FAMILY DOCTORS HAUSA NOVEL

FAMILY DOCTORS HAUSA NOVEL 1

“Aff baki san shi ba ashe, yana nan office ɗin sa na kallon nan wajen ta hannun dama”.

“Ok sai na sake zuwa kenan Aunty?” Tafaɗa tana miƙewa tsaye

Murmushi Aunty Zainab tayi tace, “Tom My Sister, ki gaishe dasu Kakus me ran ƙarfe”.

Dariya tayi tace, “insha Allah zai ji”.

Daga haka ta fice bayan sun sake sallama.

   Tana fita kamar yanda Aunty Zainab tace mata hakan tayi ta nufi hannun daman ta, tana zuwa ta soma dudduba sunayen Offices ɗin, nan kuwa taci karo da sunan sa a saman nashi Office ɗin, Nocking ta soma yi

Dr. Said dake zaune yana ma wata budurwa bayani yayi saurin ɗago kansa cike da fargaba, kallon Budurwan yayi yace, “Yi maza ki kwashe magungunan nan ki saka a jaka”.

Babu musu kuwa ta kwashe ta zuba a jakan ta

Shi kuma ya gyara zaman sa yana rufe Files ɗin dake gaban sa tare da kifa wa sannan ya ba da umarnin shigowa

Turo ƙofan Ɗahira tayi da sallama ta shigo

Idanun sa ƙyar a kan ta ya’amsa mata sallaman yana kallon ta, duk da be santa ba amma ya ga tana masa kama da Familyn Dr. Al’ameen

Ita kuwa ƙariso wa wajen Table ɗin sa tayi ta miƙa masa files ɗin tace, “ga shi Aunty Zainab ta ce in kawo maka”.

Sai a lokacin ya ɗan saki fuskar sa yana bin ta da wani irin kallo, cike da murmushi a face ɗin sa ya miƙa hannu ya’amsa yace, “Ok thanks”.

Juya wa kawai tayi ta fice ba tare da ta kalli ko budurwan dake zaune ba

Har ta fice yana kallon ta cike da tsananin burge sa da tayi, sosai Ɗahira ta ɗauke masa hankali da kyawun ta da cikan halittan ta, musamman ma da take siririyan mace, domin yana ƙaunar irin su. sai faman doka murmushi yake yi ya kasa ɗauke kai daga ƙofan da ta fice

Sai da budurwan nan ta buga table kafin ya dawo hayyacin sa

Ɗan shafa kan sa yayi yana kallon ta kafin yace, “kin tabbatar cikin nan be wuce 5 Months ba?”

Kallon sa tayi a yatsine kafin tace, “Dr. Na rigada na faɗa maka wata 4 ne”.

“Ok bari in zo”.

Miƙe wa yayi ya nufi wani dogon sip ya buɗe, ya soma bincika kayan aikin da zai yi mata amfani wajen cire mata cikin.

     Wannan shi ne halayyan Dr. Said, yana cire wa ƴan mata ciki ba tare da sanin kowa a cikin a sibitin ba, domin doka ne idan har aka kama ka kana irin wannan cin amanar za'a kore ka, asibitin kwata-kwata basu yarda da aikata wannan zunubin ba.

                  ⚫⚫⚫

 Ɗahira sai da ta koma Office ɗin ta tayi sallah kafin taje ta ƙara duba patients ɗin ta, tana dawowa ta haɗa komi nata da abinda zata buƙata ta fito ta rufe office ɗin

Office ɗin Baffa dake hawa na biyu ta nufa, dai-dai zata shige cikin office ɗin Yusra ta fito nata office ɗin dake kallon na Baffa, kallon juna kawai su kayi suka ɗauke kai, Yusra har da wani sake tamke fuska ta wuce abin ta tana jan tsaki

Ɗahira juya kanta tayi tana kallon ta cike da mamakin ta, har yanzu ta rasa meyasaka Yusra take nuna mata tsana

Bata gama tunanin ta ba Baffa ya buɗe ƙofan yana kallon ta

Murmushi ta ƙirƙiro tana kallon sa tace, “Yayana na gama”.

“Ok Muje Nima tafiya zan yi na gama na yau kuma”.

Sai da ya rufe ƙofan kafin suka tafi.
[5/23, 11:10 PM] Oummu Ɗahirah: ????????????????????????????????????????
FAMILY DOCTORS
????
????????????????????????????????????????

????????????????????????????
NAFEESAT RETURN
????????????????????????????

MALLAKAR:
NAFISAT ISMA’IL LAWAL

بسم الله الرحمن الرحيم


FEENAH WRITER’S ASSO????
®Ɗaya tamkar da Dubu????✓

JIKAR LAWALI CE✍️

Wattpad: UmmuDahirah????

     *\F.W.A????/*

SADAUKARWA
Na sadaukar ga Family na gaba ɗaya. GOMA’S FAMILY

Ga masu min magana akan littafin JARUMAI kuyi haƙuri don Allah an samu matsala ne shiyasa na dakata amma insha Allahu zan ci gaba very soon.

.

    *EPISODE Twelve*

 Fitowar ta kenan daga wanka taji wayan ta tayi ƙaran shigowar Text, kallo ɗaya tayi wa wayan ta ɗauke kai ta nufi gaban dressing mirror, zama tayi kan stool tana tsane gashin kanta, bayan ta gama sai ta ɗau handrayer ta soma busar da dogon baƙin gashin nata me tsananin santsi, sabida santsin sa ne ma ba ta yin kitso sai dai ta riƙa gyarawa

Ajiye handrayern tayi bayan ta gama ta soma shafa Lotions ajikin ta, tana gamawa tayi Light makeup a baby face ɗin ta, sai ta miƙe ta ciro kayan ta tasaka

Doguwar riga ce robber kalan ruwan hanta, babu kwalliya a rigan ko ɗaya sai dai wuyan V yake dashi wanda aka saka masa bakin less white colour, haka ma dogon hannun a ƙarshen an saka masa bakin less, Hula ta saka fari wanda ya kasance na rigan ne, tayi kyau sosai kasancewar ta kyakykyawar

Wayan ta kawai ta ɗauka ta fito Parlour.

 Fadila na zaune tana cin abinci at the same time tana latsa wayan ta

She Sit on the One sitter next to Fadila on the Two sitter

Ɗan kallon ta kawai tayi sai ta ɗauke kanta ta mayar kan plasma t.v dake aiki babu me kallo, shiru tayi na ɗan wani lokaci sai kuma ta ɗago wayan ta ta soma latsawa

Da text ɗin da ya shigo wayan ta ɗazu ta fara cin karo, har zata wuce kuma sai ta ga kamar da number akayi mata Text ɗin wanda ada azaton ta MTN ne su kayi mata

Buɗe wa tayi da mamaki take kallon text ɗin, har sake murza idanuwan ta tayi tana sake ƙura manyan idanun nata, jikin ta na rawa ta soma karanta wa:

“Aslm alaikum ya ke kyakykyawa abar so ga kowa, za kiyi mamakin ganin wannan text ɗin nawa aduk lokacin da ya riske ki, amma ba abun mamaki bane domin an ce me son ɗan tsuntsu shi ke bin sa da ji fa, Ɗahira na daɗe da ƙaunar ki cikin zuciya ta, sai dai har yanzu na kasa fitowa fili na sanar miki, ba don komai ba sai don ban san ya zaki amshe Ni a matsayin Masoyi ba, but know that I love you and I will continue to love you until my breath goes out, I Love You .. I love You with all my heart.”

    _MASOYIN KI✍️_

Ta maimaita text ɗin ya fi sau biyar, gaba ɗaya ta ruɗe domin abin da bata taɓa gani bane a gare ta, tunda take babu wanda ya taɓa nuna yana son ta kuma babu wanda ya taɓa tura mata text da sunan masoyin ta, hakan ne ya saka ta shiga wannan ruɗun tare da bugawar zuciya me tsanani

Zumbur ta miƙe ta nufi ɗakin su

Fadila tabi bayan ta da kallo cike da mamakin sauyawan ta lokaci ɗaya, amma sai dai bata ce komi ba ta maida hankalin ta kan wayan ta.

Tana shiga ta nufi kan gadon ta ta zauna, sake ɗago wayan nata tayi ta sake karan ta text ɗin

“Anya wanda ya turo text ɗin nan ba mistake yayi ba?” Tafaɗa cikin sanyin murya tana bin wayan nata da kallo

Ƙure Numban tayi da idanu ko za ta san me irin shi but ko kaɗan bata taɓa ganin ma irin Numban ba, domin kuwa sabon Numban da MTN suka fito dashi ne me 091

Har ta latsa da ninyan kira taji ko wane ne sai kuma ta yanke da sauri don bata san me zata ce ɗin ba ko da an ɗauka, zuciyarta ta bata shawaran kar ta sake ta kira wataƙil mistake ne aka yi, kuma be kamata ta kira ɗin ba, da haka ta’ajiye wayan ta kwanta tana tsira wa waje ɗaya idanu cike da tunani

Da sauri kuma ta tashi zaune tana faɗin, “amma kuma ya kira suna na ai, Of course I am. This text is for me, but who is it?”

Duk yanda taso yin tunanin gano wanda zai iya mata amma ta kasa, koma wa tayi ta kwanta tana ajiyan zuciya.

       ⚫⚫⚫

Yana kwance saman kujeran sa yana faman latsa wayan sa yana murmushi

Wayan ce ta soma ringing hakan ya saka ya dakata da abinda yake yi yana kallon baƙuwar Numban da aka kira sa, shiru yayi na ɗan wani lokaci kafin yayi peacking call ɗin ya saka a kunne

Daga can ɓangaren muryan mace ce ta doki dodon kunnen sa

“Aslm alaikum”.

“Wa’alaikis salam”. Slowly he gets up and sits up

She smiled and said, “Do you know who Dr. Al’ameen Abubakar Al’ameen is?”

Baffa da yayi tsimi yana sauraron muryan ta sai be ce komi ba

Hakan ya bata damar ci gaba da faɗin, “My name is Dr. Ayush Abdulkarim and I work at your Family Hospital.” Sai kuma tayi shiru tana tunanin abinda zata ce

Baffa yace, “to Allah yasa dai lafiya? But I don’t know you.”

She smiled and said, “Yes, you will never know me because I have just started working at the hospital, but idan har ka bani dama zan iya bayyana maka kai na domin mu san juna, tunda ina son alaƙar mu tayi nisa ne, that’s why.” so I asked for your number and I called you “.

Shiru yayi cike da mamakin ta

“To me zai sa ta so ƙulla alaƙa dashi?..”

Be gama guntun tunanin sa ba ta katse sa da faɗin, “I’ll meet you tomorrow insha Allah, I’ll come to your office. Byee Take care.” Bata jira me zai ce ba ta kashe wayan

Shi kuma ya ciro wayan yana kallo, ya jima a haka yana tunani kafin ya’ajiye wayan ya miƙe ya shige toilet don ɗauro alwala.

⚫⚫⚫⚫⚫⚫⚫⚫⚫⚫

   Dariya suka kwashe dashi har da tafa wa

“Wow gaskiya kin yi ƙoƙari Ayush, amma kina ganin zaki iya jawo hankalin shi gare ki har ya manta da wancan shashashan?”

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56Next page

Leave a Reply

Back to top button