id Khan mayen Mata, sai na ɗanɗana yarinyan nan, domin hankali na bazai taɓa kwanciya ba sai na ganni tare da ita a kan gado ɗaya. Har yanzu ta kasa barin ruhi na ya samu sukuni, ta shiga rayuwata da yawa”.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56Next page

Leave a Reply

Back to top button