FAMILY DOCTORS HAUSA NOVEL 1

Gaishe su yayi cikin girmamawa, su kuma sai tambayan shi hanya suke yi cike da fara’a, haka ya’amsa musu sannan ya wuce ya nufi babban Parlour
Fadil na zaune a kan kujera yana kallo shi kaɗai ya shigo
Da sauri Fadil ɗin ya gaishe shi
Da kai ya’amsa masa ya nufi hanyan da zai sada shi da ɗakin Kaka
Da idanu Fadil ya bi shi dashi, sai da ya shige sannan ya taɓe baki a ransa yana mitan “miskilin banza! kai da Fadila wlh ban san wanda yafi mugun hali ba”.
Sai kuma ya kwaɓe fuska yaci gaba da kallon sa.
Tura ƙofan yayi ya shiga yana motsa bakin sa
Kaka dake zaune kan Wheel chair ɗin sa kamar ko yaushe yana karatun Jarida ya ɗago yana kallon sa, sai kuma ya yalwata fuskar sa da fara’a yace, “Maraba da Jikalle na”.
Takowa yayi ya zauna saman kujeran ɗakin yana kallon Kaka, kaɗan ya saki fuskar sa yace,
“Old man are you still alive?”
Sai Kaka ya saki dariya me sauti yace, “ja’iri ka ƙosa na mutu ko? To ina nan babu inda zan je sai na ga auren ka”.
Kyakykyawar murmushin sa yayi yana shafa gashin kansa yace, “uhmm Kaka kace da sauran ka kenan tunda Ni dai ba yanzu ba”.
“Koma dai me zaka ce sai naga auren ka tukun zan bar duniyar nan, dama tunda nayi muku maganar kai da takwara babu wanda ya haɓɓa sa, kun fi so dai a haɗa da ƙannin ku ko?”.
Usman taɓe baki yayi sai dai be ce komi ba
Kakan changed the conversation and asked, “Ya hanya?” Shi kuma ya’amsa masa a taƙaice
Kaka sai zuba masa hira yake yi, shi kuma daga ya’amsa da Eh sai A’a, daga ƙarshe wayan sa ya ciro yana latsawa yana sauraron Kakan, a haka yaja dogon lokaci a ɗakin kafin ya miƙe yayi masa sallama ya fice.
[5/26, 9:37 AM] Oummu Ɗahirah: ????????????????????????????????????????
FAMILY DOCTORS
????
????????????????????????????????????????
????????????????????????????
NAFEESAT RETURN
????????????????????????????
MALLAKAR:
NAFISAT ISMA’IL LAWAL
بسم الله الرحمن الرحيم
⚖
FEENAH WRITER’S ASSO????
”’®Ɗaya tamkar da Dubu????✓”’
JIKAR LAWALI CE✍️
Wattpad: UmmuDahirah????
*\F.W.A????/*
SADAUKARWA
Na sadaukar ga Family na gaba ɗaya. GOMA’S FAMILY
*EPISODE Sixteen*
Sai ƙarfe 05:45pm. Ɗahira ta koma Office ɗin ta, Jakarta ta ɗauka da abinda zata buƙata ta fito ta rufe Office ɗin ta nufi Lifter
Tana sauka ta fita ta nufi inda motan ta yake ta buɗe ta shiga, rufewa tayi ta’ajiye jakar ta kan Kujeran me zaman banza sannan tayi ma motan keey, sai dai yaƙi tashi, ta daɗe tana gwadawa amma yaƙi ya tashi, guntun tsaki taja tana dafe goshin ta, lumshe idanuwan ta tayi na kusan minti 2 kafin ta buɗe ta sake gwadawa amma ina har yanzu be tashi ba, fitowa tayi tana ɗan waige-waige, sai kuma ta nufi gaban motan ta buɗe Garage ɗin ta soma tattaɓa wa, duk ta duba ko da akwai matsala ne amma ita a fahimtan ta bata ga komi ba
Tana nan tsaye a wajen tana ɗan sake duba wa taji sallama, sai ta ɗago kyawawan idanuwan ta wanda ƙwayan ciki suke ƙyalli sakamakon Hasken fitillun haraban wajen, amsa mishi tayi tana kau da kanta ganin kallon da yake mata tamkar zai haɗiye ta
“Are you all right? I’ve seen you here before. Are you still gone? What’s going on?”
Ɗahira kamar baza tayi magana ba, sai kuma ta ga hakan be dace ba tunda taimakon ta zai yi, bata ɗago ba ta bashi amsa, “Wlh nima ban sani ba, kawai ta ƙi tashi ne”.
Dr. Sa’id yace, “ok bari in duba miki mu gani ko?”
Babu musu ta matsa mishi yazo ya soma duba mata, shima ya daɗe yana taɓe-taɓen sa kafin yace mata, “wake up the car”.
Shiga tayi tayi ma motar keey amma har yanzu ya ƙi tashi
“Ina ga dai motar ki sai ta ga bakanike coz myb wani matsalan ne babba wanda baza mu iya gane wa ba”. Yayi maganar bayan ya rufe mata garejin
“To Nagode”. Tace dashi tana ciro jakarta kafin ta rufe motan da keey
“In ba damuwa muje in rage miki hanya mana”.
Ta tsinkayi muryan sa da har ta juya baya zata tafi
Jimmm tayi tana tunani domin ita mutumin ko kaɗan be mata ba, coz ta kula kallon tsiya ne dashi tun ganin sa na farko
Murmushi yayi yana takowa wajen ta yace, “don’t worry. Ni ba siyar da kanki zanyi ba, ai kin san a nan nake aiki balle kice Ni ɗin baƙo ne, so ni ba baƙo bane babu wanda be San ni ba, My name is Dr. Sa’id Khan”.
Kallon sa ta ɗan yi sai kuma tayi guntun murmushi tace, “ba damuwa mu je”.
“Yauwa ko ke fa”. Yafaɗa yana yin gaba wajen motar sa
Shi ya buɗe mata murfin motan da zumman ta shiga
Sai kawai ta ga abun yayi mata wani iri domin ita idan har ba Baffa ba basu taɓa hakan da wani ba, hakan ko kaɗan be burge ta ba, amma babu yanda zata yi ta shige ta zauna ya rufe mata
Shiga shima yayi yaja motar suka bar asibitin
A cikin motan ma babu wanda yayi magana cikin su, sai da suka ɗan yi tafiya kafin ya soma jan ta da Surutu duk a kan aikin nasu
Ko kaɗan ba ta jindaɗin surutun nasa
Shi kansa ya gane ba ta ƙaunar hiran sa; yanda take amsa masa maganar kamar baza tayi ba, don haka yaja bakin sa yayi shiru yana mamakin yarinyan, shi tunda ya ganta yaji ta burge sa matuƙa kuma yana son ƙulla alaƙa da ita, sai dai ya ga alamun hakan ba me yiwuwa bane duba da yanda take ɗin, da alamun tana da girman kai kuma zata yi wuyan sha’ani, a yanda ya fahimce ta kenan
Har suka kai ƙofar gidan su kafin ya tsai da motan
Kallon sa Ɗahira tayi cikin siririyan muryanta me kamar tana yanga tace,”Thank you, Dr.”
He smiled and looked at her and said, “It’s all right.”
Buɗe motan tayi ta fito
Dai-dai lokacin su Baffa da Usman suka ƙariso wajen sun dawo sallan magriba
Gaba ɗaya kallon ta suke yi, yayinda Usman ya ɗauke kansa time ɗin da ta juyo zata sauke idanun ta a kansu, cikin gidan ya wuce batare da yayi wa Baffa magana ba
Shi kuma Baffan sai ya nufo ta fuskarsa duk babu walwala yana bin motan Dr. Sa’id da kallo da har ya ja ya tafi
Itama ganin ya taho ɗin ne yasa ta tsaya tana masa murmushi
Yana ƙari so wa idanun sa a kanta yace, “wannan kuma wane ne? ina Motar taki?”
Sai da ta kalli hanyar da Dr. Sa’id yabi kafin ta dawo da ganin ta kanshi tace, “Yaya Motata taƙi tashi ne wlh ban san kuma me ya faru ba, shi ne yace in zo ya rage min hanya”.
Gaba ɗaya zuciyar Baffa ba ta mishi daɗi, tsananin kishi ne yake nuƙurƙusan sa a ransa, daƙyar ya”iya saisaita kansa ya sake jeho mata tambaya
“Aina Motar taki ta tsaya da har kuka haɗu dashi?”.
“A cikin Hospital ɗin ne fa, kuma shima Dr. Ne cikin asibitin shiyasa ma na yarda na hau, but da farko ban yi ninyan hawa ba”.
Murmushi Baffa ya kirƙiro yace, “let’s go then”.
Babu musu tayi gaba yana bin ta a baya duk da ita bata fahimci musabbabin tambayan nasa ba, amma ta san cewa shi ɗin Yayanta ne yana da right ɗin tambayar ta
Sai da suka shiga ciki kafin suka jera cikin gidan, Part ɗin su Ɗahira suka wuce
Suna shiga da sallama, Aunty Amarya dake zaune ita da Fadil suka amsa musu
“Aaah maraba da Mijina”. Aunty Amarya tafaɗa tana yalwata fuskarta da fara’a
Baffa na faman shafa kansa yana murmushi ya ƙariso ya zauna a kan kujeran kafin ya gaishe ta
Ta’amsa masa cike da fara’a tana tambayar sa aiki
Itama Ɗahira sannu da gida tayi mata ta wuce ɗakin su ba tare da ta zauna ba
Su kuma suka ci gaba da hira suna kallo
Daga baya itama Umma ta fito aka ci gaba da hiran da ita
Baffa duk ya ƙosa Ɗahira ta fito amma tunda ta shiga bata sake fitowa ba, shi kuma ya zauna ne don ita amma tunda ta fito ta zuba abinci ta sake shige wa ɗaki, aiki take yi a ciki shiyasaka ta zauna nan ɗin tunda ba ta son hayaniya
Sai da aka kira sallan isha’i kafin Baffa ya miƙe tare da Fadil suka fito
Anan suka ci karo da Fadila itama dawowar ta kenan, gaishe da Baffa tayi