FAMILY DOCTORS HAUSA NOVEL

FAMILY DOCTORS HAUSA NOVEL 1

Daga Ayush da tun zuwan Fadilan take kallon ta har Shakira bin bayan ta da kallo suka yi har ta ɓace ma ganin su

Tsaki ne ya biyo bayan shirun nasu

Ayush ta kalle ta da mamaki tace, “mene ne ƙawata?”

Sai da Shakira tayi ƙwafa kafin ta buɗe motan tace, “Allah Fadila tana baƙanta min rai idan nayi mata maganar Ɗahira take nuna halin ko in kula wanda Ni ba hakan nake so ba”.

Dariya Ayush tayi duk da bata fahimci me take nufi ba, ta nufi ɗayan side ɗin ta buɗe ta shiga, itama Shakiran shiga tayi ta rufe ƙofan tare da jan motan suka bar haraban Hospital ɗin.

       ⚫⚫⚫

           Kai tsaye hawa na uku ya wuce inda a nan ne office ɗin sa yake, Office ɗin na kallon na Ɗahira ne

Buɗe wa yayi ya shiga ya rufe, kallon ko ina yake yi da idanu fuskar sa babu fara’a, ko kaɗan ba ya farin ciki da kasancewar sa a nan ɗin, jin sa kawai yake yi cikin takura kuma hakan ne ya ƙara ɓata masa rai sosai

Duk da office ɗin yana da girma, ga shi ya haɗu tako ina amma shi be burge shi ba ko kaɗan tunda ko kwatan nashi na ƙasan Turkey be yi ba

A hankali ya soma takawa ya nufi kan kujeran ya zauna yana kwantar da kansa jikin kujeran, ya lumshe idanun sa yana jujjuya wa cikin kujeran, numfashi kawai yake sauke wa ba tare da ya motsa ba tsawon lokaci, sai da wayan sa ta soma ringing ne sannan ya buɗe idanun sa yana ɗago kai yabi wayan da kallo a inda ya’ajiye saman table, ganin sunan Dady na yawo a screan ɗin wayan hakan yasa shi sanya hannu ya ɗauka ya kanga a kunne bayan yayi peacking call ɗin, shiru yayi yana sauraron sa kafin ya buɗe baki a hankali yace, “Eh na zo”.

Kallon files ɗin gaban sa yayi, sannan ya yamutsa fuska yace, “ok”.

Sai ya cire wayan a kunnen sa yana ajiye wa, ya sake maida kansa jikin kujeran ya rufe idanun sa

Bayan mintuna biyar ya jiyo Nocking, iznin shigowa ya bayar ba tare da ya motsa ba

Ɗaya daga cikin staff’s ɗin asibitin ne ta shigo, ta gaishe sa but ko amsa ta be yi ba, kamar ma be san da wanzuwar ta ba

“Dr Noor told me to bring this to you.”

Hannu ya nuna mata alamun ta ajiye a table

Don haka babu musu tayi yanda yace mata sannan ta juya ta fice

A ƙalla ya ɗau tsawon mintuna goma kafin ya buɗe idanun sa ya ɗago kai yana kallon files ɗin gaban sa, numfashi yaja me ƙarfi sannan kuma ya ɗaura kansa saman table ya sake rufe idanun sa be da alaman yin abinda ya kawo sa.

     ⚫⚫⚫


     Hannun yarinyan ta riƙe tana kallon ta cike da tsantsan tausayi, wai yarinya ƙarama kamar wannan ace an yi mata Fyaɗe, kee duniya ina zaki damu ne? Mene mutane suke nema a kan ƙaramar yarinyan da bata fi shekara biyar ba?

Numfashi taja tana sanya hannun ta kan yarinyan ta soma shafa mata gashi, ko kaɗan yarinyan ba ta motsi, ba ma zaka san tana da numfashi ba sai idan ka ƙura mata idanu sosai zaka ga tana fitar dashi ɗai-ɗai ta cikin Oxgyen ɗin da aka sanya mata

Ta jima tana kallon yarinyan wanda a baɗini tunani ta lula a kan abinda ke faruwa a ƙasar mu, wanda Fyaɗe ya zama ruwan dare a wannan zamanin

Hannun ta tajanye ta miƙe daga kan gadon ta fito waje

Matar dake zaune bakin ƙofan a ƙasa tana kuka ta ɗago kai da sauri tana kallon Ɗahira, sai kuma ta miƙe cikin rawan baki tace, “Likita..”

Kuka ne yaci ƙarfin ta dole tayi shiru

Ƙwallan da ya cika mata idanu na tsaban tausayin matar da ƴarta ta share sannan ta dubi matar a tsanake tace, “Calm down, she will be relieved by God’s will, but follow ME and we will talk”.

Kallon ta Matar tayi alamun kamar bata fahimta ba

Hakan yasa Ɗahira ta sake maimaita mata da Hausa, “ki kwantar da hankalin ki zata samu sauƙi da yardan Allah, amma ki biyo NI ofiice muyi magana”.

Gyaɗa kanta tayi tana saka gefen zanin ta ta share hawayen ta da suka haɗe da majina, sannan tabi bayan Ɗahira da har ta soma tafiya

Office ɗin ta suka zarce, sai da suka zauna sannan Ɗahira ta kalle ta tace, “zan so ki bani bayani a kan abinda ya faru, sam abun be min daɗi ba kuma tabbas dole ne hukuma ta ɗau mata fansa”.

Numfashi taja kafin taci gaba, “Mun rigada mun cire spain ɗin waɗanda sukai mata wannan aika-aikan, kuma insha Allahu idan result ya fito zamu miƙa case ɗin ga hukuma domin abi mata haƙƙin ta”.

Cikin kuka Matar ta soma magana da faɗin, “Likita mun rigada mun bar su da Allah, sam baza mu iya Shari’a dasu ba domin kuwa waɗanda suka aikata mata hakan sun fi ƙarfin mu nesa ba kusa ba, Ni fata na Allah ya tashi kafaɗun ƴar mu domin kuwa ban san me zance wa Mahaifin ta ba idan ya dawo ya tarda abinda ya faru..” Sai ta fashe da kuka tana ɗaura hannun ta ɗaya saman fuskarta

Kallon ta kawai Ɗahira take yi na tsawon lokaci kafin tace, “kar ki damu dole ne mu miƙa wannan case ɗin ga hukuma, domin a yanzu zancen da nake miki Human right sun shiga zancen nan, kuma ya kamata ki kira mijin naki duk inda yake yazo ya ga abinda ya faru hakan shi ne maslaha, sannan ina so muyi magana dashi”. Taƙarike maganar tana janyo Pepper gaban ta taɗau Bairo ta soma rubutu

Matar bata ce komi ba sai kukan ta da take yi

Miƙa mata Peppern da ta gama rubutu tayi, “Ki je ki siyo wannan alluran ina buƙatar su yanzu”.

Hannu ta saka ta’amsa tana jan majina, “Na gode Likita Allah ya saka da alheri”.

Murmushi kawai Ɗahira tayi mata bata ce komi ba, tana bin ta da kallo har ta fice sannan ta kau da kanta tana sauke ajiyan zuciya, hannu biyu ta saka ta tallabo haɓan ta bayan ta ɗaura gwiwowin hannun saman table, sosai take cikin damuwa akan abin da ke faruwa da yaran mutane

“Wai shin mene ne matsalan hakan? Meke jawo yawan Fyaɗe a wannan lokacin? Sannan mene ne mafita?”

Nocking ɗin da aka yi yasaka ta dawowa hayyacin ta, numfashi taja tana kallon Baffa da ya turo ƙofan ya shigo.
[5/28, 9:55 AM] Oummu Ɗahirah: ????????????????????????????????????????
FAMILY DOCTORS
????
????????????????????????????????????????

????????????????????????????
NAFEESAT RETURN
????????????????????????????

MALLAKAR:
NAFISAT ISMA’IL LAWAL

بسم الله الرحمن الرحيم


FEENAH WRITER’S ASSO????
”’®Ɗaya tamkar da Dubu????✓”’

JIKAR LAWALI CE✍️

Wattpad: UmmuDahirah????

\F.W.A????/

SADAUKARWA
Na sadaukar ga Family na gaba ɗaya. GOMA’S FAMILY

EPISODE Eighteen

  "Yayana baka tafi ba?"

Murmushi yayi ya tako ya zauna yana cewa, “yanzu na tashi nace bari inzo inga ƙanwa ta”.

“Allah Sarki Yayana, ina to budurwan taka ko ta tafi ne?” Tayi maganar tana dariya

Shima dariyan yayi yace, “kai sis yaushe nace miki budurwa ta ce?”

Ɗage kafaɗa tayi tana taɓe baki tace, “Ni naga alama ne ai”.

“Serious ba budurwa ta bace freindship ne kawai a tsakanin mu”.

“Anya Yaya ban yarda ba?”

Langaɓe kansa yayi yace, “shikenan tunda baza ki yarda ba?”

Ɗahira dariya tayi tace, “na yarda to, yaushe ne kuma zaka haɗa ni da budurwan ka ko sai ka kawo ta gida ne zamu ganta?”.

“Very soon lokaci nake jira ai”.

Ɓata fuska tayi tana shirin magana aka yi Nocking

“Yess come in”. Tafaɗa idanun ta a kan ƙofan

Matar da ta fita ɗazu ne ta dawo

“Sis bari in tafi sai mun haɗu a gida”. Baffa yafaɗa yana miƙe wa

“Ok Byeee Yaya”.

Sannan ta kalli matar tace zauna

Zama tayi kamar yanda ta buƙata sannan ta miƙa mata alluran da ta siyo

Amsa Ɗahira tayi ta duba kafin ta kalli matar tace, “Shin Mijin naki ya zo?”

Girgiza kanta tayi sannan tace, “yana Zaria ne a yanzu haka, sai dai kuma na faɗa masa yace min yana kan hanyan dawo wa”.

Gyaɗa kanta tayi kafin tace, “to ki je ki kula da ita, Dr. Rahab zata riƙa zuwa ta duba ta, idan ya ƙariso sai ku taho tare ina son ganin ku”.

Jinjina kanta matar tayi sannan ta miƙe tayi hanyar ƙofa ta fice

Waya ta ɗauka tayi kira sannan ta kara a kunne

“Ki zo ina son ganin ki”. Abun da tafaɗa kenan kafin ta’ajiye wayan taci gaba da duba files ɗin gaban ta

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56Next page

Leave a Reply

Back to top button