Uncategorized

ABDUL JALAL PART 1 HAUSA NOVEL

“Hakane mami, Allah ya nuna mana lokacin da burinmu ze cika zan cigaba da hakuri in cigaba da kokari se burinmu ya cika akan Jalal da mummyn Sa”

Buri kuma, Wane irin buri ne haka hasashe na ze zama gaskiya kenan
Jalila tayi maganar a zuciyarta
Fasa abinda tayi niyya tayi takoma cikin Gida

Kayan da aka aikomata daga gidansu Jalal taga Nana tana budewa
Less ne me kyau da agogo se turare da wani Dan karamin kit Ja anyi rubutun larabci a jiki Qur’ani ne izu sitting a ciki me matukar kyau
Se envelope da akasaka kudi dubu goma
A jiki aka rubuta
safe journey from daddy

“Yanzu duk wannan nawane?”
“Ai Jalila indai kyauta ne babansu Jalal akwai kyauta yana da kirki sosai”

“Nana ni duk Qur’anin nan yafi min kyau bazan dinga bude shi ba ajiye shi zan in dinga kallonsa yayi kyau sosai ajiya zan masa me kyau”

Nana ta kwashe da dariya
“To ai saboda ki karanta akabaki shi sekuma yazama abin kallo”

“Eh mana koba komai zan dinga tuna baban zalimu ne yabani”

“Me kikace Jalila?”
“Ba komai, bari inje in nunawa maama kayan”

Zuwa sukayi suka nuna mata ba fuskarta ba yabo ba fallasa tace yakamata taje tayi musu godiya
Sannan itama tabata abinda zata bata
Abba yayi mata nasiha sosai sannan yace university a kano zatayi in lokaci yayi zezo a Dakota daga Kaduna
Jalila ko a jikinta bata dauki abun serious ba ita dai babban burinta taga sun kama hangar Kaduna
haka yaimata alheri shima tare da yimata nasiha akan hakuri da rayuwa ta kula da tarbiyarta sannan tayi karatu.

Misalin karfe biyu tagama shirinta tsaf JAWWAD kawai take jira
after dress ce a jikinta baka se mayafin After dress din data yafa akanta tayi kyau matuka

Taje gidansu Jalal tayi musu godiya
Daddyn Jalal shima haka yayi mata nasiha tai musu godiya ta fito taga Ilham ta dawo maybe wani gurin taje

“Juliet INA romeon naki,?
Tafada cike da tsokana
Nikam yau zan koma inda na fi wayo nasan na bata miki a Dan zaman damukayi kiyi hakuri Ilham ni duk abinda na miki wasa ne”

Mtsewww Ilham taja wani dogon tsaki
“Ke kikasani ma gulmaciyar banza kawai”
Ilham ta fada tana ma Jalila kallon up and down
Jalila tayi wani kasaitaccen murmushi

“Nagode Yar wahala nice ma ke, let me tell u something ur mission will fail u will never succeed”
Tafice daga gidan tabar Ilham tsaye tana juya maganar Jalila
“Ur mission will fail”

A harabar gidan taga Jawwad da mayensa
Jawwad yasamata trolley dinta a boot
Jawwad na ganinta yace
“Masha Allah looking so gorgeous sisyna let’s take a pic”

Kusa dashi Jalila taje ta tsaya sukai ta hotuna hada Nana

Shikam gogan wani uban tsaki ya dinga Ja ganin yadda JAWWAD yake biyewa wannan fitsararriyar yarinyar

Nana ce ta rungumo Jalila tana share kwalla “Dan Allah kikuma dawowa”
“Insha Allah karki damu Nanancy na zankuma zuwa insha Allah”

Suka shiga Jalila suka kuma sallama da maama sannan ta fito

Jawwad ya Riga ya shiga ya kunna mota yana jira ta karaso ta faki idon Jawwad
Tacewa Jalal to yau zan tafi se hankalinka ya kwanta bame kumayi maka shishshigi amma zan tuna maka ne ban yafema cin zalina da kaiba mugu kawai kuma insha Allah se……
Bige mata baki yayi
“Ki barni da Wanda akayi min a baya yake wahal dani, in kika sake kikamin mummunar addu’a a sena baki mamaki
A cikin gidan naku a gaban yayan ki zan tattakaki in koya mini hankali dama namiki alkawarin maida ke Irina amma tunda tafiya zakiyi yayanki zan mayar Irina, in ya aureki se aji dadin fada matar Dan giya

wuce ki bani guri ko in barar dake anan Mara kunya sha³”

Kaman munafuka haka ta wuce tana shafa baki taga ko Jini ya fito

Nana tafito da karfi race
“Jalila safe journey I will miss u”

Daga mata hannu kawai Jalila tayi ta shiga gaban motar saboda bakinta ji take kaman banata ba
Jalal ne yazagayo inda Jawwad yake dan uwana a sauka lafiya, ka dawo da wuri Dan Allah, akwai wani zazzafan guri dazaka rakani
Jalila ta dago da sauri tana kallonsa
Allah ka tsaremin yayana

“Ta Allah bataka ba “
Tafada a fili
“Ya dai magana kike ne”
Jalal yai mata tambayar

“Bakina ne a haka tabashi amsa”

“Na fuskanci dai ba kwa jituwa, Jalal ma fa yayankine”
Jawwad yai magNar yana kallon Jalila
“Allah ya kiyaye”

“Dan uwana ina dawowa zan raka ka insha Allah idan na dawo”
Jalal yafada yafara Jan mortar

“To seka dawo”

Sun hau kan kwalta sosai Jawwad tuki yake a hankali cikin kwarewa
Jalila tayi nisa cikin tunani

“KE YAKAMATA KINEMI YAFIYATA , DUK WANI ABU DANAKE AIKATAWA KECE SILA,
KINSAM GASKIYA AMMA KIN RUFE IDONKI KINAMIN FADA”

“ZANCIGABA DA HAKURI HAR BURINMU YA CIKA AKAN JALAL DA MUMMYN SA”

“KARKI SAKE KIMIN MUMMUNAR ADDU’A KIBARNI DA WANDA AKAYI MIN ABAYA YAKE WAHAL DANI”!!!!!!

Gaskiya akwai abubuwa masu rikitarwa game da rayuwar Jalal haka nan taji tana son Sani

” sisyna”
“Na’am yayana”
“Nasan abinda yasa kikeson komawa gida, yana da nasaba da abinda Yaya mairo taimiki, Amma Dan Allah kiyi hakuri ki dena bari irin wannan maganganun suna tasiri a zuciyarki kowa yasani dagake har Ummi mutanen kirki ne
Ni kaina banji dadinin abinda tayi ba”

“Yaya na nifa ba hakane yasa zan koma Gida ba kamanta kawai”
“Kin tabbata?”
“Eh na tabbata babban Yaya”
“To yanzu se yaushe zaki dawo?”

“Se wataran”
“Se wataran kuma ba rana kenan”
“Hhh da wataran zan dawo”
“Hmm to shikenan”

Shiru ya Dan ratsa
“Yaya Jawwad”

“Nana’am Anty JALILA”
Murmushi tayi
“Wadan dan Allah wace Ilham a gurin Jalal”

“Yaya JALAL dai shima yayanki ne”
Allah ya kiyaye Amma a fili se tace
“To naji zan dinga fada”

“Yawwa sisyna
Yadda muke dake cousins haka ILHAM take da Jalal da mummyn Jalal da mamann ILHAM ubansu daya
Gyada kai Jalila tayi
” to meyasa Jalal yake haka, meyasa kuma ka

ke abota dashi,? Gashi ya raina mamansa kaga abinda yake mata kuwa?
“JALAL ko?”
JAWWAD yafada yana kallonta
“Au namanta Yaya JALAL”

Ajiyar zuciya yayi yace

“Se randa kika dawo kano zan baki amsoshin tambayoyinki”

“Why not now?
Ta tambayeshi

” kawai sekin dawo Kano zan gaya miki ke dai in kinyi sallh kidinga Sa shi a addu’a

Gyada kai kawai tayi

Amma a ranta cewa tai tabdij nida kano ai seda wani babban dalili
A gefe data kuma zuciyarta na kwadaita mata son sanin waye Jalal

Share please

More comments more typing…….

Aimin afuwa page din yau bashi da yawa am busy that’s why

Naji shiru ba akawon ragon salla ba
In ba abani ba nadena typing se bayan salla lolz????

Inayinku masoya wannan novel irin sosai din nan ❤❤❤ comments dinku na kayatarr dani
Ku biyoni a hankali domin ganin darrusan dake cikin littafin

????️????️????️????️????️????️
[8/31, 8:26 AM] Safiyya: ????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????

_ABDUL  JALAL_
       (2020)

  _WRITTEN BY AISHA HUMAIRA_
(Daddy's girl)

           PAGE-  8

PART 1

_Bismillahir Rahmanir Rahim, da sunan Allah me Rahma me jin kai, Allah ka yi salati a bisa shugaban mu Annabi Muhammad (salallahu alaihi wassalam)
Bayan haka, ban rubuta wannan littafi domin cin zarafin wani ko wata ba, na yi shine domin nishadantarwa, da kuma wa’azantarwa, ku biyoni domin jin me wannan labarin ya kunsa.
Yanda nafara Allah yabani ikon kammala shi

Ina maraba da shawarwari, sharhi, ko kuma gyara, nagode.

Domin Samun karanta wannan littafin yi magana ta what’s app akan wannan lambar

07063065680
What’s https: //chat.whatsapp.com/EtB4KI52K0v5FQc2ELhidL

Is a free book

I want comments not stickers or just thanks????????????????
Your comments give me courage

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button