ABDUL JALAL PART 1 HAUSA NOVEL

I dedicated this page to you sister like no other
Saddika Adam (baby)
can’t love u less
But stop asking silly questions if not zan hadaki da JALAL lolz
_My first novel_
Aimin afuwa
Today’s page is
Not Edited
Gadan² yanufi inda Jalila take,
Kasa kwakwakwaran motsi Jalila tayi, ta kuramasa ido jira kawai take taga hukuncin daze mata
kawai se ya canza shawara ya koma ya fice daga palourn
Ajiyar zuciya Jalila tayi dataga be mata komai ba
Ilham ta kalli Jalila cike da bacin rai
“Waike Dan Allah meyasa kika fiye shishshigine ina ruwanki da shi wannan fa sabgar family ce meye naki a ciki Yar karere”?
Jalila ta kalleta tai maganar kasa²
“Hmm so hana ganin laifi”
Daddyn Jalal ne yayi gyaran murya yace
“A’a Ilham abinda yayanki yake baya kyautawa abinda takwararsa tafada gaskiyane se dai muyi masa fatan Allah ya shiryeshi”
Wani dam kirjin Ilham yayi takwararsa kuma?
Tai maganar a zuciyar ta
Jalila ta karasa cikin palourn ta durkusa har kasa ta gaishe da daddyn Jalal
Mummy kuwa tuni tabar palourn ranta yana daci game da abubuwan da Jalal yakeyi Sam baya ganin kimarta a matsayinsa na Dan da ta haifa
Fuskarsa a sake ya amsa mata gaisuwar
“Jiya ake gayamin baki da lafiya har an kaiki Asibiti, dazu mummyn su zata je dubaki da safe akace Baku dawo ba,
“Yanzu ya jikin naki”?
” ai naji sauki daddy “
Tayi maganar kanta a kasa
“To dama kiran kenan in miki sannu
Ya gurin mamanki ?”
“Tana nan lafiya”
“Masha Allah kin dawo nan ne gaba daya”?
“A’a zuwa nayi nakusa komawa”
“Allah sarki in kin tashi tafiya kizo muyi sallama kafin kitafi”
“To daddy nagode”
“Yawwa Allah yabaki lafiya”
“Ameen”
Ta amsa
“To daddy seda safe”
“Allah ya tashemu lafiya daddy nagode”
“Ameen Yar albarka
Allah yayi miki Albarka”
“Ameen ta mike ta nufi hanyar fita”
“Daddy dama kasanta ne?”
Ilham tafada tana ya mutsa fuska
“Nasanta Ilham amma tun tana Karama nasan mahaifinta kanin Alhaji Mahmud ne (baban su Jawwad) mutumin kirkine sosai”
Dan tabe baki kawai Ilham tayi
Jalila kam kama hanyar fita tayi
taji an riketa a firgice ta waiwayo taga waye da wannan aikin
Jalal tagani idon Sa Jawur yana wani irin huci
Ya daga hannu ya wanka mata mari, ta gigice tana nema ta fadi, ya dagota yakuma wanka mata wani Marin
Hannu biyu tasa ta dafe fuskarta lokaci guda kuma hawaye na zubowa daga idonta,
“Why meyasa kike son shiga rayuwata?
Ina ruwanki dani?
Sa’anki ne ni ko dankinga ina kyaleki saboda yayanki nake daga miki kafa, amma ki tambayeshi waye ABDULJALAL!!!
ba a shigowa hanyata duk Wanda ya shiga rayuwata se na tabbatar Dana koya masa darasin da har ya mutu baze manta ba,
Kifita daga rayuwata nagaya miki sha³ kawai I hate u!!!”
Yafada yana kuma zazzaro mata ido
“Bazan fita ba, in har bazaka rabu da yayana ba kuma bari in gayamaka baka isa kamin abinda Allah bemin ba”
Ta fizge hannunta tai tafiyarta fuskarta na cigaba da radadi saboda Marin ya shigeta seda tai gaba ta tsaya ta waigo ta kalleshi
“Ka rubuta ka ajiye Marin nan dakayi min seka biya shi kuma na fada Mara tarbiyya, in kaji haushi kadena abinda kake, sannan ka koma makaranta Dan wannan abinda kake ba alamar Ilimi a tare da kai in kaga dama ka yayyankani ka cinye I hate u too,
Tai ficewarta ta tafi Gida, harta shiga gidan, ta tafi dakinsu bata ci karo da kowa ba,
Nana ma bata dakin, dan haka ta dau wayarta da Ilham ta kawo mata dazu
Missed calls din Ummi tagani a ciki dayawa sekuma na kawarta siyama
” Allah sarki Ummi na nayi missing dinki, dole ma inzo in tattara kayana in bar garin nan tsakanin Jiya da yau nayi Dana sanin zuwa kano ga cin zarafin da wannan matar tayimin, ga kuma wannan Azzalumin Dan shaye² da yakeneman illatani
In na tafi bazan sake zuwa kano ba insha Allah gobe zanyiwa Abba magana ni Gida zan koma”
Tai dialing lambar Ummi bugu biyu ta dauka
“Jalila meya faru nake ta kiran wayarki tun jiya da daddare amma baki daga ba?”
Ummi tayi maganar cike da damuwa
“Ummi wayace a silent kuma na manta inda na ajiyeta se dazu na ganta”
“Jalila akwai matsalane? Naji muryarki wani iri, ko baki da lafiya ne?”
“A” a lafiyata kalau mura nake ne”
Badan Ummi ta yarda ba ta bar zancen
“Ya gidan ya yan uwan baki?”
“Kowa lafiya Ummi”
“Ina fatan ba wata Matsala dai ko?”
Matsala kam akwaita very soon ma zan dawo Gida amma a zahiri se cewa tayi
“Eh babu wata matsala amma a satin nan zan dawo Gida insha Allah”
“Kin fasa hutun a nan ne?
” Eh nafasa kewarki ce ta dameni Gida zan dawo “
Ummi ta fuskanci akwai matsala Jalila bata son gaya mata ne.
“To shikenan se da safe ki gaida mutan gidan naku”
“Zasuji insha Allah, mu kwana lafiya kyakykyawar uwa”
“Ameen yar albarka”
Tagama wayar kenan Sega Nana ta shigo
“Yar uwa kin dawo Ashe ? Kiran me akayi miki ince ko lafiya”
“Lafiya kalau, dama babansu Jalal ne yamin ya Jiki, sannan yace ranar dazan tafi inzo,”
“Allah sarki babansu Jalal akwai kirki kaddarace tasa Allah ya hada shi da tantirin da, kodayake yana Dan ganin girman babansa akan mummyn shi”
“To Allah ya shiryeshi in me shiryuwane”
Jalila ta fada tana mikewa domin ta gabatar da sallar isha’i
Bayan sun kwanta Jalila takasa bacci se Juyi take kanta har ciwo yake saboda zafin Marin da ta sha
“NI KIKAYIWA LAIFI YAFIYATA YAKAMATA KINEMA BANI ZANNEMI YAFIYARKI BA KIN SAN GASKIYA AMMA KIN RUFE IDO KINAMIN FADA KECE SILAR KOWACE RAYUWA NAKE A YANZU”
Maganganun Jalal suka dawo mata To me hakan ke nufi lallai akwai wani abu a kasa
Wai meyasa duk lokacin dazan hadu da yarinyar nan se tayi abunda zata konamin rai, seta gayamin maganganun dazasu bata min rai
Meyasa ta kenema ta Shiga rayuwata, ba Wanda ya isa ya tsaya gabana yana gayamin abinda ya gadama,
Ina daga mata kafa ne saboda aminina,
Ire iren wannan tunanin Jalal ya dingayi ga mummy itama ta caza mai kai ransa yagama baci zuciyarsa a cunkushe
Dan haka ya yanke shawarar abinda ze fishsheshi Dan haka ya dau motarsa ya tafi mashaya gurin Jeje.
Jawwad ganin abinda yafaru dazu tsakanin Yaya mairo da Jalal yasan
Jalal fushi yake dashi Dan haka ya yanke shawarar zuwa yabashi hakuri.
Yaje part din Jalal amma bayanan, yashiga cikin gidansu nan ma bayanan
Ya dinga kiransa a waya amma shiru be dauka ba.
Dan haka ya koma Gida har ya kwanta yaji yanaso yasan inda Jalal ya tafi.
Danhaka ya kuma komawa gidansu Jalal don ya duba ko ya dawo,dayake Jawwad yana shiga gidansu Jalal koda yaushene tunda iyakacinsa, part din Jalal be fiye Shiga cikin gidanba se da dalili
Dan haka Jawwad yanazuwa me gadi yake bude masa ya shiga Dan shima Dan gidane.
Har yanzu Jalal be dawo ba
Har had JAWWAD ya juya ze tafi, seyaga kawai so yake yaga Jalal yaji inda ya tafi haka
Jeje kuwa yakara ingiza Jalal ya dinga tuttulawa Jalal giya, se dayaga yayi mankas ba iya komai ya dauko shi yasahi a mota yadawo dasshi gida.
Rungumo Jalal Jeje yayi ya shige dashi part dinsa saboda Sam Jalal baya hayyacinsa tangadi kawai yake
Tunda Jawwad yaji karar motar Jalal yafito kofar part dinsa ya tsaya yana jiran Sa amma seyaga Jeje rungume da Jalal ko ba a gaya masa ba yasan Jalal a bige yake, Jawwad be kulasu ba,
Hanya yabasu Jeje ya wuce da Jalal bedroom dinsa ya kwantar dashi, yazo fita Jawwad yasha gaban Jeje
“Me kabashi?sannan daga ina kuke?”
Yayiwa Jeje tambayar ransa a bace
Jeje ya kalli JAWWAD a wulakance
“Wane irin tambaya ne wannan? Kaima kasan me yasha giya CE meye kuma na tambayata ina mukaje ai kasan inda yake zuwa