FAMILY DOCTORS HAUSA NOVEL

FAMILY DOCTORS HAUSA NOVEL 1

“Ai kam yanzu ta tashi anan ta gama min daɗin baki”. K.b yafaɗa yana murmushi

“Hmm kai dai ka faɗa gaskiya ko dai kai ne ka gama mata daɗin bakin? Ai nasan hali”.

K.B said, ” Let me call her and u ask her,”

“A’a Ni bance ba, ka barta nariga dai nasan Shamsiyya baza tayi maka haka ba, ya Ɗan kinibibi ina fatan yana lafiya? Duk da nasan kai dashi baku da zumunci, wai ace anyi Waliman mu amma kuka ƙi zuwa”.

K.b dariya yayi yace, “sorry Madam wlh kin san Ni aiki ne yayi min yawa, idan ma wani zai ƙi zuwa ai Ni bazan ƙi ba tunda har da my dear, amma insha Allahu kwanan nan zan zo Garin ma”.

Taɓe baki Ɗahira tayi tana kallon Fadila da ta shiga Toilet tace, “Mu dai muna zuba idanu; and Kar ka manta da saƙo na don Allah idan zaka zo”.

“Ok insha Allah, ga fa Mutumin naki nan ya shigo in ba shi wayan ne sai ki faɗa masa sunan da kika kira sa dashi?”

Rufe baki Ɗahira tayi cikin waro idanu tace, “don Allah rufa min asiri kar ka haɗa ni dashi”.

K.b me zai yi in ba dariya ba

Ita kuwa Ɗahira wayan ta miƙa ma Fadila da ta dawo ta zauna kan gadon tana faɗin

“Riƙe wayan ki naga Yaya K.B yana son yaja min salalan tsiya”.

Fadila amsar wayan tayi tana maida wa a kunne, sai kuma tayi dariya tana faɗin, “ai har ta fice ma a ɗakin”.

Dariya ta sake yi tana gyara zaman ta, daga nan hiran su suka ci gaba da yi.

    Kabir K.B shi ne ɗa na uku wajen Hajiya IKRAM, ɗiyar ta na farko Sunan ta Nafisa, suna  kiran ta Aunty Mimi, tayi aure har da yara, sai Isma'il, suna ce masa Dady, sannan K.B ɗin, sai kuma Jalil sannan Shamsiyya, sai ƙannin Shamsiyyan guda uku

K.b ke son Fadila har kowa ya rigada ya san da zancen, yanzu kawai lokaci ake jira sanda Kaka zai ce su fito da mazajen aure ayi musu.
[5/25, 6:44 PM] Oummu Ɗahirah: ????????????????????????????????????????
FAMILY DOCTORS
????
????????????????????????????????????????

????????????????????????????
NAFEESAT RETURN
????????????????????????????

MALLAKAR:
NAFISAT ISMA’IL LAWAL

بسم الله الرحمن الرحيم


FEENAH WRITER’S ASSO????
®Ɗaya tamkar da Dubu????✓

JIKAR LAWALI CE✍️

Wattpad: UmmuDahirah????

     *\F.W.A????/*

SADAUKARWA
Na sadaukar ga Family na gaba ɗaya. GOMA’S FAMILY

Wannan shafin naku ne masoyana, kuji daɗin ku.❤️

    *EPISODE Fifteen*


  Fitan Ɗahira ɗakin sai ta wuce ɗakin Maman ta kai tsaye, babu ita ciki tana can General parlour

Kan gadon ta tanufa ta soma kwashe mata kayan wankin ta dake ajiye an ninke, kwashewa tayi ta kai mata sif ta dawo ta soma gyara ɗakin, ba wani datti yayi ba amma haka ta sake gyarawa har da wanke mata Toilet, ta dawo Kan kujera ta zauna ta soma duba wayan ta, message ɗin da Masoyin ta ya turo mata yanzu babu jimawa ta buɗe

“Kyakykyawa ta Barka da hantsi da fatan kina lafiya? Ya Weekend Ina fata kina enjoying?”

Murmushi ta saki, a karo na farko yau tayi tunanin tura masa amsa, sai ta soma typing cikin ƙware wa

_”Alhmadulillah ina fata kaima haka? Please I want to know who?”

Sai tayi sending ɗin shi, tana nan zaune tana jiran ko za’a dawo mata da amsa but babu, sai ta gyara kwanciyar ta tasoma chatting da friends ɗin ta waɗanda sukai school tare

Can kuma sai saƙo ya shigo, da sauri ta buɗe tana murmushi duk farin ciki ya cika ta

“Hmm kyakykyawa ta Kar ki damu da sannu zaki san ko Ni wane ne, Ni dai fata na in samu soyyayyar ki, don Allah ki so ni ko da kaɗan da yanda nake miki”.

Wani irin farin ciki ne yake mamaye da Ɗahira, sai dai bata mayar mishi da amsa ba tunda bata san me zata ce ɗin ba, sai taci gaba da chatting ɗin ta cike da nishaɗi.

          ⚫⚫⚫


   Buɗo ƙofan Hajiya tayi ta shiga parlour'n da sallama

Yusra dake kwance cikin 3 Sitter tana kallo ta’amsa mata

Zuwa tayi ta zauna tana faɗin, “Yusra, get me some water.”

Tashi Yusran tayi ta nufi Fridge tana faɗin, “Hajiya wai don Allah da gaske gobe Yaya zai dawo?”

Hajiya bata amsa mata ba har sanda ta kawo mata ruwan, ta’amsa tasha sannan ta’ajiye sauran kan Centre table tana maida hankalin ta kan t.v

Turo baki Yusra tayi ta zauna gefen ta tana cewa, “Hajiya I am talking to you.”

Sai Hajiya ta kalle ta tana hararan ta tace, “dan ƙaniyar ki Dadyn naki ƙarya zai miki? Ina ce a gaban ki ya faɗa?”

Sake bunso baki gaba tayi tace, “to Ni Hajiya gaskiya bazan zauna ba zan koma gidan Aunty Zainab da zama, don wlh bazan zauna anan kullum ina cikin takura ba”.

Hajiya tace, “to Ni ban aike ki ba, idan kin tambayi Dadyn ki ya yarda sai ki fi ruwa gudu ma”.

“Don Allah Hajiya kiyi masa magana mana wlh bazai yarda ba in Ni ce”.

Hajiya bata sake mata magana ba

Ita kuma sai magiya take mata har da ƴar ƙwallan ta

Ko kaɗan ba ta farin ciki da dawowar Yayan nata, tunda sai tafi kowa takura kasancewar Part ɗin su ɗaya, ko kaɗan idan yana nan ba ya ƙaunar kayi ƙwaƙƙwaran motsi a gidan, yanzu sai ya zama laifi a wajen sa

Daga ƙarshe ma Hajiya tashi tayi ta nufi cikin ɗakin ta tabar Yusra nan tana kumbura fuska kamar Flower, ba don ranta ya so ba itama ta tashi ta fice a part ɗin ma gaba ɗaya, duk zuciyarta babu daɗi.

⚫⚫⚫⚫⚫⚫⚫⚫⚫⚫

TOMORROW MORNING

  Monday tushen aiki ko Bature na tsoron Monday

Gaba ɗaya ahalin gidan sun tafi aikin su, sai su Umma da aka bari su uku a gidan sai kuma masu aiki, sannan Kaka dake Part ɗin sa

Hajiya itama tunda ta tashi ta soma soye-soyen ta wanda zata tarbi Babban ɗanta dashi, yau gaba ɗaya farin ciki ya cika ta Allah-Allah take yi anjima yayi ta ga dawowar sa, dama sun yi waya jirgin ƙarfe 02:00pm. Yace mata zai biyo; don haka komi take yin sa a tsanake, ita da kanta ta shiga ɗakin sa ta gyara masa tayi masa duk abin da ya dace, bayan ta saka airfreshna sannan ta ƙara masa da turaren tsinke ta rufo ɗakin ta koma kichen taci gaba da harkokin ta.

       ⚫⚫⚫


     Ɗahira tunda ta fara duba Patiens ɗin ta take jin kanta na sara mata, amma dayake ita ɗin jajirtacciya ce bata bi takai ba taci gaba da harkokin ta

Bayan ta gama ta nufi
Ward ta duba sauran mara su lafiyan ta sannan ta dawo Office ɗin ta

Tana son yau ta koma gida kamar lokacin tashin ta but ko kaɗan ba ta ƙaunar taje ta haɗu da maƙiyin ta (sunan da ta saka masa kenan)

Tunda Baffa ya shigo ɗazu ya sanar mata da lokacin da zai je ɗauko sa a airport take ta jin ta babu daɗi, sosai kan nata yake ƙara ciwon

Agogon dake ɗaure a tsintsiyan hannun ta takalla taga ƙarfe 01:20pm. Ne yanzu

Tsaki taja ta tashi ta nufi drower ta ciri magani tasha da ruwan Robber dake ajiye saman table ɗin ta, Labcoat ɗin ta tacire ta rataye akan Hanger sannan ta cire Eyeglasess ɗin ta ta’ajiye saman table ɗin ta nufi Toilet

Alwala ta ɗauro ta fito ta tada sallah, har ta’idar tana zaune nan tana lazimi, barci ne ya soma fisgarta don haka ta tashi ta ninke sallayan ta’ajiye ta nufi gaban table ɗin ta taɗau Glasses ɗin tamayar a idanun ta

Hanyan ƙofa ta nufa don zuwa Office ɗin Abbu ta kwanta acan, amma me ta tuna sai ta dawo tana jan tsaki

Ta san idan taje can zai tilasta mata ta koma gida ne, kuma a yau dai ba ta buƙatar ganin ta a gida, shiyasa ta dawo ta zauna kan kujeran ta ta ɗaura kanta a Deks ta rufe idanun ta, dayike barcin ne sosai yake cin ta don haka babu daɗewa ya ɗauke ta.

Koda ta farka babu ciwon kan a yanzu, sallan Asar tayi sannan ta saka Labcoat ɗin ta, tana shirin fita ne Beeper ɗin ta ya soma ruri, don haka ta fita da sauri tayi hanyan emargency ward.

          ⚫⚫⚫


    At home, everyone was celebrating Usman's return

Gaba ɗaya matan gidan suna part ɗin Hajiya sun je taya sa murnan dawowa

Sai da kowa ya watse sannan Shakira da Yusra da take Part ɗin su Shakiran yanzu suka nufi sashen Hajiyan don su gaishe sa

Yana zaune a dainning yana cin abincin da Hajiya ta girka masa da kanta

Yayi wanka har ya sauya shigan sa cikin ƙananan kaya kamar yanda ya saba

Koda suka shiga gaishe sa suka yi, ya’amsa musu cikin Izza da taƙama

Basu sake cewa komi ba suka miƙe suka fice don ba shi wuri, Part ɗin su Shakiran suka koma suka dasa hira.

       Shi kuma bayan ya gama ɗakin sa ya koma, kwanciya yayi kan Three sitter ya lumshe idanun sa, shi ba barci yake yi ba kawai kwanciyar yayi, sai da aka kira sallan la'asar kafin ya tashi yayi alwala ya fita

A waje suka haɗu da Baffa suka jera har masallacin dake nesa kaɗan da gidan su

Bayan sun dawo a haraban gidan suka haɗu da Abba da Abbu da dawowar su kenan daga aiki

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56Next page

Leave a Reply

Back to top button