FAMILY DOCTORS HAUSA NOVEL 1

Can kuwa wajen babban motan nan tuni tayi ciki da wasu motan da suka dumfaro ta, nan da nan motoci da mashina suka harhaɗe aka haɗa babban hatsari, jini ya soma ambaliya a titin, machine ɗin nan na saman motan Ɗahira, inda wata motan kuma ta bugi motan nata tuni tayi ratsa-ratsa.
Kankace me mutane sun soma zuwa ceton rai, nan da nan wajen ya hargitse da hayaniya. Allah yasa kusa da asibiti ne, nan akai ta zaro mutane ana nufan asibiti da su.
[6/6, 9:23 AM] Oummu Ɗahirah: ????????????????????????????????????????
FAMILY DOCTOR’S
????
????????????????????????????????????????
????????????????????????????
NAFEESAT RETURN
????????????????????????????
MALLAKAR:
NAFISAT ISMA’IL LAWAL.
بسم الله الرحمن الرحيم
⚖
???????????????????????? ????????????????????????’???? ????????????????????*
®Ɗ???????????? ???????????????????????? ???????? ????????????????????✓
JIKAR LAWALI CE✍️
Wattapad: UmmuDahirah????
\????.????.????????/
SADAUKARWA
???????? ???????????????????????????????? ???????? ???????????????????????? ???????? ???????????????? ɗ????????????. ????????????????’???? ????????????????????????.
_Wannan shafin naku ne Masoyana, kar ku ce ban gaishe ku ba????, to ku shaƙata da wannan na ku ne kyauta, ina ƙaunar ku nima, har da waɗanda suka ɓoye kansu, Ni *JIKAR LAWALI* ina matuƙar jin daɗin nuna soyayyar ku gare Ni, idan baku Fans to babu Ni ce._
*EPISODE Twenty Eight*
Su Abbu na cikin Office ɗin Big Dady, inda suke meeting a kan shigo da magani da za'a yi musu, da sauran abubuwan da asibitin yake buƙata. A lokacin ne labarin mummunan hatsarin da ya afku a wajen Hospital ya iso gare su, ai tuni sun fito don zuwa su ba da agajin gaggawa
Sai da suka sauka downstairs ne, labari ya riske su da Ɗahira hatsarin ya ritsa. Innalillahi wa’inna ilaihi raji’un tashin hankalin da suka shiga baki ma bazai iya bayyana shi ba, kankace me sun ruɗe gaba ɗaya kowan su sai sharce gumi yake yi, musamman da suka ga yanda ake shiga da masu hatsarin rai a hannun Allah. Nan su ma suka bi ayari fannin emergency rooms
Su Baffa da Fadila basu fito gida ba ma, labari ya kai musu, tunda shi Baffa dama be yi ninyan shiga ba yau, sai yamma, amma tuni sun ruɗe da su Aunty Amarya sun taho asibitin, sai dai an kasa sanar wa Kaka tunda ba'a san halin da take ciki ba yanzu.
Lokacin da suka iso asibitin, a reception suka tarar da su Aunty Zainab da Yusra da Shakira, tunda su ba fannin su bane, su Big Dady kuma na ciki.
Haka DOCTORS da staff's suke ta sintiri suna ba da taimakon gaggawa
Baffa wuce su yayi ya bar su nan, shima ya nufi emergency rooms ɗin, duka tagumi suka yi har Hajja Fatu, domin itama taƙi shiga tunda itama ba fannin ta bane. Aunty Amarya ne kaɗai a wajen take share hawaye, sai Fadila da tayi zugum tana tunanin ƴar uwan ta a ranta, har bata san sanda ƙwalla ya zubo mata ba, babu abinda take tuna wa sai fitowar ta gida yanzu da abinda ya faru, dayake ta side ɗin windown ɗakin su suka tsaya, shiyasa tana kallon draman da suka yi da su Sa’adatu daga saman bene. haka Allah ke lamarin sa, da mutuwa ne sai a aiko musu a ce ta mutu.
Allah ya taƙaita, Ɗahira bata wani ji rauni sosai ba, sai dai suman da tayi ne har yanzu bata farka ba, ta samu buguwa a kanta har da ciwo, sai kuma gwiwar ƙafafuwan ta da suka ƙuƙƙurje. Alhmadulillah gaba ɗaya ahalin sun samu kwanciyar hankali musamman da suka shiga suka duba ta, time ɗin tana barci tunda an yi mata alluran barci, ba'a haɗa ta da kowa ba a ɗakin da take, sauran suna can rooms ɗin, sun daɗe wajen ta, inda suka je ɗaki-ɗaki suka duba sauran mara su lafiyan.
Sai da ta farka kafin su Aunty Amarya suka bar asibitin, tare da masu aiki suka koma tunda sun kawo musu abinci.
Ɗahira tana samun kulawa sosai wajen su Abbu, barin ma kar ace Doc. Sa'id, domin kasancewar fannin sa ne, shi yayi ruwa yayi tsaki yana kula da ita, abu kaɗan ya matso kusa da ita yana tambayan ta abinda ke damun ta, sai hakan ya faranta ran iyalan gidan, musamman su Abba, don a tunanin su akwai wani abu a tsakanin su, tunda itama Ɗahira sosai ta saki jikin ta dashi, ta yanda ma ta nuna sanayya a gare sa.
Hakan ko kaɗan be ma Baffa daɗi ba, shiyasa be wani zauna ba ya bar wajen, domin bazai iya zama yana kallon wani banza yana hira da ita ba, da kuma bata kula wa sosai.
Usman kam koda ya san abinda ke faruwa, ko leƙowa be yi ba, yana Office ɗin sa, sai da Big Dady ya kira sa yayi masa faɗa, sannan ne ya zo ya duba ta, kuma komi be ce mata ba, kamar yadda itama bata ko kalli inda yake ba. Haka ya juya yabar ɗakin yana taɓe baki.
Babu wanda ya sanar wa Kaka, har sanda su Abbu suka dawo gida, sannan ne suka sanar masa cikin nutsuwa, amma duk da haka sosai ya ɗaga hankalin sa, cewa yayi "dole sai an kai sa ya duba ta". Ga shi lokacin dare ne. Dole haka suka fito gaba ɗayan su, Big Dady Abba da Abbu suka nufi asibitin.
Umma ce da ɗaya daga cikin ƴan aikin su za su kwana da ita, bisa umarnin Abbu. time ɗin ma tayi barci sanda suka zo
Sai a nan hankalin Kaka ya samu sukuni tunda ya ganta a kyakykyawar yanayi. Sun jima kafin suka baro asibitin.
Washe gari da safe ma ya saka aka sake kawo shi
Lokacin Ɗahira na zaune tana shan tea da aka haɗa mata suka shigo, taji daɗin ganin su, nan tabi su ɗaya bayan ɗaya tana gaishe su
Kowan su na amsa mata cike da kula wa, tare da tambayan ta ya jiki?
Murmushi tayi tace, “it’s so easy”.
Big Daddy yace, “Are You sure my daughter babu abinda ke damun ki?”
Gyaɗa kanta tayi tana sake tabbatar masa da cewa, “Yes my Dady”.
Murmushin farin ciki gaba ɗaya suka yi
Kaka yace, “ai gaba ɗaya kin ɗaga min hankali Matata, a jiya kasa barci nayi, ban ma karya ba na taho duba ki, ashe ke ga shi har kin samu saka abinci a cikin ki, kin bar Mijin ki cikin tashin hankali”.
Ɗahira murmushi ta sakar masa, tana langaɓe kai tace, “eyya Miji na, ban sani bane ai, ka ga da ban ci komi ba nima kamar kai, na tausaya maka matuƙa tsoho na”.
Dariya gaba ɗaya suka yi har Kaka da ke faɗin, “Ja’ira”.
Itama dariyan tayi cike da farin ciki. Haka suka ci gaba da hira na ɗan wani lokaci, inda su Big Dady suka tafi Offices ɗin su suka bar Kaka a nan, don ya ce, “ba yanzu zai koma ba”.
Doc. Said ne ya shigo da sallama a bakin sa
Suka amsa mishi suna kallon sa, musamman ma Kaka
Shi kuma murmushi yayi ya iso wajen yana durƙasa wa har ƙasa ya gaishe da Kaka
Kaka ya amsa cike da fara’a da jin daɗin girmama sa da yayi
Ɗahira bata bari ya sake magana ba, ta gaishe shi itama
Amsa wa yayi yana kallon ta yana murmushi, sannan ya tambaye ta “ya jikin nata?”
“Alhmadulillah”. Ta amsa mishi da shi
Zama yayi gefen kujeran da ke kusa da gadon ta yana kallon ta, kafin kuma ya ce, “Yakamata a wanke miki ciwon idan kin gama ko?”
Ajiye Cup ɗin hannun ta tayi tana cewa, “ok Doctor I’m done ai”.
Miƙe wa yayi ya soma haɗa magunguna
Ita kuma suna hira da Kaka, inda yake tambayan ta “wane ne wannan?”
Dariya tayi tace, “Kaka Doctor ne shima ai”.
Gyaɗa kansa yayi yana bin Doctor Said da kallo
A haka dai har Doc. Sa’id ya gama abinda zai mata, sannan ya zauna ana hira da shi
Sosai a nan Kaka ya sake fahimtar akwai wani abu a tsakanin su, inda lokaci ɗaya ya ji farin ciki a ransa, shiyasa ya sake jan Doc. Sa’id a jikin sa, ko ba komi nan da lokaci kaɗan zai ga auren Jikar tasa, ko kaɗan ba ya son ƴan uwan ta su yi aure su bar ta, sosai hatsarin nan ya sake ɗaga masa hankali.
Ana haka su Aunty Amarya suka zo
Ɗahira taji daɗin ganin su sosai, nan ta sake sakin jiki ana ta hira gaba ɗaya, ga shi sosai take farin cikin yanda ake ba ta kula wa, musamman su Big Dady, da zaran mintuna ƙalilan ya wuce za su taho duba ta.
Sai yamma duk suka tafi har Kaka.
Kwanan ta biyar a asibitin tana samun kulawa, kafin aka sallame ta, ta koma gida tana ci gaba da jinya. A haka har ta samu sauƙi sosai, inda ta nemi ta koma bakin aikin ta, amma sai Abbu ya hana ta tunda har yanzu ɗingishi take yi.
Sai da aka shafe kusan sati Uku kafin ta warware, sannan ta koma bakin aikin ta, zuwa yanzu sosai Ɗahira da Doc. Sa'id suke mutunci, koda aka sallame ta a Hospital be taɓa zuwa gidan su ba, amma kuma suna waya sosai, hakan yasa suka saba, har ita Ɗahira tana tunanin son ta yake yi, sabida yanda yake ba ta kula wa ainun, shiyasa ma ta sake sakin jiki sosai da shi, sai dai har yanzu kalman da take so taji a bakin sa ya ƙi ya sanar mata, ko kaɗan ba ta ƙaunar a sake zaman meeting ba tare da tana da tsayayye ba, sai dai babu yanda zata yi tunda be ce yana son ta ba har yanzu, sai ma daga baya ta gane yana da mata har da ƴaƴa biyu, amma hakan be ɗaga mata hankali ba, a ganin ta idan yana son ta zata iya auren sa, tunda duk wani ɗabi'u na kirki shi yake nuna mata, sai dai lokaci na ta ja babu wannan kalman a bakin Doc. Sa'id, ga shi har yanzu saura sati biyu auren ƴan gidan.
Kamar yanda suka saba meeting ranan Lahadi, haka wannan Lahadin aka tara su, Ɗahira aka soma tambaya, amma tace musu "bata da wanda take so" maganar ya girgiza su
Kaka yace, “kina nufin wannan Doctorn har yanzu be yi miki ba?”
Kallon Kaka tayi tace, “Kaka ai ba soyayya muke yi da shi ba, it’s just Friendship”.
“Uwata dama ai ta hakan ne soyayya take ƙulluwa, ke dai kawai ki sanar mana idan da akwai wani abu a tsakanin ku, kar ki zauna ki ce zaki ja mishi aji kinji ko?”
Gyaɗa kanta tayi kafin kuma tace, “amma Abba wlh be taɓa cewa yana so na ba, kuma ma yana da iyalan sa”.
Shiru suka yi duk kan su, kafin kuma Kaka ya sake Tambayan Usman da cewa, “to kai kuma Fodio aina taka take?”
“Nima Kaka har yanzu ban samu wacce nake so ba”.
“Kana nufin har yanzu maganar da muka yi maka baka ɗauke ta da muhimmanci ba?” Big Dady ya faɗa yana kallon sa
Shiru Usman yayi kansa a ƙasa
Nan Dady ya dinga faɗa kamar zai ari baki, kuma ya ce “dole sai yayi aure da ƴan uwan sa, idan be samo matan ba shi yana da hanyar da zai samo masa”
Kaka ne ya tsayar da shi da faɗin, “ƙyale shi Noor, duk hakan be ta so ba, yanzu dai aci gaba da hidiman biki kar a fasa, su kuma Allah ya kawo musu na gari, lokacin su ne be yi ba babu yanda zamu yi da su”.
Daga haka ba’a sake yin wata maganar ba, aka sallami kowa.
Inda daga ranan gadan-gadan aka ci gaba da hidimomin biki, ko wanne fanni suna nasu, tunda kowa a cikin su zai aurar, illa Aunty Amarya ce kaɗai da babu ita, amma kuma komi da ita ake yi ana Fadila, duk ita take shirin komi, sai ƴan uwan Umman dake nasu, duk da suna yaɓa mata maganganu amma ko bi ta kansa ba ta yi, abinda yafi ɗaga mata hankali yanda gidan duk ya cika da mutane, babu hiran da suke yi sai na Ɗahira, wai "har yanzu bata da mashinshini, tayi kwantai, maza ma tsoron zuwa wajen ta suke yi, bare su furta mata suna son ta." Kowa ba ya lura ba ita kaɗai bace a gidan da baza ayi auren ta ba, har da Usman, shi da yake ma babban su amma yaƙi auren, amma ita kaɗai ake gani
Sanda Ɗahira ta soma jin ƙananun maganganun nan bata wani damu ba, sai dai yanda ƴan uwa suke taran ta da maganar, har wasu suna mata Shaƙiyanci suna yaɓa mata magana, sai abin ya soma damun ta, amma babu yanda zata yi haka take barin abun a ranta, duk da ita bata cika iya ɓoye damuwa a ranta ba, ko ya ya ne idan har tana da damuwa sai ka gane..
Gida fa ya sake cika maƙil inda har an soma events, duk da ba kowa bane ke wajen, wasu sun tafi can Katsina, Hajiya Laila ma can ta tafi, sai su Firdausi da sauran ƴaƴan ta masu aure da suka zo nan, Aunty Zainab ma da ita da Aunty Amarya, ana gobe suka wuce can a bisa umarnin Kaka, tunda ba za'a bar Hajiya Ikram ita kaɗai tana biki babu ƴan uwa ba, kowa ya zo nan ya shantake, wasu ma zuwa gobe ranan bikin za su wuce idan za'a kai Fadila can, sai su kwana biyu wasu kuma su yi kwana ɗaya.
Tun ana kwana biyu Sa'adatu ta koma Legos, sai ranan bikin za a kawo ta.
⚫⚫⚫⚫⚫⚫⚫⚫⚫⚫
Dafa ta Fadila tayi, hakan yasa tayi firgigit tana kallon ta
“What are you thinking sister, I’m talking to you are you quiet?”
Murmushin yaƙe Ɗahira tayi, sai ta gyaɗa kanta tana son mayar da hawayen dake cikin idanun ta tace, “nothing”.
Cike da tausayin ta Fadila tace, “don Allah ki dena saka damuwa a kan maganganun su Inna, ko ma su waye ne zasu yi miki gori don Allah ki dena saka damuwa kinji, ke baki ga yanda kika faɗa bane? Ana bikin mu amma gaba ɗaya kin tsame kanki a cikin mu”.
Shiru Ɗahira tayi, don bata san me zata ce mata ba
Sai itama Fadilan tayi shiru, sai dai bata tashi a wajen ba. Tsawon lokaci suna a haka kafin Fadilan ta kalle ta tace, “Sister, there is something I want to tell you, akwai maganar da naji wajen Hajja da Shakira, shiyasa naga dacewan in faɗa miki”.
What do you think Fadila will tell her? ????
mu je zuwa yanzu aka soma.
[6/7, 10:41 AM] Oummu Ɗahirah: ????????????????????????????????????????
FAMILY DOCTOR’S
????
????????????????????????????????????????
????????????????????????????
NAFEESAT RETURN
????????????????????????????
MALLAKAR:
NAFISAT ISMA’IL LAWAL
بسم الله الرحمن الرحيم