FAMILY DOCTORS HAUSA NOVEL

FAMILY DOCTORS HAUSA NOVEL 1

     ⚫⚫⚫⚫⚫


   Baffa dake tsaye kan benen Part ɗin su, yana tura mata text ɗin ya saki murmushi me fid da haƙora, ya sani dole ne wannan ranan zata zo, amma yanzu ya rigada ya gama shirya mata, ya shirya yanda zai fito fili ya bayyana ƙaunar sa ga masoyiyar sa, domin samun mallakan ta a matsayin matar sa, wanda ya daɗe yana tsimayen zuwan ranan

Wani kyakykyawar murmushi ya sake saki cike da farin ciki a ransa, shafa suman kansa yayi kafin ya soma taka wa ya wuce Part ɗin su, shiga yayi da sallama a bakin sa

Hajja Fatu dake zaune tana jiran dama shigowar sa ne, shiyasa ta zauna a parlour’n zaman jiran sa. Amsa mishi sallaman tayi tana murmusawa tace, “yauwa Baffa na, taho ka bani labarin surukar ta wa”.

Dariya ya saki yana isowa wajen ya zauna tare da faɗin, “kai Hajja wai dama jira na kike yi?”

“Iyi wlh, ai tunda kafaɗa na kasa zaune na kasa tsaye ina so inji wacce me sa’ar ce ta same ka?”

“Uhmmm Hajja kenan! Ko dai Ni ne me Sa’ar dana same ta, ke kanki Hajja sai kin yaba da zaɓi na, because you will never have a Daughter-in-law like her, I know you will be very happy if you know who she is”.

Cike da farin ciki Hajja tace, “yauwa ɗan albarka, wlh idan ka samo wacce tayi dai-dai da ra’ayina, you must finish everything for me, domin da ita ne zan riƙa ɗagawa a gidan nan, sannan zan fi kowa fariya”.

Baffa dai murmushi kaɗai yake zuba wa, yana kallon Mahaifiyar ta shi

“Ina jin ka yarinyan ƴar gidan wane ne?”

“Hajja ba wata bace sai Ɗahira wacce kika sani na gidan nan”.

To fa nan ake yin ta. Ya kuke ganin za’a kaya?

Hajja zata amince da zaɓin Baffa?

ko kuwa Ɗahira zata amince da Baffa a matsayin Mijin ta?

me zai faru?

ta Comments ɗin ku kaɗai zan tabbatar da cewa kuna so in ci gaba, idan kuma ba kwa so falillahil hamdu, dama hutu nake son tafiya, sai mun haɗu a next week.
[6/2, 12:50 PM] Oummu Ɗahirah: ????????????????????????????????????????
FAMILY DOCTOR’S
????
????????????????????????????????????????

????????????????????????????
NAFEESAT RETURN
????????????????????????????

MALLAKAR:
NAFISAT ISMA’IL LAWAL.

بسم الله الرحمن الرحيم


???????????????????????? ????????????????????????’???? ????????????????????*
®Ɗ???????????? ???????????????????????? ???????? ????????????????????✓

???????????????????? ???????????????????????? ????????✍️

????????????????????????????: ????????????????????????????????????????????????

     \????.????.????????/

????????????????????????????????????????
???????? ???????????????????????????????? ???????? ???????????????????????? ???????? ???????????????? ɗ????????????. ????????????????’???? ????????????????????????.

    *EPISODE Twenty Three*


     Zumbur Hajja ta miƙe sabida jin bazatan maganar ɗan nata, cikin tsantsan takaici tace, "kana kuwa cikin hayyacin ka Al'ameen? Ɗahira?.. Ɗahiran ce kake nufin zata zamo suruka ta?"

Shima Baffa miƙe wa yayi a wani irin yanayi, domin dai tabbas ya san akwai matsala tunda yaji Mahaifiyar sa ta kira sa da sunan sa na ainihi, cike da alhini yace, “Hajja to mene ne laifi idan na so Ɗahira? Na ga ai ita ƙanwa ta ce ko?..”

Be rufe baki ba Hajja tace, “kai da Allah ja can mara hankali mara tunani, wanda be san inda yake masa ciwo ba, ka rasa wacce zaka so sai Ɗahira? To ban amince ba, idan har Ni na haife ka, to, babu ta yanda za’a yi ka auri wannan yarinyan”.

Sosai hankalin Baffa ya tashi da jin zantukan mahaifiyar na sa, cikin matuƙar damuwa yace da ita, “Hajja wai me Ɗahiran tayi miki ne da kike son jifan ta da baƙin fenti? Mene ne aibun ta shi nake son sani?”

A fusace take kallon sa tace, “aibun ta kake son sani ko? To na tsane ta ne ba na ƙaunar ta, ba na son ta zamo suruka ta, idan ko ka bari hakan ta faru, na rantse da Allah sai na tsine maka albarka”.

“Innalillahi wa’inna ilaihi raji’un! innalillahi wa’inna ilaihi raji’un!!”. Abinda kawai Baffa yake faɗa kenan yana bin ta da kallo

Ita kuwa zama tayi tana huci kamar zakanya, sai kuma ta sake kallon sa tace, “umarni nake ba ka, idan har ka bari wani ma yasan da zancen kana son ta a gidan nan, to har abada bani ba kai, tun wuri kaje ka nemo wata ka aura, ko kuma Ni in zaɓa maka zaɓi na”.

Baffa shiru yayi har yanzu idanun sa a kanta, sai dai a wannan lokacin komi ya tsaya masa cak daga duniyar tasa, be san sanda hawaye suka soma sintiri a fuskar sa ba, sai jin ɗumin su yayi saman kuncin sa.

  A dai-dai lokacin ne Shakira ta shigo part ɗin, kallon Yayan nata tayi dake hawaye, kafin ta mayar da idanun ta kan Hajja dake faman karkaɗa ƙafafu fuskarta a matuƙar ɗaure, nan da nan hankalin ta ya tashi ta ƙariso da sauri tana tambayan "me ke faruwa?"

Lumshe ido kawai Baffa yayi, sai ya buɗe ya ja ƙafafuwan sa ya nufi hanyar ɗakin sa, yana shiga ya faɗa kan gadon sa ya soma tsiyayar da hawaye, sosai yake kukan zuci, zuciyar sa na tafarfasa, babu abinda ke dawo masa a kwanya sai maganganun Hajja, “shin taya ma hakan zai faru? Taya zai iya cire ƙaunar Ɗahira da ya jima yana dakon sa? Ina sam bazai yiwu ba, idan kuwa hakan ta faru, ya tabbata mutuwa zai yi”.

     **** **** *****


   Hajja duk abinda ke faruwa ta sanar wa Shakira

“Ai dama na sani, ba tun yau ba dole ne akwai soyayya a tsakanin su, I already understand Hajja.”

Hajja said, “Then why didn’t you tell me in the first place, sai da abu yayi nisa? Yanzu da ace ban tambaye sa ba haka zai je ya faɗa ma mutanen gida ga wacce yake so, kinga kuwa babu ta yanda za’a yi in hana faruwan hakan, na tabbata wlh sai anyi auren nan, tunda dama iyayen ku babu abinda suke ƙauna sama da su ga anyi haɗin zumunci a gidan nan, ina sam wlh ba dai da ɗana ba, dama Yusra ko Fadila yace yana so sai in bar sa, amma ya rasa wacce zai jajibo min sai ƴar A’ishah, maƙiyiya ta” .

Shakira tace, “Nima kai na Hajja na so raba su tun farko, ina wannan ƙawar tawa da muka taɓa zuwa da ita gidan nan Ayush?”

Hajja gyaɗa kanta tayi tace,”yes I understand her, wacce kuke sintiri a asibiti tare lokacin ciwon Kaka”.

“Eh ita, wlh she really loves Baffa Hajja, kawai ki haɗa sa da ita tunda shima Yayan ya saba da ita”.

Ɓata fuska Hajja tayi tace, “sam ɗana bazai auri ƴar talakawa ba, da ace dai suna da hali ne, amma tunda basu dashi ban amince da ita ba, Ni yanzu na tsara wacce zai aura, idan be samo wata ba, zan haɗa sa da Sa’adatu ne, yanzu ma ɗauko min wayata in Kira Mahaifiyar ta muyi magana, gwara ta dawo nan ko ya ganta ya so ta”.

Tashi Shakira tayi don ɗauko mata wayan, duk da a ranta bata ji daɗin haɗin ba, amma ko ba komi Yayan ta bazai auri Ɗahira ba.

Sa'adatu yarinya ce wajen ƙanwar Hajja Fatu, Hajiya Amina wacce tayi aure a Legos. Dama tun farko Sa'adatu ta jima tana ƙaunar Baffa, sai dai shi ya ƙi amince wa da ita sabida bata yi masa ba, wayewar ta yayi yawa, akwai ta da rawan kai.

⚫⚫⚫⚫⚫⚫⚫⚫⚫⚫

     *WASHE GARI*

  A ranan Ɗahira ta tashi ne cikin walwala da farin ciki, burin ta kawai anjima yayi ta sanya masoyin nata a idanu, koda ta gama shiryawa cikin Abaya baƙa me kwalliyan stones, sai ta yafa gyalen shi ta saka flet shoes, sallama tayi wa Aunty Amarya ta fito ta shiga cikin motan ta

Koda ta isa asibiti Direct office ɗin Baffa ta wuce, sai dai babu shi, domin Office ɗin ma a rufe yake, tayi mamaki sosai amma bata tsawwala ba, sai ta wuce Office ɗin ta.

       ⚫⚫⚫


   Ɗan adai-daita sahu ne ya sauke Ayush a bakin Hospital ɗin, kuɗin sa ta biya sa sannan ta shigo cikin asibitin

A dai-dai lokacin ne Shakira ta shigo itama da motan ta, parking tayi ta fito tana gyara zaman mayafin ta

Hango ta da Ayush tayi ne yasa ta nufo ta tana washe baki, tana ƙarisowa suka soma gaisawa kafin suka jero suka nufi cikin asibitin, Office ɗin Shakira suka wuce kai tsaye.

  Sai da suka zauna kafin Shakira tace, "I called your phone yesterday but it turned off. What happened to her?"

“Wlh kuwa babu caji ne, kuma ban samu na kai an saka min ba sai daga baya, yanzu ma na amshe ta wajen me shago”.

“Okay, I want to talk to you. kin san jiya Tsoho me ran ƙarfe ya taso da babban zance?”

Ido Ayush ta tsira mata tana gyara zaman ta tace, “I wonder what happened?”

Sai da ta sauke ajiyan zuciya kafin tace, “uhmmm! Jiya gaba ɗayan mu yace mu fitar da miji, su Ya Baffa kuma su fitar da mata, we will be married in a month”. ta ƙare maganar da murmushi

Waro ido Ayush tayi, sai dai bata iya magana ba

Sai Shakira taci gaba da faɗin,
“But do you know what? There is a problem, because Hajja tayi wa Ya Baffa mata”.

Still shiru Ayush tayi tana kallon Shakira

“Lafiyan ki ƙalau kuwa Ayush? I’m talking you are silent”.

“To ai maganar taki ne tazo min a bazata. Now you mean I will not marry Dr. Baffa?”

Taɓe baki Shakira tayi tana janyo wasu files gaban ta tace, “to ban dai sani ba, amma idan har kin yi ƙoƙari kin saka ya Baffa ya so ki a ɗan ƙanƙanin time ɗin nan, to tabbas zaki iya auren sa, domin Hajja ta ba shi zaɓi, duk wacce ya kawo zata aura masa, sai dai ban da Ɗahira, kin ga kuwa burina ya cika, dama ita ce ba na so”.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56Next page

Leave a Reply

Back to top button