ABDUL JALAL PART 1 HAUSA NOVEL

“wannan wane irin shirmen banza ne kawai Ku dauki da Ku kaiwa mutanen da Baku Sani ba to ni ban yaddaba, akan me kawai ni gayamin inane inje in dakko shi”
“Sannu sarkin azarbabi kai ko kara babu, gidan mutanen kirki ne har nan mahaifin yaron yazo ya roki alfarma yanzu yasakasu a islamiyya daya”
Inna mairo ce take wannan jawabin
“Au saboda wulakanci had da canza masa makaranta haka akeyi kaikuma kana zaune”
Seda aka gaya masa gidansu yaron yana gadon kaya Yakama hanya ya tafi dakko JAWWAD,
yana zuwa ya tarar an shiryasu me gidan ze fita da su Jawwad da wani yaro da befi sa’an jawwad ba
Da gudu Jawwad ya tafi ya rungume Aliyu ganin haka yasa shima Yaron ya tafi ya rungume Aliyu, ya rungume su gaba daya
Suka gaisa da mutumin
Aliyu Yace masa
“Dana Nazo dauka”
“Wanne kenan?”
Mutumin ya tambayeshi
“Jawwad mana”
“To ai har gida na tura aka dakko shi da izinin mahaifinsa”
“To ai nine babansa tafiya nayi ne kuma na dawo abani Dana ban yadda ya dinga zuwa wani guri yana zama ba”
Yayi maganar yana janyo hannun Jawwad aikuwa Jalal ya fashe da kuka ya bisu yana “daddy kace ya dawo min da shi”
Aliyu ba yadda beyi ba adena kai Jawwad gidansu jalal amma abu yaki,
Inma ba akai Jawwad ba za akawo JALAL sekace tagwaye
A yan kwanakin da Aliyu yayi a kano Dan uwansa ya fuskanci akwai abunda yake damunsa saboda Sam baya walwala sosai
Usman ne yaje ya sameshi adaki yana waya da marry ya jirashi ya gama sannan ya mai tambayar
“Dan uwana me yake damunka ne naga Sam Baka da walwala ko akwai wata damuwa ne”?
” akwai kam yayana”
“Me yafaru?”
Usman ya fada yana kallonsa
Be boye masa komai ba ya gaya masa halin dayake ciki
Jinjina kai yayi
“Gaskiya Dan uwa ka debo da zafi shawarar da zan Baka ka hakura bana tunanin abin nan ze yiwu kasamu wata anaan ka aura”
” a lokacin da ka dakko naka Auren waya hanaka, kamin addu a kawai bana son wanna shawarar taka , tashi kabani guri'”
Aliyu ya fada yana nuna masa hanyar fita
Satinsa daya a kano ya koma kogi state an kai ruwa rana sosai a gidansu marry da aka gano tana soyayya da musulmi kuma bahaushe
Kwanci tashi Aliyu ya kammala service dinsa
Dayazo da maganar auren marry Gida malam yace be yadda ba, ga yayan musulmi nan a garin nan dan haka ya hakura da maganar yarinyar nan.
Marry kuwa taita rashin lafiya saboda Aliyu ya tafi ga kuma anki yadda da ya aureta, mamanta ta dena kulata sarki yayi fushi da ita duk da soyayar da yake mata, ita kuma ta kafe tace ita se Aliyu
Shima nan haka Aliyu yake ta fama da malam amma yaki yadda, inna mairo CE kawai ta goyi bayansa amma malam ya kafe yace be yadda ba sedai ya auri musulma
Da wannan rikicin seda aka shafe shekara biyu ana fafa tawa da wannan rikicin
Marry taje ta samu maman ta tace itafa gaskiya zata tafi kano gurin Aliyu shi takeso bazata iya zama a garin nan ba
A gigice Maman ta taje tasamu sarki ta gaya masa, juyin duniya marry ta kafe tace itafa gaskiya tunda bazasu yadda ba tafiya zatayi,
Dan haka sarki yace to ya sallameta basu ba ita har abada karta kara dawowa, marry tace ta yadda,
Tana kuka mamanta na kuka haka ta hada kayanta ta nufo kano………
Bayan la’asar marry ta sauka a kano layin Aliyu ta shiga kira bugu biyu ya dauka
“Aliyu kana ina ne?”
ta tambayeshi
“Ina gida”
Yabata amsa
“Kazo ka tafi dani Dan Allah”
“Ahh wai kina ina ne?”
“Aliyu kazo ka daukeni ina kano fa yanzu na karaso”
Zaro ido yayi
“Are u serious?”
“Dagaske nake”
A kidime ya tashi ze fita sukayi karo da Usman
“Dan uwa ina zaka, naganka a kidime haka”
“Dan uwa marry ce ta biyoni kano”
“What are u serious”
” yanzu mukayi waya da ita ta fadamin”
“Muje tare”
Usman ya fada yana Jan hannunsa suka fice
Kaman yadda ta fadamasa a tasha sukaje suka sameta rungume da akwatinta
Haka suka Dakkota suka taho gida
Suna zuwa Zainab ta karewa marry kallo
“Wannan fa daga ina”?
Tafada a yatsine saboda ta ganta tare da Usman ga kuma uban akwati
” bakuwace”
Shine kawai abinda Usman yace mata suka wuce bangaren inna mairo
Lokacin ana ta kiraye² sallar magariba dan haka suka kaita dakin inna mairo suka tafi masallaci
Bayan inna ta idar da salla ne tare da lazimi
Ta kalli marry tace mata
“Sannu da zuwa”
“Yawwa mama ina wuni”
Tafada da hausa amma a hausan tata zaka fuskanci ba cikkakiyar ba haushiya ce ba
“Lafiya kalau, amma banganeki ba “
Dan sunkuyar da kai tayi
“Tare muke da Aliyu”
Nan inna mairo ta gane wace ce
Tabata Abinci da ruwa tabata guri ta huta
Se bayan sallar isha’i sannan su Aliyu suka dawo gidan a dakin inna mairo suka hadu suna jiran zuwan malam Imam suji me ze yanke,
Zainab se sintiri take so take taji wace wannan bakuwar dasuka zo da Usman da Aliyu harda su trolley ita dai bata san taba
Akajima se ga malam imam ya dawo yazo ya samesu a zaune jungun² a dakin inna mairo
“Ya akayine na ganku a zaune kunyi shiru, bakuwa mukayine”
Inna mairo ce ta shiga korawa mamalam imam bayani
Ransa ne yayi matukar baci da jin inda jawabin NATA ya dosa, ya tashi ya bar gidan gaba daya
Seda yayi kwana biyu baya shiga harkarsu
Zainab kam ta uzzurawa Usman setaji wace ce yarinyar nan amma yaki gaya mata
A kwana na uku
Aliyu ne yasamu malam a tsakar gida yaje gabansa ya durkusa
“Baba na dama akwai lokacin da zezo kayi fushi dani haka kadena kulani Aliyun ka nefa dan autanka
Kasan bantaba dakko maka magana ba meyasa bazaka yadda da niba”
“Ya raina baze baci ba, seda na jamaka kunne akan yarinyar nan, amma saboda baka jin maganata kaje ka ja jubota ka kawomin ita gida haba Aliyu yaushe kafara dena jin maganata”?
Marry tanajin abinda ya faru a hankali ta tako ta karaso gaban malam imam ta zube
“Baba ba laifin Aliyu bane ni na kawo kaina dan girman Allah karka koreni, kafison in koma inda na baro kan addinina na baya?
Baba kaifa malamine kuma ubane dan Allah baba musulunta zanyi, ka auramin Aliyu idan na bar nan bazan koma gida ba wani gurin zanyi in ka koreni bansan inda zani ba,”
Duk wannan maganar da take cikin kuka takeyi
Aliyu ma gaban malam ya durkusa ya rike hannunsa
“dan Allah baba na ka amsa mana ka yadda in auri maryam dan Allah baba inba ita na aura ba wallahi bazan iya auren wata mace ba”
Usman ma gaban malam yaje
” baban mu tun tasowarmu kake sonmu kake kula damu, kake son abinda mukeso, baba ka amince da bukatar dan uwana,
Baba ka girmama son da maryam da Dan uwana kema junansu Wanda yasa ta baro daular da take ciki ta taho gurin mu, inka yadda da auren nan kaman kayi jihadi ne”
Inna mairo ma cewa take
“Malam a duba lamarin nan d’a na kowa ne mukanmu misaline munzo garin nan. Bamu da kowa”
Ajiyar zuciya yayi ya nisa sannan yace……..
Share please
More comments more typing……………..
Mss~dyjeer naga rago godiya nake????
Anty Jamila a soye tabani ta hutaddani suya
Afshan
Rahmatoulaye
Salma
Afshan
Fatima zahrahs (tsofaffi)
And the remaining members
Ina alfahari daku ❤❤❤❤❤
????️????️????️????️????️
[8/31, 8:26 AM] Safiyya: ????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????
_ABDUL JALAL_
(2020)
_WRITTEN BY AISHA HUMAIRA_
(Daddy's girl)
PAGE- 10
PART 1
_Bismillahir Rahmanir Rahim, da sunan Allah me Rahma me jin kai, Allah ka yi salati a bisa shugaban mu Annabi Muhammad (salallahu alaihi wassalam)
Bayan haka, ban rubuta wannan littafi domin cin zarafin wani ko wata ba, na yi shine domin nishadantarwa, da kuma wa’azantarwa, ku biyoni domin jin me wannan labarin ya kunsa.
Yanda nafara Allah yabani ikon kammala shi