FAMILY DOCTORS HAUSA NOVEL

FAMILY DOCTORS HAUSA NOVEL 1

A ran Ayush tsaki taja tana cewa, “aikin banza ta jiƙa shi tasha mana, Ni yanzu ba tashi nake ba, matsala ta na ga gwani na”. A fili kuwa sai tace, “ƙawata yanzu shi kuma Dr. Usman kin san wacce yake so ne?”

Kallon ta Shakira tayi, kamar tana tunani sai kuma tace, “taya zan sani? Ai sai nan da sati ɗaya idan Kaka ya buƙaci ganin mu”.

“Haka ne! To bari inje, yanzu ina da aiki da yawa”.

“Ok”.

    Da fitan Ayush ta shige Office ɗin ta, jikin ta na rawa ta soma sintiri a Office ɗin, ko kaɗan ta kasa yin tunanin da zai kai ta ga mafita, duk wata hanya da zata bi domin magana da Usman abun ya faskara, ta jima tana bibiyan sa a facebook amma har yanzu bata samu yayi mata reply ba, kusan kullum sai ta tura masa saƙon soyayya amma a banza

Tsaki ta ja tana zama akan kujeran ta, wayan ta ta sake ɗauka ta shiga facebook ta hau yin masa text, ga dai shi yana online amma bata samu reply ba. Ayush kamar tayi kuka ta ajiye wayan tana buga tagumi

Jin ƙaran shigowar text, tayi tunanin shi ne tayi saurin ɗaukan wayan, sai dai wata best friend ɗin ta ne tayi mata magana, dogon tsaki taja kafin ta yi mata reply, charting suka soma yi, anan take faɗa mata halin da take ci, kasancewar ita ƙawarta Safra ta tambaye ta “kwana biyu ina ta shige?” Shi ne ta soma bata labari aiki ne ya riƙe ta, har suka gangaro kan matsalan ta

Nan Safra tayi mata alƙawarin taimaka mata, ta yanda zata samu Usman a hannu, nan ta sanar mata nan da kwana biyu zata shigo Kadunan, kasancewar ita tana Zaria ne tana karatu

To a nan ne dai hankalin Ayush ya kwanta, duk da bata san Safra sosai ba, kasancewar a Facebook suka haɗu, amma ta yaba da wayewar ta, tasan zata iya taimakon ta, tunda tafi ta sanin kan duniyar.

⚫⚫⚫⚫⚫⚫⚫⚫⚫⚫

   Ƙarfe 01:30pm. Yau Ɗahira ta tashi daga aiki, tana komawa gida ta shiga ɗakin mahaifiyar ta

Aunty Amarya looked at her in surprise and said, “ah a yau kuma da wuri kika dawo?”

Murmushi Ɗahira tayi tace, “yes Mama”.

“Are you all right?”

Still Murmushi Ɗahiran tayi tace, “akwai baƙon da zan yi ne anjima Mama, shi ne na dawo tun yanzu”.

Aunty Amarya smiled and said, “Masha Allah! May Allah bring him peace”.

“Ameen Mama”. Ɗahira ta amsa mata, sannan ta fice tayi ɗakin su

Kwanciya tayi don ta huta, zuwa anjima sai ta tashi ta shirya.

Bata fi mintuna goma da kwanciyar ba, Fadil ya shigo ya sanar mata Aunty Amarya na kiran ta

Koda taje kiran, Aunty Amarya kallon ta tayi tace, “in ce dai kin shirya abinda zaki tarbi baƙon naki?”

“A’a Mama”.

“To haka ake yi ne? Ki je ki shirya masa wani abun, koda yake ki buɗe Fridge ɗina zaki ga markaɗaɗɗen kayan miya dana saka, anjima zan yi amfani dashi, sai ke kiyi amfani dashi ɗin kiyi masa miya zai fi”.

“To Mama”. Ɗahira ta amsa mata tana yin wajen Fridge ɗin

Da kallo Aunty Amarya tabi ta dashi har ta fice, sai ta saki murmushi kawai, a ranta tana ma ɗiyarta fatan dacewa da Miji na gari.

Ɗahira da fitar ta kichen ta nufa takai kayan miyan ta ajiye, sannan sai ta koma kan dainning taci abinci, tana gamawa ta koma kichen ta soma haɗa abincin baƙon ta, shinkafa da miya tayi masa, sannan ta haɗa Juice Kala biyu, sai tayi masa farfesun kifi, kasancewar shi suke dashi, dayake Abbu yafi son kifi shiyasa ba sa rabo dashi a koda yaushe, za su iya rasa Nama na kwanaki a gidan amma ban da kifi.



  Time ɗin da ta gama komi ƙarfe 02:40pm. Tayi, da sauri-sauri ta zuba a cikin coolars masu kyau, sannan ta wuce ɗaki tayi wanka, tana fitowa ta shirya cikin riga da skert na atamfa me ruwan silver, sai ratsin fari kaɗan-kaɗan, sai tayi make-up tayi ɗaurin ɗankwali me kyau da ya ƙara fito da kyawun ta

Zama tayi gefen gado tana kallon agogon ɗakin, har ƙarfe uku tayi ta wuce ma, wayan ta ta ɗauka tana kallo ko zata ga message ɗin sa, but babu, dole tayi zaman jiran sa.
[6/3, 8:41 AM] Oummu Ɗahirah: ????????????????????????????????????????
FAMILY DOCTOR’S
????
????????????????????????????????????????

????????????????????????????
NAFEESAT RETURN
????????????????????????????

MALLAKAR:
NAFISAT ISMA’IL LAWAL.

بسم الله الرحمن الرحيم


???????????????????????? ????????????????????????’???? ????????????????????*
®Ɗ???????????? ???????????????????????? ???????? ????????????????????✓

???????????????????? ???????????????????????? ????????✍️

????????????????????????????: ????????????????????????????????????????????????

     \????.????.????????/

????????????????????????????????????????
???????? ???????????????????????????????? ???????? ???????????????????????? ???????? ???????????????? ɗ????????????. ????????????????’???? ????????????????????????.

    *EPISODE Twenty Four*


     Har ƙarfe 04:30pm. Ɗahira tana zaune jiran masoyin ta, amma babu shi, kuma babu text ɗin sa, ta ɗauki wayan ta tana ajiye wa yafi sau a ƙirga, daga ƙarshe ta tura masa message, but babu reply, dole ta haƙura ta tashi tayi sallan Asar, sannan taci gaba da zaman jiran sa, ji kawai take yi tamkar ta ɓarke da kuka, amma haka ta daure, a ranta tana ba shi uzuri; Maybe wani abu ne ya hana sa zuwa

Har aka kira magriba Ɗahira na zaune bakin gadon ta, ta zuba tagumi tana ta tunani. Tashi tayi ta gabatar da sallan tukun ta koma ta zauna.

  Aunty Amarya aiko Fadil tayi yazo ya kira ta, koda taje sai Aunty Amarya ta tambaye ta "ko bazai zo bane?"

“I don’t know either. Mama, I still keep quiet, and at three o’clock we made it come.”

Ajiyan zuciya Aunty Amarya ta saki, tana kallon Ɗiyarta ta da damuwa ya nuna a fuskarta kafin tace, “to kiyi masa uzuri,
maybe there is something stopping him from coming, Allah yasa dai lafiya”.

“Ameen”. Ɗahira ta amsa tana ficewa

Ɗaki ta koma ta kwanta tana lumshe idanun ta, jin ƙarar shigowar text, da sauri ta tashi zaune tana ɗaukan wayan ta, nan da nan murmushi ya suɓuce mata ganin Masoyin ta ne, buɗe wa tayi jikin ta na rawa ta soma karanta wa

  _"Ban san da bakin da zan baki haƙuri ba Ɗahira, tabbas nasan zaki fahimce ni sabida ke me yiwa kowa uzuri ne, kuma na san kina da kirki da sanin Ya kamata. yau na so in bayyana a gaban ki, in nuna miki tsantsan ƙaunar da nake miki, sai dai kuma abu mafi girma ya shigo rayuwar mu, bazan ɓoye miki sirri na ba Ɗahira, na zaɓi faɗa miki ne kar ki ga laifi na, wanda na san zaki fahimce ni kiyi min uzuri. Mahaifiya ta ta haramta min zuwa gare ki, domin ta ce "idan har na aure ki bata yafe min ba," ta rigada ta zaɓa min matar da zan aura, don Allah! Kiyi haƙuri domin ba'a son Raina zan bar ki ba, sai don bin umarnin mahaifiya ta, amma ki sani ina matuƙar ƙaunar ki, har in koma ga mahalicci na bazan taɓa dena son ki ba."_

   _A.A.A. Masoyin ki._✍️



  Lumshe idanuwan ta tayi, hawayen dake tsiyaya akan kuncin ta tun soma karanta text ɗin; suka ci gaba da kwaranya, wani irin ƙunci ne ya tokare mata maƙogwaro, wanda daƙyar take iya haɗiye yawu

Dauriya dai me dauriya sai da ta gwada yin shi, amma ta gaza, dole ta zube kan gadon ta hau rusa kuka, kuka take yi sosai zuciyarta na mata zafi tamkar zai faso ƙirjin ta

Taya ma zata iya jure wannan halin da take ciki, meyasa zai mata haka? Meyasa zai tafi ya bar ta a lokacin da take buƙatar sa cikin rayuwan ta? Ya tafi ba tare da ta gansa ba, ya tafi ba tare da tasan sunan sa ba, dama ashe ba son ta yake yi ba? Meyasa to ya koya mata ƙaunar sa?…

  Fadila ce ta shigo ɗakin, ganin Ɗahira a wannan halin, sai tayi saurin ƙarisowa wajen ta hankalin ta a tashe, ta hau tambayan ta "lafiya?"

Cikin kuka Ɗahira ta bata amsa,
“He is gone ..! Wlh I really love him, ban taɓa son wani ba sai shi, meyasa zai tafi ya bar Ni?..” ta kasa ƙarisa wa illa kukan da taci gaba da yi, hawaye na ambaliya a kyakykyawar fuskar ta

Sosai Fadila ta tausaya mata, riƙo ta tayi tana faɗin, “ki nutsu Ɗahira, tell me what happened, shin wane ne shi wanda ya tafi ya bar ki?”

Ɗago idanun ta da suka kaɗa suka yi jazur tayi ta aza akan Fadila, cikin raunin murya take faɗin, “wanda muka yi alƙawarin aure dashi, ya ce min Mahaifiyar sa ta haramta masa aure na, me zai saka yayi min haka? Me zai sa in ba aure na zai yi ba ya zo ya koya min son sa? Meyasa tun farko ya zo wuri na?” Taƙarishe maganar cikin kuka

Da mamaki take kallon ta, sabida ta san babu wanda ke zuwa wajen ta, tunda take bata taɓa ganin Ɗahira ta kawo baƙonta gidan nan ba, “shin aina shi kuma wannan suke haɗuwa?” Tayi ma kanta tambayar, sai dai babu me bata amsa, dole ta kawar da zantukan daga ranta ta soma rarrashin ta. Ta daɗe tana rarrashin ta, amma Ɗahira ta kasa yin shiru, dole ta haƙura ta bar ta, ta miƙe tabar ɗakin.

   Kuka sosai Ɗahira tayi, kukan da ke fitowa daga zuciyar ta. Tunda take bata taɓa yin soyayya ba, koda da rana ɗaya bata taɓa son wani ba, amma kuma ta rigada ta kamu da ƙaunar wannan bawan Allan da bata san ko shi waye ba, bata san sunan sa ba, ko kaɗan baza ta iya juran rasa shi ba, soyayyan gaskiya take mishi, taya lokaci ɗaya zai tafi ya bar ta a lokacin da take matuƙar buƙatar sa? Wannan amsoshin su suke yawo a zuciyar ta, wanda ya ƙara haddasa mata cinkushewar baƙin ciki a ranta

Allah ya gani ita baƙuwa ce a soyyayya, ko kaɗan baza ta iya juran wannan yanayin ba.

  Har Fadila ta sake dawowa ɗakin Ɗahira na kwance tana kuka

“Wai don Allah Ɗahira baza ki dena wannan kukan da kike yi ba? Taya kuka zai miki maganin matsalan ki? Ke fa ba ƙaramar yarinya ba ce”. Cewar Fadilan tana kallon ta daga bakin gadon ta da ta tsaya

Ɗahira bata ce komi ba, illa miƙe wa da tayi ta shiga Toilet, alwala tayi ta fito ta soma gabatar da sallan isha’i da aka daɗe da yi, har ta idar tana zaune a wajen ta kasa tashi, sai ma haɗa kanta da gwiwowin ta da tayi; tayi shiru tana tsiyayar da hawaye

Fadila dake kwance tana faman latsa waya, ta kalle ta tace, “I forgot I didn’t tell you, Aunty Amarya is calling you”.

Shiru Ɗahira tayi mata

Ita kuma bata sake bi ta kanta ba, taci gaba da charting ɗin ta ita da K.B, tana yi tana sakin murmushi.

  Sai da kusan mintuna goma suka shuɗe sannan Ɗahira ta tashi ta fice, babu kowa a Parlour, kai tsaye ta wuce ɗakin Maman ta. Sai da tayi sallama aka ba ta iznin shiga sannan ta shige

Aunty Amarya na zaune akan sallaya, shi kuma Abbu na gefen gado zaune yana waya, da alamun wayan me muhimmanci ne shiyasa gaba ɗaya attention ɗin sa ya ba wa wanda suke wayan ne

Durƙusa wa gaban Aunty Amarya tayi, cikin dashashshiyar muryan ta na wanda tasha kuka tace mata “ga ta”.

“Ya naga kamar kin yi kuka? What’s wrong with you?” Aunty Amarya asked her this question keeping an eyes on her

Sake sunkuyar da kanta ƙasa tayi, in a weak voice and said, “nothing”.

Shiru Aunty Amarya tayi na ɗan wani lokaci, sai kuma tace, “je ki kici abinci, kar ki kwanta da yunwa kin ji ko?”

Gyaɗa mata kai tayi tana miƙe wa ta fice

Aunty Amarya tabi ta da kallo cike da tausayin ɗiyar ta ta, tabbas ta san akwai ɗinbim damuwa a tattare da ita, kuma ta gane kuka tayi, amma kuma ba ta son ta dame ta da tambaya a wannan lokacin ne har sai ta samu sauƙin damuwar nata..

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56Next page

Leave a Reply

Back to top button