NOVELSUncategorized

BARIKI NA FITO (BOOK 1) 8

                     PAGE 8
Murmushi tayi tare da ri’ke kugu, tace dole kace fah? Bari kaji ni bariki ba irin matan da ake tursasa su bane, wlh Idan banso ka ganni ba duk yanda

kaso daka ganni bazaka ganni ba, in banda abunka taya zan aureka kai ba babban banana ba, inda kana da banana babba dasai in yarda in aureka, gashi Kai inka tashi baka wasa sai dai ka shige kaman ka sami jaka, sannan kace in aureka, haba wannan maganan wasa kake, sannan Allan musali koda nayi aure toh Wlh nabar ka kenan, kaga cikin zabin ka babu wanda na d’auka, Alh madu dariya yayi yace yaro man kaza, wlh bariki bazan barki ba, miye bana miki? Mai kika ce in miki na kasa? Ko kin tab….  Tace ya isa haka dakata, taci gaba da fad’in duk abunda ka bani cina da kakeyi shine ka biya ni, sannan kuma ban taba ro’kan ka wani abuba, so dan haka baka da daman fad’amin magana, sannan ina so ka sani daka yau na barka har abada, dama bason mu’amalan mu nake ba, kaiba gamsar da mutum ba sai jaraba kabar mutum yaita fama da sha’awa in banda bala’i irin naka kasan abunka karami ne Aida ma sexy doll ka siya sai kayi ta cinta Ina ga da yafi mak……  Tas taji saukan Mari ya wanketa da Mari da sauri ta ri’ke wajan tare da fad’in nika mara? Kara mata wani Marin yayi tare da fad’in kisan da wanda kike magana, kodan Kinga ina sakar miki kike neman cimin mutunci sai insa a kawar dake, murmushi tayi tare da fad’in mutunci baka dashi a wajena tunda ka tube tsirara na ganka tumbur kaga kuwa babu maganan inga mutuncinka har abada, yace dama haka halin karuwa yake so ba’a bun mamaki ne dan kince haka amma zan nuna miki Waye alh madu, dariya tayi tare da tafa hannu tace babu abunda zan gani bariki sunana fah, ko ka manta ne? Dama kace zaka sa a kawar dani Toh Ina jira tana fad’in haka tayi d’aki, Jim kad’an sai gata da akwatin ta tana ja, tsayawa tayi tace sai kasan bariki ka mara ai Kai dan siyasa ne nida kai mu zuba mai karamin ayaba kawai tana fad’in haka ta fice, koda ta fita tsaki tayi tare da fad’in gashi visa din sati d’aya Allah yasa ATM dinta master card ne ciran kud’i tayi haka ta dinga yawo inda taga wani hotel ta shiga ta biya kud’i ta kama d’aki na dai dai kwanakin da zatayi, koda ta shiga d’akin kwanciya tayi akan gadon d’akin Mai shegen kyau, ido ta lumshe tana mai jin tsanar alh madu tare da fad’in dan iska mutum ya kusa mutuwa amma yana neman mata tsohon banza mara mutunci sai Nayi maganinsa wlh, sai na yanke masa wannan Shegiyar karamar ayabarsa dinnan kowa ya huta munafuki, duk wannan surutan bariki ita d’aya take yinsa, kana kallonta kasan ranta a bace yake domin ba karamin haushin Marin da alh madu yayi mata taji ba, tsaki ta saki tare da fad’in Wlh saina wulakanta ka dan iska kawai, saboda takaici ko abinci ta kasa ci. Shiko alh madu ya shiga Tashin hankali da yaga ta tafi dagaske domin bai San mai yasa ba, Allah ya saka mishi son bariki yana son yarinyar Sosai sannan zai iyayin komai danya mallaketa, fita yayi ya dinga nemanta amma babu ita babu Mai kama da ita, haka ya dawo cikin kunci, gashi bai riga dama ya sai Mata sim din kasar ba daya kirata.

Yarima Aliyu sun isa masarautar katsina wajan karfe 3 dan saida yasa suka biya maraban jos ko zaiga yarinyar da yake burin gani amma baiga koda Mai kama da itaba ba, gashi yau baiga habib ba, haka suka ‘kara juyawa don tafiya katsina, bayan sun isa an tarbi Yarima Aliyu cikin mutuntawa, yaso yaje hotel ya dinga kwana Wanda mum dinshi tace karya Fara dan irin al’adan masarautar katsina ne, Indai zaka auri y’arsu sai kayi sati d’aya a masarautar su dan ku saba da matar da zata aura, Yarima Aliyu bai so hakan ba amma babu yanda ya iya, tunda an tursasa shine, kuma bazai iya yima iyayensa musu ba, Yarima Aliyu na zaune akan kujera a cikin bedroom din d’akin da aka daukeshi ba komai yake tunani ba sai yanda zaiyi rayuwan aure da Gimbiya zinatu shidai yasan ba Sonta yake ba, gashi yana yinta da irin maganan ta ya nuna mishi ko ita wacece, inda Tana da kamun kai abunda tayi tun ranan Farko da suka had’u da batayi ba, wai a hakan ma dan akwai jinin sarauta a jikinta, yana cikin wannan tunanin yaji an bud’e kofar d’akin an shigo, d’ago dakai yayi Gimbiya zinatu ce ita da kuyanginta kuyangin sun ri’ke tray da kayan fruit ajiyewa sukayi akan center table sannan suka fita, Gimbiya zinatu zama tayi a kujeran da Yarima Aliyu yake, kallonshi tayi tare dayin murmushi tace ina maka Barka da zuwa masarautar mu,  baiko kalleta ba balle ya amsa, taci gaba da fad’in ina son ka sani Gimbiya zinatu bata magana aki bata amsa, amma tunda ina Sonka kuma naga sarautar taka ita ke hanaka magana, muyi wani abu mana, ni in Ina gabanka mantawa nake dako ni wacece, kaima kayi haka, kallonta yayi sannan yace baki da wannan matsayin, na farko keba kyau ba balle ace don kyanki mutum ya manta dako shi Waye, banga abunda kike dashi ba Wanda zaisa ni Yarima Aliyu in manta dakai na in Ina gabanki, sannan ina so ki sani wannan auren tursasa ni akayi bada son raina bane, so ina son kisa wannan abun a ranki, ina fatan kin fahimta? Shuru tayi ba tare da tace komai ba ganin haka yasa ya tashi daka kan kujeran da take ya koma kan gadon d’akin, tashi tayi tazo har inda yake ta zauna gab dashi tace Yarima  naji baka sona an tursasa Kane ka aureni, amma ina son ka sani baka da wani zabi face kasa ma ranka so na tunda ni zaka aura, kuma karka manta gidan sarauta ba’a saki sai an kama mutum da laifi babba na kisan Kai ko zina…. Murmushi tayi sannan tace Kaga kuwa dole ka soni ba….. Yace really? Kai ta d’aga alaman eh hakane, murmushi yayi tare da fad’in gidan sarauta ba’a saki amma ina da ikon in auro wacce nake so, ke kuma saiki zauna cikin kunci tunda baki da soyayyan miji, hawaye ne ya fara zubar Mata a ido tace Yarima Ina Sonka karka manta da matsayina ni Gimbiya ce inada jinin sarauta amma duk na ajiye nake fad’a maka irin soyayyan da nake maka, dan Allah Yarima karka sa wata mace a ranka sai ni, Wlh bazan iya juran ganin wata tare dakai ba, tana maganan tana kuka, jin kukan nata yayi yawa yasa zuciyarshi ta karaya, gashi baya son sautin kukan nata, yace look zinatu bazan miki karya ba ko in yaudareki bani da burin tara Mata, ni tsari na shine in zauna da mace d’aya, toh amma yanzu what will I do?  Iyayena sun bani ke, and ni kuma bana son wannan auren but tunda Abun yazo da haka dole Nayi accepting sai dai karki sama ranki bazan kara aure ba, domin ke zabin iyayena ce, nima nan gaba kad’an zan aura zabina insha Allah, jin maganan nashi take kaman ana buga mata Rodi akai, wai yau itace namiji yake fad’ama wannan maganan ita da maza da dama sunzo neman auranta taki yarda Yarima Aliyu ne kawai taji tana so, amma kuma sai akai rashin Sa’a shiba ta ita yake ba, kallonshi tayi tace Yarima zan yarda in zama baiwarka har karshen rayuwa na, amma dan Allah ka daina tunanin Karin aure ni Gimbiya zinatu bazan iya had’a kishi dako wace mace ba, ina nufin ko wace mace, Yarima Kai ya girgiza dan yaga alaman tayi nisa, sannan komai zai fad’a mata bazata gane ba yanzu sai yasa yace Mata Ina bukatar hutu zaki iya tafiya, kallon shi tayi tace zan tafi yanzu amma ina son ka sani ni d’aya ce matarka har abada tana fad’in haka ta fita daka d’akin cikin fushi, shiko dariya ma maganan nata ya bashi yace mad girl. Gimbiya zinatu na shiga d’akinta ta Fara fashe fashe tana jifa da kayan d’akin tana kuka, mai yasa na Fara son wanda baya sona? Miye banda shi? Maina rasa? Kuka take Sosai duk ta fashe kayan glass din d’akin gaba d’aya, idonta yayi ja, tace zan iya juran duk abunda Yarima zai min bayan munyi aure amma bazan jura yace zai kara aure ba, inko Yarima dagaske yake zai kara aure inya aureni Wlh sai dai nida shi da amaryan mu mutu, bazan jura ba bazan jura ba, duk wannan abunda take kuyanginta suna kofar d’akin suna jinta, jin tayi shuru yasa sukai tunanin shiga cikin d’akin suga ko lafiya, suna shiga sukaga komai ta fasa ita kuma tana zaune a kasa tana hawaye, cikin sauri suka fara kwashe kayan daya fashe bayan sun gama suka nufi wajan mahaifiyarta suka fad’a mata halin da gimbiyar ke ciki, bayan mum dinta tazo cikin Tashin hankali ta kalli y’ar tata Wanda hannunta duk taji ciwo, mamanta tace zinatu lafiya maiya sameki? Rungume mamanta tayi tana kuka tace mum Ina son Yarima Aliyu Ina sonshi bazan iya juran in ganshi da wata mace ba, maman tace kaman ya? Tace mum cewa yayi In munyi aure zai kara auran wata, maman tsaki tayi tare da fad’in Toh sai me? Danya kara aure laifi ne? Dama akan wannan abun kikai wannan haukan? Wlh ban taba sanin baki da hankali ba sai yau ke matan babanki nawa, kin taso Kinga mu biyu ne, danme zaki ce mijinki bazai kara aure ba inya aureki, wlh ki shiga tai tayinki tun wuri karma ki bari Mai martaba yaji wannan zancen dan Wlh sai yayi mugun saba miki, maza ki tashi ki bada umarni a kawo miki wasu kayan tunda kin fashe wannan mara tunani kawai, fita maman tayi cikin takaicin y’ar tata, Gimbiya zinatu tashi tayi ta koma wani falo bayan ta bada umarnin a kawo mata wasu kayan, zama tayi tana tunanin yanda zata bullowa Abun.
Washe gari Bayan su Hjy habiba da Haulat sun tashi daka bacci, bayan sun kimtsa, Haulat tana manne a jikin Hjy habiba tace amma wannan ne yin lesbians dinki na farko koh?  Hjy habiba tace mai kika gani? Haulat tace akwai abubuwa da yawa wanda baki min ba nima ban miki ba, Hjy Habiba tayi murmushi tace kaman me fah? Haulat dariya tayi tace naga baki bari nahau ki ba, Hjy habiba tayi murmushi tace gaskiya na yarda kin dad’e kina wannan Abun Toh amma ni maganan gaskiya jiya na farayi ban taba yiba, sai dai Inbi maza, ganin in naci gaba dabin maza Asirina zai iya taunuwa ga mijina sanannan mutum, sai yasa kawata taban shawara akan in daina neman maza gara Mata domin duk Wanda ya ganki bazai kawo komai a ranshi ba, mijina minister of finance ne yana da mahaukatan kud’i, komai nake so ina samu amma bashi da lokaci na, inya ya sami lokaci na toh baya gamsar dani, ni kuma bazan iya rabuwa dashi ba sai yasa na fad’a wannan harkan, kawaye na duk suna lesbians domin duk matsalan mu d’aya mazajanmu suna da kud’i amma basu da lokacin mu, ina da yaro d’aya yana kasar Canada yana karatu, sai inyi wata wani zubin banga mijina ba, Kinga ai ni mutum ce ba dutse ba, Haulat tace hakane Hjy, Hjy habiba tace daka yau Momy zaki dinga kirana Kinji? Haulat tace eh mumy, murmushi Hjy habiba tayi tare da fad’in kinsa naji dad’i dama Hjy Umaima tasha fad’a min love da mace akwai dad’i ni Wlh kinfi min duk mazan da Nayi hulda dasu, Haulat dariya tayi tace damma ban hauki ba Aida kinfi jin dad’in abun, Hjy habiba tace toh muyi na safe mana tare da kashe ma Haulat ido, Haulat tace Momy muje muci abinci tukun na mana, dakyar Hjy habiba ta yarda sukaje sukai breakfast, tun a wajan cin abincin take ta wani shafa Haulat tana romancing dinta, bayan sun kammala sukai ciki inda aka fara wani sabon Abu. Kwanan Haulat biyar a Abuja tace ma Hjy habiba zata dawo kaduna, Hjy habiba tace ta Bari ta kara mata kwana biyu mana, Haulat tace zata dawo amma tana son tafiya yau akwai abunda za tayi, badan Hjy habiba taso ba ta sallami Haulat tare da bata kud’i masu yawa tasa driver ya tafi da ita har kaduna din. Lokacin dasu Haulat suka karasa maraban jos tana fita direct d’akin magajiya ta nufa inda taga magajiya tana waya ko bata tambaya ba tasan ita da Hjy habiba ne dan sanda ta shigo taji magajiya na fad’in Kinga y’ar halak din har sun Iso, bayan magajiya ta gama wayan cikin dariya tace kinja kaya koh? Haulat tace naja kaya kuma nasha wuya Wlh magajiya wannan matar jarabbiya ce mata koda yaushe tace Ayi love kai Wlh duk ta tsotse ni, magajiya dariya tayi tace hakuri za kiyi da ita dan Wlh matar akwai kud’i gashi bata da rowa Kinga in kina Mata abunda take so zaki ja kud’i Sosai, Haulat tace haka zanyi ta hakuri, amma fah akwai jaraba Kut gata babbace amma tana son harka, bari kiga inje d’akina in huta, magajiya tace toh ki kunna wayarki dan tace ta kira a kashe, tace toh, aiko tana kunna wayar saiga kiran Hjy habiba d’auka tayi tare da barin d’akin magajiya, Hjy habiba tace daughter kin koma lafiya? Tace lafiya kalau Momy, Hjy habiba tace Wlh Nayi missing dinki Sosai ji nake kaman ki dawo wlh, dan Allah ki tawo gobe mana, Haulat tace Momy Ina zuwa zan kiraki, kashe wayan tayi tare da fad’in Kut wannan matar harija ce Wlh karo sukaci ita da Hjy babba, yace na shiga uku miye haka? Ganin Haulat ce yasa yace oh ke kuma daka ina? Nasha ko wani gardin ne ya bigeni Ashe yar uwata ce mace wai ina kika je kwana biyu? Tace Hmmm Hjy babba Abuja Naje Hjy babba yace kice kin ja kaya, tace naja kaya nasha wuya kuma ba, tabe baki yayi tare da fad’in kodai kin samu Mai plantain ne? Tace ai in big banana ne Aida sauki, wajan wata tsohuwar kilaki Naje duk ta tsotse ni, Hjy babba yace oh sai yasa naga duk kin fige kin rame Ashe kin had’u da jarabbiya tace Kedai bari Hjy babba, tace bariki fah? Yace bata nan amma Nasan zuwa jibi zata dawo itama inji inda taje take boyemin zata Mai dani karamar karuwa, gaba yayi yana wani tale kafa tare da turo duwawu baya Wai shi a dan dole mace …..
MARYAM OBAM

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button