FAMILY DOCTORS HAUSA NOVEL

FAMILY DOCTORS HAUSA NOVEL 1

“I will never forget her in my life. har yanzu zanen halin ta na nan daram cikin raina”.

Murmushi kawai Ɗahira take yi tana kallon Kakan nata, sai da ya dasa aya a maganar nasa sannan tace, “Grandpa tell me about the day you first met her”.

Sai ko Kaka ya saki dariya me sauti, ga duk kan alamu ya tuna wani abu ne, cikin murmusawa yake cewa, , “This is the day I will never forget in my life, ranan da na haɗu da Babyna matata abar ƙauna ta, lokacin da naje Hospital ɗin da nake aiki, a bakin Hospital ɗin na kusa bige ta da motata, hakan ya saka ta tsorata har ta faɗi taji ciwo a hannu sannan kuma nayi mata asaran shinkafan da take siyarwa”.

Ƙwalalo idanu Ɗahira tayi tace, “Kaakaa Talla?”

Dariya yayi yace, “eh Talla, ai talla naga take yi lokacin da muka fara haɗuwa, Hmm my Baby taga rayuwa duk da kasancewar ta ƴar gata don mahaifin ta me kuɗin gaske ne..”

“To amma Kaka ya akayi ta koma yin talla?” Ɗahira ta katse sa da tambayan nan

“Ƙaddara, ko ince canjin rayuwa”.

“To Kaka ya kuka ƙare da ita kuma wani kalma ta soma shiga tsakanin ku? And kuma lokacin ne ka soma sonta?” ta sake tambayan sa cike da zumuɗi da son jin labarin

Murmushi Kaka yayi yana lumshe idanun sa, sai ya buɗe a kanta yace, “kalman da ta soma fitowa a baki na shine haƙuri na bata, sannan ne ta ɗago ta kalle ni, tabbas kallon farko da nayi mata na kamu da matsananciyar ƙaunar ta, kuma sai na nemi alfarman tabi ni inyi mata dressing hannun, da farko bata da ninyan bi na but mutanen da suka taru wajen ne suka saka ta taje, kalman da na soma ji a bakin ta har ta tafi sunan ta kaɗai ta faɗa min”.

“Kaka kasan me?”

Girgiza mata kai yayi yana kallon ta

Murmushi tayi da ya bayyana ƙananun haƙoran ta tace, “abinda yake bani mamaki da burgewa yanda ka auri Mata har uku masu suna ɗaya, ko a Film da littafai ban taɓa ganin hakan ba, kuma har kayi rayuwa dasu alokaci ɗaya”.

Shima murmushin yayi yace, “Allah kenan shi ya ƙaddara hakan, gashi ke kuma kin zo a ta huɗu”.

She laughed and said, “Show me the other pictures, ka ga har yanzu bansan sauran matan naka ba ko a hoto ka ƙi ka nuna mana, wancan ƴar uwan taka da tayi aure a ƙauye kawai nasan zan iya tunawa, tunda nasan ta muna yara kafin ta rasu”.

Jakan ya buɗe ya kuma zaro wani hoton ya miƙa mata

Hoton ta’amsa tana kallon matashiyar da aƙalla zata kai shekara 19 zuwa 20, fara ce sol kyakykyawar bafulatana, da sauri Ɗahira ta ɗago kai tana kallon Kaka tace, “Laa Kaka wlh wannan sak Big Dady, ba su da maraba kamar tayi kaki ta ajiye”.

Murmushi yayi yace, “Matata ta farko kenan UMMEE NAFEESA, Mace ƴar aljanna me tsananin haƙuri, dattako da sanin ya kamata, bazan iya fasalta miki kyawawan halayyan ta ba, wannan hoton anyi sa ne gab da zata rasu, Ni na ɗauke ta a waya shine na ba da aka wanko min, Allah Sarki ta rasu da ƙuruciyarta, ta rasu lokacin da nake matuƙar buƙatar ta, ta rasu sanda ta gama naƙudan Noor (Big Dady) batare da ta ganshi ba ta koma ga Allah. Allah ya jiƙan ki da rahma Ummeeta”. Kaka ya ƙarike maganar tasa yana share hawaye

Itama Ɗahira har sai da tayi nata hawayen sabida tausayi sannan tace, “ameen Kaka, may Allah have mercy on them all”.

Amsan hoton yayi ya maida a jaka, yana shirin rufewa Ɗahira ta saka hannu ta zaro wasu hotunan biyu tana cewa, “Kaka ka bari mana ka gama min bayani, wannan kuma yaron me tsananin kama da kai wanene?”

Ta nuna masa hoton ɗan ƙaramin yaro dake wasa da kayan wasan da aka zube masa da yawa a gaban sa

“Yarona na farko kenan sunan sa Arif, Sunan Kakana yaci Khabeer, amma tun yana ƙarami ya rasu”.

Ɗahira tace, “laa Kaka ashe ban da Big Dady dama kayi wani yaron? Wacece maman shi?”

Hoton hannun ta ya nuna mata

“Ga Maman shi nan cikin hoton nan”.

Shafa hoton Ɗahira tayi da hannun ta tana murmushi, hoton KAKA ne da Ƙannin sa biyu Baseera da Ihsan sai kuma Nafeesa mahaifiyar Arif”.

“Kaka kuna tsananin kama sosai duk kan ku kowa ya gan ku ya san ƴan uwan juna ne”.

Murmushi kaɗai yayi ya miƙa hannu ya’amsa hoton sannan yace, “kawo in mayar zanyi sallah”.

“So what about the story Kaka?”

“Ki bari duk sanda na sami lokaci zan tara ku gaba ɗaya in baku cikakken labarin aurena dasu”.

“Yauwa Kakus ɗin mu, Allah yakai mu to”.

Bayan ya zuba hotunan ya bata jakan ta mayar, ita ta tura sa har Toilet ta zuba masa ruwa yayi alwala sannan ta tafi part ɗin su bayan ta bar sa nan cikin ɗaki yana Sallah.

Tana zuwa Parlour’n su da Fadil taci karo yayi ɗai-ɗai yana kallo

“Yauwa Aunty Ɗahira kin bar wayan ki ana ta kira”.

Bata ce komi ba ta wuce cikin ɗakin nasu, ƙarar zuban ruwa tajiyo a Toilet ta san Fadila ce, zama tayi ta ɗau wayan tana duba missed calls ɗin da akayi mata, Baffa ne ya kira ta, itama kiran sa tayi but be ɗauka ba, sai ta’ajiye wayan ta ɗau Novel ɗin da take karantawa JARUMAI ta gyara zamanta ta soma karanta wa kafin Fadila ta fito daga Toilet tayi alwala.
[5/23, 3:56 PM] Oummu Ɗahirah: ????????????????????????????????????????
FAMILY DOCTORS
????
????????????????????????????????????????

????????????????????????????
NAFEESAT RETURN
????????????????????????????

MALLAKAR:
NAFISAT ISMA’IL LAWAL

بسم الله الرحمن الرحيم


FEENAH WRITER’S ASSO????
”’®Ɗaya tamkar da Dubu????✓”’

JIKAR LAWALI CE✍️

Wattpad: UmmuDahirah????

     *\F.W.A????/*

SADAUKARWA
Na sadaukar ga Family na gaba ɗaya. GOMA’S FAMILY

.

    *EPISODE Ten*



   *WASHE GARI*

   BAFFA ne jingine jikin motar sa yana duba waya, yana sanye cikin ƙananan kaya kamar yanda ya saba waɗanda suka matse sa sosai, kansa da askin zamani da yayi masa kyau sosai, sai faman shaining yake yi alamun ya sha mayuka masu tsada

Shakira CE tafito cikin shirin ta, tana tafiya ɗai-ɗai kamar baza ta taka ƙasa ba, har ta wuce ta hangi Yayan nata tsaye wajen motan sa, sai ta juyo tana kallon sa taɗan ɗaga murya tace, “Yaya inzo mu tafi tare ne?”

Lokacin ne Baffa ya ɗago kansa yana kallon ta, sai da ta samu harara kafin yace, “Where is your car and I will take you?”

“Here’s Yaya, wlh I don’t feel good about my body that’s why I don’t like driving”.

Gajeren tsaki ya ja yana ɗauke kai a kanta yace, “babu inda zan kai ki ki nemi drever”.

Har ta buɗe baki da ninyan yin masa magiya sai taga yana kallon hanyan ƙofar shiga gidan yana sakin murmushi, itama juya kai tayi ta kalli wajen

Ɗahira ce ta fito sanye da Jan abaya me kwalliyan Flower’s da stones a jiki, tayi Rolling da ɗankwalin Rigan, face ɗin ta sanye da ɗan siririn farin glasses ????ɗin ta wanda ya ƙara wa Sky Green ɗin cikin idanuwan ta kyawu, tunda ta fito itama take murmushi tana taho wa cikin tafiyar ta na yanga tamkar zata karye

Tana isowa suka sakarwa juna murmushi me bayyana haƙora, sannan ya buɗe mata motan ta shiga, shima zagaya wa yayi ya shige yaja ya nufi Gate

Shakira dake tsaye kamar an dasa ta ta saki baki tana kallon motar har ta fice

“Cab ɗijam.. Kar dai ace hasashe na ya zama gaske? Uhmm idan ko haka ne tabbas akwai matsala, babu yanda za ayi na bar Yayana yaso wannan me kama da mujiyan.. ina sam”.

Ƙwafa tayi tana nufan motan ta ta shige taja ta fice a gidan, ko a cikin motan tunanin yanda ta gansu yau ɗin ya tsaya mata arai, duk da ta san cewa babu wanda ya kai Ɗahira da Baffa shaƙuwa a gidan, amma kuma abinda take gani cikin idanun yayan ta yasa yau ta ɗaura zargi akan su.

         Har tazo ta wuce motan su Baffa a hanya tana kallon motan ta mirror tana jan tsaki, tana kitstsima abubuwa aranta da yawa.

      Su kuwa a cikin motan hira Baffa yake ta mata cike da tsananin ƙaunar ta, ji yake yi ba ya son ko kaɗan tafiyan da suke yi ya ƙare sabida shauƙin da yake ji, shiyasaka yake tafiya a hankali kamar bazai yi ba

Ɗahira kallon sa tayi tana dariyan labarin da yake bata tace, “Yaya don Allah ka bari haka kar cikina ya fashe”.

Dariya shima yayi yana kallon ta cike da so yace, “ai Ni nafi son in gan ki kina Farin ciki ne shiyasa nake baki labarin, don haka Ni bazan Dena ba, bari ma in baki wani”.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56Next page

Leave a Reply

Back to top button