FAMILY DOCTORS HAUSA NOVEL 1

Sosai Hajja Fatu tayi murna da ganin ta, nan tayi ta nan-nan da ita har ta cika mata gaban ta da kayan ciye-ciye
Ruwa kawai ta ɗauka tasha, sannan ta kalli Hajja Fatu tace, “Hajja where is Shakira I didn’t hear her movements?”.
“Ai kuwa Shakira tana wajen Yusra, amma yanzu zaki ga ta zo tunda ta san an tafi ɗauko ki”.
Gyaɗa kai Sa’adatu tayi, kafin ta sake cewa, “Hajja is something happened to Yaya Baffa? na ga tunda muka zo be ce min komi ba ne?”
Murmushin yaƙe Hajja tayi tace, “bar shi nan yanda kika ganshi, shi ya san me ke damun shi”.
Langaɓe fuska tayi tace, “eyya Hajja taya zan bar shi bazan damu ba? kinga fa shi ɗin Yayana ne, wlh baki ga tunda muka biyo hanya duk na gama damuwa da halin da na ganshi, ko dai Ni ce ba ya son gani?”.
Hajja tace, “Taya Zaki ce haka? Ina ruwan shi dake da zai ce ba ya son ganin ki? Kin San tunda nayi masa maganar bazai auri yarinyan da ya zaɓa bane, shi ne ya dena min magana, ko abinci ma ba ya ci a nan, ya dena walwala gaba ɗaya, Ni kuwa bazan yarda ya aure ta ba bayan ga ki kina son shi, muddin idan be kawo wacce yake so ba, to ke ce matar sa da yardan Allah kamar yanda muka tsara”.
Washe baki Sa’adatu tayi, cike da farin ciki tace, “Allah ya amsa bakin ki Hajja ta. Amma to wace ce wacce ya ke so ɗin?”.
“Kar ki damu ba sai kin san ta ba, don ba na son ma maganar tariƙa tsawo azo kuma a samu matsala, maganar ta faɗa kunnen wani”.
“Haka ne Hajja, amma ai Yakamata ki sanar dani tun wuri, don wlh har na ji tsanar ta a raina, kinga kuwa gwara in santa in San yanda zan yi zama da ita koda watarana na ganta”.
Taɓe baki Hajja Fatu tayi tace, “ai kin ma santa tunda ba wata ƴar nesa bace, Ɗahira ce ta nan gidan”.
“What ..! But wlh Hajja I hate this girl so much, God forbid that you forbid her, Allah yasa gwara da kika hana, don wlh wannan yarinyan idan ta aure sa babu ke babu ɗanki, domin irin su ne masu raba uwa da ɗan ta, sai dai ki riƙa hangen sa daga nesa”.
“Ai nima shi na gani, ya rasa wacce zai aura sai ita, ba ga shi ba muna gani a wajen uwar ta, yanda take juya Al’ameen, Bilkisu kuwa ta zama abun kallo kamar ba ita ce matar sa ta farko ba, sai abinda tace za’a yi, ke wlh in gaya miki duk iyayen nasu maza sun fi ƙaunar ta, idan har wani abu zai fito daga hannun su to ita suke ba ma wa, ko Kaka shima idan zai yi shawara da matan gidan ita yake kira, komi yace A’isha, uhmmm wlh abun yana baƙanta mini Rai, shiyasa na matuƙar tsanar ta sabida gaba ɗaya Kaka ya rage nuna min kula wa kamar baya, burina kawai ta bar gidan nan tunda Innar ku Safiyya bata aure sa ba, to nima bazan samu kwanciyar hankali ba har sai na kora ta ta bar gidan nan. Mu dai bar maganar nan ki ci abinci tukunna”.
“Ok Hajja”. Sa’adatu tafaɗa tana saka hannu ta buɗe coolarn
Daga nan sauya hiran suka yi, inda Hajja take tambayan ta mutanen gida da basu gaisa ba.
⚫⚫⚫⚫⚫⚫⚫⚫⚫⚫
Gaba ɗaya a kwanaki biyun nan da suka wuce Ɗahira ta sauya, ba komi ya sauya ta ba illa kewar masoyin ta, a kullum ranan duniya zata ɗau wayan ta sau babu adadi don ganin ko zata ga message ɗin sa, sai dai kuma har ranan ta wuce baza ta ga ko me kama da Numban sa ba, ta kasa haƙura har kiran Numban tayi, amma kuma a kashe ne kamar ko yaushe, duk ta rasa nutsuwar ta ta saka wa kanta tunani, kullum bata da aiki sai tunanin sa, idan ta je Office ma zama take yi tayi ta faman tuna sa, har mafarkin sa tana yi wai ga shi sun haɗu, tabbas sosai take son bawan Allan nan da ya guje ta, ta kasa cire sa a ranta ta saba da rashin sa, ga shi ya tafi ya bar ta koda sunan sa ne bata sani ba, illa kawai A.A.A. da ya rubuto mata a ƙarshen text message ɗin da yayi mata na ban kwana, kuma duk iya tunanin ta na ganin ta gano ma'anar A.A.A ɗin ta kasa, haka zata zauna ta saka wannan sunan ta saka wancan sunan don ganin ta ba shi suna, amma ko wanne ta saka sai ta ga be dace ba.
Ga shi tana son tayi magana da Baffa, koda zai ba ta shawara ne, amma kuma ta kasa ganin sa shima, shi kaɗai ne wanda zata iya faɗa masa damuwar ta amma kuma duk idan taje office ɗin sa ba ta ganin sa, dole yau bayan ta shirya zata wuce aiki, sai ta fara wuce wa Part ɗin su ta duba sa, wataƙil akwai abinda ke damun sa ne ba ta ganin sa a Hospital, Tabbas tana ji a jikin ta ba ya zuwa ne, idan da yana zuwa dole zai neme ta.
A time ɗin su Hajja Fatu duk sun tafi aiki, illa Sa'adatu dake zaune ita kaɗai a Part ɗin, tana Parlour ne tana Breakfast tana latsa wayan ta, sai ta jiyo sallaman Ɗahira da ta shigo parlour'n, ɗago kai tayi tana kallon ta, sai ta ɓata fuska tana kau da kanta
Ita kuwa Ɗahira fara’a ta saka a fuskar ta tana cewa, “ah ah yau Sa’ada ce a gidan na mu? Saukar yaushe ba mu da labari?”
Sa’adatu bata ɗago kai ba, sai tsaki da taja tana kai loman abinci
Hakan sai ya sanyayar wa da Ɗahira jiki, bata sake cewa komi ba tayi hanyar ɗakin Baffa
“So, Ma’am, where are you going?”
Juyo wa Ɗahira tayi tana kallon ta, hakan yasa suka haɗa ido
Sai Sa’adatu ta banka mata harara tace, “dama kin bar wahalar da kanki a kan Ya Baffa, domin kuwa shi ɗin nawa ne Ni kaɗai, ba’a yi macen da ta isa ta ƙwace min shi ba, don haka idan ma zaki nemi mijin ki a can wani wajen ki nema, domin dai Baffa nawa ne, nima kuma tashi ce”.
Baki sake Ɗahira take bin ta da kallo, a haƙiƙanin gaskiya Sa’adatu ba wai haushi ta ba ta ba, illa dariya da maganar nata ya bata, wanda har sai da ta murmusa, a ganin ta in ba hauka ba, Taya ma zata ce ta zo wajen Baffa ne domin neman soyayyar sa, bacin ta san da cewa shi ɗin yayan ta ne, ko kaɗan bata taɓa kallon Baffa a matsayin wanda zata iya aure ba, ba wai don wani abu ba, a’a, sai dai tana mishi kallon wanda suka fito ciki ɗaya, duk yanda mutane suke fassara su bata taɓa koda kallon abun hakan ba, “to meyasa su suke wannan tunanin?” Ta tambayi kanta idanuwan ta akan Sa’adatu tamkar da ita take yi, sai dai yanda tayi maganar a hankali babu wanda zai iya ji bare ya bata amsa. Ajiyan zuciya ta sauke sannan ta juya taci gaba da tafiya zuwa ɗakin nasa, don a ganin ta ɓata lokaci ne ta zauna tana biye wa Sa’adatu, tasan ciwon kanta, duk da a girme dai baza ta girmi Sa’adatu ba, amma kuma za su yo sa’anni da juna.
Tana zuwa ƙofar ɗakin ta cinma a rufe yake, bata yi ƙoƙarin buɗe wa ba duk da kuwa tana tare da keey ɗin ɗakin shi a cikin nata, tunda tasan shi dai ta zo nema ba wani abun ba, shiyasa ta juya ta wuce tabar Part ɗin baki ɗaya, ko kallon inda Sa'adatu take zaune ma bata yi ba. Motan ta ta hau ta wuce Hospital, tana isa ta fara zuwa Office ɗin Baffa, amma kuma babu shi sai dai Office ɗin a buɗe yake, kai tsaye lefter ta hau ta koma Office ɗin ta, ta soma duba Patients ɗin ta, tunda a time ɗin har sun soma zuwa.
[6/4, 11:48 AM] Oummu Ɗahirah: ????????????????????????????????????????
FAMILY DOCTOR’S
????
????????????????????????????????????????
????????????????????????????
NAFEESAT RETURN
????????????????????????????
MALLAKAR:
NAFISAT ISMA’IL LAWAL.
بسم الله الرحمن الرحيم
⚖
???????????????????????? ????????????????????????’???? ????????????????????*
®Ɗ???????????? ???????????????????????? ???????? ????????????????????✓
???????????????????? ???????????????????????? ????????✍️
????????????????????????????: ????????????????????????????????????????????????
\????.????.????????/
????????????????????????????????????????
???????? ???????????????????????????????? ???????? ???????????????????????? ???????? ???????????????? ɗ????????????. ????????????????’???? ????????????????????????.
HIKIMAR FARILTA SALLAHAn farilta sallah domin a cikin ta akwai godiya ga Mani'imcin sarki jalla Ta'ala, wanda yake shi ne macancancin godiya da yabo, kuma shi ne kaɗai muka keɓe shi da ruku'u da sujada. Ba wani mahaluki da ya dace da wannan. Idan wata masifa ta sami mutum yakan yi maza ya fake da Allah ta yin Sallah, kamar dai yadda Allah yayi umurni a cikin suratul Baƙara, aya ta 45 da cewa: "Kuma ku nemi taimako da yin haƙuri, da Sallah". Ganawar da bawa yake yi da Ubangijin sa a cikin Sallah ita ce bauta wadda take ƙarfafa zumunta tsakanin bawan da Ubangijin nasa. Ubangiji kuma yana yi wa bawan baiwar darajar samun kusanta da shi. Hikima ce kammalalliya da aka farilta sallah, don kuwa ta yin Sallah ne ake kankare wa bawa zunubai, muddin dai ya yi sallah yadda ake so. An ruwaito cewa annabawan da suka wuce, ko wannen su yana da Sallah da yake ibada da ita. Sallolin suna da lokatai biyar; asuba, azahar, la'asar, lokacin faɗuwar rana da na isha'i. Ashe za mu lura cewa Allah ya tara wa Annabi da al'umma tasa sallolin dukan annabawan da suka gabata. Allah ya sa mu dace.
*EPISODE Twenty Six*
*SUNDAY*
Gaba ɗaya sun taru a General Parlour kamar yanda al'adan gidan yake, sai da suka gama raha da nishaɗin su, sannan Kaka ya soma magana da cewa, "Kai Fadil ki rawo Fodio tunda ya ƙi zuwa".
“To Kaka”. Fadil ya amsa mishi da sauri yana tashi ya fita
Babu jima wa sai ga Fadil ya dawo, ya isar da saƙon zuwan Usman
Kamar mintuna biyar da shigowar sa ne, Usman ya shigo yana ciccin magani, fuskar nan ko alamun fara’a babu, babu wanda yayi masa magana sai Big Dady dake faman hararan sa, sai dai shi ɗin be ma san yana yi ba, tunda be kalli kowa ba, ya samu wuri ya zauna gefen Baffa, sannan ya gaishe su yana latsa wayan sa
Kowa ya amsa, banda Big Dady da hakan ya ƙular da shi, a fusace ya ce, “kai Usman wannan wani irin ɗabi’ar banza ce? Ina ce gaishe mu kake yi amma kanka a waya?”
Sai a lokacin Usman ya ɗago kansa, sai dai be ce komi ba, illa jikin sa da yayi sanyi ya zame hannayen sa daga wayan ya bar sa a saman cinyan sa
Zai sake magana Big Dady, sai Kaka ya tare shi da faɗin, “bar wannan maganar Noor, mu Yi abunda ya tara mu, kasan halin wannan yaron meyasa kake son ɗaukan zafi da shi ne?”