FAMILY DOCTORS HAUSA NOVEL 1

Ya’amsa yana faɗin, “Sarkin miskilanci sai yanzu aka dawo?”
Murmushi tayi tace, “Yaya kana son dai tsokana ta ko?”
Murmusawa yayi shima yana cewa, “ai gaskiya ne, kwana biyu ma gaba ɗaya kamar ba kya nan a gidan, rabon da in ganki na jima sai jiya a wajen meeting”.
Fadil dake tsaye yana sauraron su yace, “ai Yaya wlh duk wanda ya auri Aunty Fadila ya bani, shiyasa ma zan ba ma Yaya K.B shawara tun wuri ya sauya ta don baza tayi daɗin zama ba idan ya aure ta, yana ji yana gani zata mayar da waya abokin rayuwanta ta ƙyale shi yay ta surutun sa..”
Kawo masa duka tayi dole yayi shiru yana matsawa gefe da sauri
“Wlh zan ɓalla ka a nan wajen; Ni sa’ar wasan ka ne Fadil?” Tafaɗa tana hararan sa cike da haushi
Baffa dariya yayi yace, “mai da wuƙan don Allah wasa yake miki”.
Ƙwafa kawai tayi ta juya ta buɗe ƙofan Part ɗin nasu ta shige, tana jin Baffa yana faɗin
“Babu sallama kuma zaki tafi?”
Amma bata jiyo ta kalle sa ba bare ta tanka masa
Su ma wuce wa suka yi suka tafi, Baffa na shan dariyan Fadil da yaci gaba da maganar Fadilan.
⚫⚫⚫
*08:45pm.*
Suna zaune su huɗu a kan dainning suna cin abinci, babu me magana cikin su sai ƙaran cokula da Plate da ake ji
Kansa na ƙasa yana cakalan abincin kamar bazai ci ba, rabi kuma hankalin sa naga wayan sa yana kallon wani abu da aka tura masa, har kowa ya miƙe suka bar sa nan zaune be ma san sun tashi ɗin ba
Parlour suka koma sukai zaman su, Big Dady da Hajiya suna taɓa hira while Yusra kuma ta mayar da hankalin ta kacokan kan Film ɗin da ake yi a Bollywood, Film ɗin زوجة زوجي searese
A hankali ya miƙe ya taho cikin parlour’n yana shirin wuce wa ɗakin sa
Dady ya tsayar dashi yana faɗin, “Fodio come here we’ll talk”.
Juyowa yayi ba tare da yace komi ba ya taho ya zauna kan One sitter dake Facing ɗin nasu Dady
Ɗan gyaran murya yayi yana kallon sa kafin yace, “gobe ne zaka soma zuwa Hospital ɗin ko ya?”
Cikin ƙasa da murya kamar wanda yake tsoron yin maganan yace “No .. until Monday”.
Jinjina kai Dady yayi kafin yace, “to har yanzu baka shirya aure bane? Tunda ga shi yanzu ka dawo gida Ya kamata ace kun ajiye mata kai da Baffa amma shiru har yanzu baka ce komi ba, kuma idan ban manta ba naji Baba yayi muku magana akan maganar auren ku”.
Shiru Usman yayi be ce komi ba, sai ma sad da kansa ƙasa da yayi
Su kuma sun zubo masa ido daga shi har Hajiya suna sauraron abinda zai ce
Yusra dake kallo ma hankalin ta na wajen
Girgiza kansa Dady yayi don yasan halin ɗan nasa, don babu wanda be saba da miskilancin sa ba
“Ya kamata dai kusan kun girma tun kafin mu ce zamu nuna fushin mu a kan ku ku fito da mata, don baza mu zira muku idanu kuyi yanda kuke so ba, ka tashi kaje Allah yayi muku albarka”. Dady ya sake faɗan hakan
Miƙewa yayi yana ɗan motsa bakin sa kafin ya nufi hanyan ɗakin sa
Su kuma suka rakasa da kallo har sanda ya gifta ta gaban su ya wuce
Ajiyan zuciya Dady ya saki yana miƙewa ya kalli Hajiya yace, “Let me in. I have a job.”
Be jira amsar ta ba ya sake maida kallon sa kan Yusra yana cewa, “Auta ke baza ki je ki kwanta ba sai kin makara ko?”
Kallon sa tayi tana murmushi tace, “Dady zan kwanta yanzu za’a gama wannan sai inje in kwanta”.
Gyaɗa kansa yayi kafin yayi gaba yana shigewa ɗaki
Itama Hajiyan bin bayan sa tayi suka bar Yusra ita kaɗai a parlour’n.
[5/27, 8:43 AM] Oummu Ɗahirah: ????????????????????????????????????????
FAMILY DOCTORS
????
????????????????????????????????????????
????????????????????????????
NAFEESAT RETURN
????????????????????????????
MALLAKAR:
NAFISAT ISMA’IL LAWAL
بسم الله الرحمن الرحيم
⚖
FEENAH WRITER’S ASSO????
”’®Ɗaya tamkar da Dubu????✓”’
JIKAR LAWALI CE✍️
Wattpad: UmmuDahirah????
*\F.W.A????/*
SADAUKARWA
Na sadaukar ga Family na gaba ɗaya. GOMA’S FAMILY
*EPISODE Seventeen*
*MONDAY*
*12:30pm.*
Ya gama shirin sa na zuwa Office, yana sanye cikin wandon jeans blue, sai baƙar riga me gajeren hannu da ya sake fito da hasken skin ɗin sa sosai ya kuma ƙara masa kyau ainun, kwantaccen baƙin gashin sa sai shaining yake yi zuwa siririn sajen sa, babu abinda yake tashi ajikin sa sai sassanyan ƙamshi me tsananin daɗi ga duk wanda ya shiga hancin sa
Wrest watch yake ɗaura wa a tsintsiyan hannun sa me haske sosai da yalwan gashi, fuskarsa babu alamun fara’a ko kaɗan, har ya gama sakawa kafin ya zauna gefen gado ya soma saka Combat ɗin sa da ya kasance Blue Colour da igiyan sa suka kasance baƙi, bayan ya gama saka wa sai ya miƙe ya ɗau briafcase ɗin sa ya fito cikin ɗakin yana rufe wa
Babu kowa cikin parlour’n, sai ya nufi ɗakin Hajiya yayi Nocking yana jiran izni
Hajiya dake zaune kan gado wanda fitowar ta kenan daga Toilet ta ba da iznin shigo wa
Tura ƙofan yayi yana motsa bakin sa idanun sa a kan ta
Kamar yanda itama ta zuba masa idanu tana kallon sa
Takowa yayi a hankali har zuwa gaban ta kafin ya zauna gefen gadon, shiru yayi yana murza hannun jakan dake riƙe cikin fararen tafin hannun sa
Tsawon mintuna biyu Hajiya tana jiran taji yayi magana amma sai taga be da alaman yi, hakan yasa tace, “har ka shirya my son?”
Gyaɗa mata kai yayi yana kallon ta
She smiled and said, “God bless you and good luck.”
“Ameen”. Yafaɗa a hankali wanda a laɓɓan sa ta fahimci abinda yace
Miƙe wa yayi ya taka ya fice cikin ɗakin yana duba agogon hannun sa.
Yana fita wajen motan sa ya buɗe ya shiga ya zauna sannan ya rufe, tada motan yayi yaja ya nufi bakin Gate
Tun daga nesa da me gadi ya hango zuwan sa ya miƙe da sauri ya buɗe masa Gate ɗin, yana fita ya ƙara Speed, cikin mintuna ƙalilan ya’isa haraban Hospital ɗin
Ɓude ƙofan yayi ya ziro ƙafafun sa a hankali sannan ya fito ya rufe, ya juya ya soma tafiya cikin taƙama da izza wanda zaka san a jinin sa ne.
Shakira da Ayush dake tsaye jikin motan Shakiran, Ayush tana faɗa mata yanda suka yi da Baffa sai idanun ta ya faɗa kan Usman dake doso cikin asibitin, baki buɗe take bin shi da kallo
Hakan yasa itama Shakira ta mayar da hankalin ta inda Ayush ɗin take kallo, nan ta hangi Usman har ya shige
Ajiyan zuciyan da Ayush ta saki me ƙarfi ya saka Shakira take kallon ta cike da mamakin ta
“Lafiyan ki kuwa?” Ta tsinkayi muryan Shakiran da ta sake dawo da ita hayyacin ta
“Hmm ba lafiya ba, wane ne wannan Handsome Guy ɗin da naga kamar yana kama da Familyn ku?” Ayush tayi maganar tana tsare Shakira da idanu
Taɓe baki ita kuma tayi tace, “Yaya Usman ne”.
“Kaiii amma wlh ya haɗu, Ni zan iya ce miki ban taɓa ganin mutumin da ya tafi da imani na a second ɗaya ba irin wannan, kai wlh ban taɓa ganin wanda komi nashi ya dace dashi ba sai wannan guy ɗin, Kai Amma wlh ban taɓa..”
“Ke dallah ya isa mana, meye haka kike zuba min hauka? ko dai hankalin ki ya gushe ne?” Shakira ta katse ta tana kallon ta cike da takaici
“Wlh baza ki gane bane, amma wlh yayi Ni dai ya gama dani”.
Shakira tace, “to shikenan yanzu kenan baki yi da Yaya na sai wannan ko? Ko kin manta alƙawarin da ki kai min?”.
Murmushin yaƙe Ayush ta saki tace, “laa I don’t mean that. I’m just saying my opinion on this, but I’m not saying I’m better than Baffa, I like Baff..” Sai kuma tayi shiru ganin zata saki layi
Shakira da hankalin ta ma ba ya ga Ayush ɗin, tana kallon Fadila da tazo wuce su tayi saurin kwaɗa mata kira
Fadila dake tafiya waya a kunnen ta tajuya ta kallo su, sai kuma ta soma takowa wajen su har a lokacin tana ci gaba da wayan ta, sai da tazo dai-dai gun su sannan ta kashe wayan tana ɗago kai ta kalle su
Shakira murmushi tayi tace, “manyan gari wai ke idan ba an neme ki bane ba kya neman mu ko?”
Guntun murmushi kawai Fadila ta saki ba tare da tace komi ba illa gyara zaman jakan ta da take yi
“Yanzu muka gama magana da mutumiyar ki a kan ki ma”. Shakira ta sake faɗan hakan still tana Murmushi
Kallon ta Fadila tayi da rashin fahimta kafin tace, “who?”
Shakira tace, “Ɗahira, ai ita nake nufi, kullum kuma idan na ganta sai na ce ta gaishe min da ke, Allah yasa tana faɗa miki don nasan halin ta ba wai son ki take yi ba?”
Numfashi Fadila taja sannan tayi murmushi tace, “haka ne.. to Ni zan tafi kin ga nayi late yau ban shigo da wuri ba”. Sai kuma ta ɗan ɗago wayan ta tana duba time kafin ta juya ta tafi ba tare da ta sake furta komi ba