FAMILY DOCTORS HAUSA NOVEL

FAMILY DOCTORS HAUSA NOVEL 1

Matar kallon drever’n da ya fito cikin motan tayi tace, “Ali where are you doing now?”

“I will go to the hospital because Alhaji said, ‘If I drop you off, he will sent me.'”Ali said respectfully.

Gyaɗa kanta tayi kana tace, “ok go, idan ka dawo I’ll sent you later”.

“To Hajiya”.

Daga haka juyawa tayi ta nufi cikin gidan, Matashiyar yarinyan itama tabi bayan ta. koda suka shiga ciki Direct Part ɗin su suka nufa, lokacin da suka shiga cikin ɗan madaidaicin parlour’n su da sallama a bakin su

Fadila ce zaune tana kallo ta’amsa musu

“Welcome Aunty” Fadilan saying

“Yauwa Fadila, ke kaɗai ce zaune?” Aunty Amarya tace hakan cike da fara’a tana kallon ta

Fadila ta bata amsa da “Eh su Umma na General parlour”.

“Ok mu ma ai bamu shiga cikin gidan ba nan muka taho, bari in shiga ɗaki in yaso sai in shiga can mu gaisa”.

“Toh aunty”.

Wuce wa ɗakin ta Aunty Amarya tayi

ita dama tuni Ɗahira ta wuce tasu ɗakin wanda ya kasance tasu tare da Fadila, tana shiga ta’ajiye Jakan dake hannun ta ta zauna gefen gadon ta, zare ɗankwalin da tayi Rolling a kanta tayi ta’ajiye tana bin gadon ta kwanta, kanta na kallon sama yayin da ta ƙure Cilling ɗin ɗakin da kallo, ta ɗan jima ahaka kafin ta sauke ajiyan zuciya tana lumshe kyawawan idanuwan ta, sai kuma ta buɗe ta tashi zaune tana zare Glass ɗin idanun ta ta miƙe ta nufi gaban Looking glass ta buɗe Locker ta’adana, darect Sif ɗin kayan ta tanufa ta ciro wasu riga da wando na Pakistan Milk and Red colour ta zube su saman gado, kayan jikin ta ta soma cire wa kafin ta ɗaura towel ajikin ta tashige toilet, wanka tayi ta ɗauro alwala ta fito, sai da ta shafa Lotions ajikin ta kafin ta saka kayan ta ɗaura Hijab tayi sallan asar da ta wuce su tun a hanya, bayan ta gama ne ta nufi wajen Looking glass ta zauna tana kallon kanta a madubi, tagumi ta zuba still tana ci gaba da kallon kanta

Fadila ce ta shigo ɗakin idanunta ya sauka akanta, sai ta taɓe baki tana ƙarisawa wajen ta tace, “Are you all right?”

Sai a lokacin Ɗahira ta ɗago kanta tana kallon ta, sai kuma takau da kan tare da faɗin “me kika gani?”

Fadila batace komi ba ta juya ta tafi, dama wayan ta tazo ɗauka, tana ɗauka ta fice a ɗakin, wannan shi ne halin su su duk ka biyun basu cika kula juna ba duk da duk kan su suna da ƙyaliya, But kasancewar Iyayen su suna kishi shiyasaka su ma suke taya su a junan su, ga dai shi ɗaki ɗaya suke kwana amma sai su wuni su hantse ba wacce zata kula ƴar uwanta, ba me shiga harkar ɗaya sai sun ga dama, ita dama Ɗahira ƴar ba ruwanta ne, bata cika shiga shirgin da ba nata ba, bata da son hayaniya amma tana da fara’a da kirki, komi tana yin abinta ne cikin class, sai dai alokaci ɗaya baza ka taɓa fahimtar halin ta ba sai ka zauna da ita, Fadila ma haka sai dai wani lokacin tana da yawan wulaƙanci a ɗabi’a, domin miskilancin ta yayi yawa don in bata ga dama ba ko kai uban waye baza ta kula ka ba sai taga dama.

Ɗahira cire tagumin tayi ta soma shafe Baby face ɗin ta da kayan makeup, ita gwanar son gayu ne duk sanda zaka ganta bata rabo da kwalliya, Light makeup tayi wanda ya ɗau fuskarta sosai ya ƙara fito da zallan kyawunta, ba maganar wasa ba Ɗahira tana ɗaya daga cikin kyawawan gidan, duk a cikin ƴan matan gidan zan iya cewa tafi su kyau duk da suna matuƙar kama, sai dai ita yanayinta da komi nata ya banbanta da nasu

Buɗe Lockern tayi ta ciro Glass ɗin ta tasanya Wanda ya zame mata ɗabi’a ko yaushe idan zaka ganta tana tare dashi, sai ta miƙe ta nufi gaban gadon ta taɗau wayan ta ƙirar IPhone 11+, takalmin ta kawai ta sanya ta fito batare da ta yafa komi ajikin ta ba baya ga ɗankwali da ta sanya ta rufe tulin gashinta, tana fitowa parlor ta hangi Fadila zaune har yanzu, sai dai wannan lokacin wayan ta take dubawa, ɗakin Mahaifiyar ta tawuce, tana shiga babu kowa hakan yasa ta fito ta doshi cikin gidan, sai da ta wuce wani dogon corridor kafin ta buɗe wani ƙofa ta shige, ahankali ta soma taka Step tana sauko wa sai gata cikin wani kyakkyawan parlour ƙarami, sai tabi ta wani ƙofan ta fito babban parlor’n gidan da ya kasance cike da mutane kowa sai harkan gaban sa yake yi, tana isa ta gaishe dasu sannan ta wuce wajen ƴan matan dake can gefe zaune, zama tayi gefen Shakira da Salma (ƴa ga Hajiya LAILA),

Shakira CE ta soma cewa, “Now I ask Aunty Amarya where are you? She told me kina Sashin ku ai”.

Ɗahira She smiled and said, “na tsaya wanka ne”.

Fiddausi da ta kasance ƙanwar Salma tace, “to ya Naga hannayen ki rabbana suna dukan cinya, ina tsaraban tamu?”.

Kallon ta Ɗahira tayi tace, “What are you eating na baka na zuba? Let me rest for a while, sai ki zo ki taya ni kwance jakan”.

Gaba ɗaya wajen su kayi dariya ban da Yusra dake faman latsa wayan ta ko ɗago kai bata yi ba

Shakira tace, “kin ji ƙyale wannan yarinyan bata da hankali, ke da akaje Duba marar lafiya kike zancen tsaraba?”

Ɗage gira Fiddausi tayi tace, “to kuma akace idan anje baza’a yi tsaraba ba? Nasan da cewa waɗannan tsofaffin baza su barta haka ba sai sun haɗo ta da abin lasawa”.

Shamsiyya (ƴa ga Hajiya Ikram) tace, “ƙwarai kuwa Fido sai dai idan mu baza’a bamu ba, don naga tunda ta shigo Shakira take ƙifƙifta mata idanu”.

Salati Shakira ta saki tana rufe bakin ta tare da zaro idanu, sai suka saki dariya suna shewa, wasu suce “eh su ma sun gani” wasu kuma suce “kai Shamsiyya banda ƙarya”.

Dogon tsaki Yusra taja ta miƙe ta wuce abin ta, yayinda duk kan su suka bi ta da idanu kana Salma tace, “Oh, that juju girl, what’s wrong with her?”

Dawo da idanun ta Ɗahira tayi gare su tana murmusawa tace, “Ni kun ga tafiya na bari inje in miƙa gaisuwata ga Kaka tunda naga ban ganshi anan ba”.

Tafa hannu Fiddausi tayi tace, “ai Kaka yau sai dai yayi haƙuri mun hana sa fitowa, cewa yayi bazai iya da surutun mu ba ya shige ciki ya kwanta”.

Tashi Ɗahira tayi tana faɗin “ai gwara haka kar ku ƙara masa damuwa”.

Daga haka ta wuce batare da ta kula su da sukayi mata caaa ba.
[5/21, 3:29 PM] Oummu Ɗahirah: ????????????????????????????????????????
FAMILY DOCTORS
????
????????????????????????????????????????

????????????????????????????
NAFEESAT RETURN
????????????????????????????

MALLAKAR:
NAFISAT ISMA’IL LAWAL

بسم الله الرحمن الرحيم


FEENAH WRITER’S ASSO????
”’®Ɗaya tamkar da Dubu????✓”’

JIKAR LAWALI CE✍️

Wattpad: UmmuDahirah????

     *\F.W.A????/*

SADAUKARWA
Na sadaukar ga Family na gaba ɗaya. GOMA’S FAMILY

NATSUWA A SALLAH
Sallah babbar matsala ce. Ganawa ce tsakanin Bawa da mahaliccin sa, Ubangiji maɗaukakin sarki. Saboda haka ana buƙatar cikakkiyar natsuwa, a tattara hankali wuri ɗaya domin wannan ganawa ta musamman.
A cikin ayoyi biyun farko na suratul Mu’uminun ana faɗa mana cewa:
“Lalle ne, muminai sun sami babban rabo, wanɗanda suke a cikin sallar su masu tawali’u ne.”
Watau, Muminai wanɗanda idan sun tsaya yin Sallah sai gaɓoɓin su da zukatan su su natsu, babu wani abu mai shagaltar da su daga ambaton zatin Allah maɗaukakin sarki, to, irin su suke rabban ta. Natsuwa cikin sallah da ƙasƙan da kai ga Allah su ne alamun imani na gaskiya da Tauhidi tsantsa, don kuwa ko yaushe bawa yayi kusa da Ubangijin sa sai ya haɗa jin tsoron sa, musamman ma dai a sallah inda yake ganawa da shi, yake tunawa da girman sa.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56Next page

Leave a Reply

Back to top button