ABDUL JALAL PART 1 HAUSA NOVEL

Jawwad ne ya dawo daga makaranta ya gaji matuka kaya wanka yayi yai salla ya tafi gurin Rabin ran nasa wato Jalal
“Dan uwa ka dawo daga makarantar kenan sannu da zuwa”
“Yawwa bros Sannu da hutawa”
Jawwad yafada yana Neman gurin zama
“Nagaji sosai Jalal,”
“Nagani a idonka ai yau kukayi tests din ko?”
” eh yaune Alhamdilillah test din duk se godiyar Allah sunyi sauki sosai kuma hada jajircewar ka da addu’arka proud of you dan uwana rabin jiki”
“Kajika kaifa kake karatunka bani nake maka ba wannan kan naka akwai ja mutumina i wish nike da kwanyarka”
“Amma fa ka zageni Jalal, kasan ban isa inyi karatun dakayi a bayaba in kana waje wayake Neman irinmu, Jalal wai yaushe zaka koma makaranta ne kai?”
“Zan koma amma ba yanzuba, bana son wannan zancen zomuje muci abinci”
“A ina kuma ga abinci can a Gida zuwa nayi muje mu ci”
“koma inane muje daganan kasha ice cream ka dan huta, ka huce wannan gajiyar “
“Kaikake koyamin kwadayi fa”
Dariya sukayi gaba daya
“Kasan wani abu Jawwad?”
“A’a seka fada?
” wallahi wata mayyace take uzzurawa rayuwata gashi tayi hiding number balle insata a black list, kullum seta kirani kota turomin messages ni na rasa yadda zanyi, wallahi na gane wacece setayi Dana sanin wannan gangancin da take min”
Dariya sosai Jawwad yayi
“To kai meye abun damuwa aciki, dan ance ana sonka”?
“Mtseww kai kafiya shirme Jawwad ni bani da lokacin wannan shirmen, inyi rayuwata ni kadai ya fiyemin, duk yayinda ka gayyoto mata cikin rayuwarka kamar ka gayyatowa kanka matsalane”
Dariya Jawwad ya dingayiwa JALAL seda Jalal yafara jin haushi sannan ya dena
“Jalal wayagaya maka mata matsalane, mata ni’ima ne, tabbas akwai daga cikinsu masu matsala, amma akwai na kirki sosai, soyayya akwai dadi mussaman in kayi dace da mosoyi na kwarai, bazaka gane hakan ba seka fada tarkon soyayya”
“Hmm mata duk matsalane indai irinsu Ilham ne duk matsalane”
“Hmm bazaka gane ba Jalal”
“Eh naji bazan ganeba”
“Lokaci ze ganar da kai ai”
“Eh naji mutafi”
Jeje ne yakira Jalal yana son su hadu Jalal
Shikuma yace masa ya fita shida Jawwad bazeyiwu su hadu yanzu ba
Gurin cin abinci suka tafi shida Jawwad
Bayan sungama cin abinci ne suna hira aka kira Jawwad lambar Ummi yagani ya kara nutsuwa ya dau wayar
“Salamau alaikum Ummi barka da rana”
“Yawwa barka Jawwad ya kake ya mutan gidan”
“Kowa lafiya Ummi ya Jalila”
“To lafiya kalau za a ce meyasamu lambar abbanku nakira bata shiga”
“Inaga inda yake ne ba network, amma lafiya Ummi”
Ajiyar zuciya Ummi tayi ta kwashe kaf abunda yafaru tagayawa Jawwad
“Yasalam Ummi kiyi hakuri insha Allah komai zezo da sauki, yanzu bana Gida idan na koma zanwa Abban bayani insha Allah, kiyi hakuri Ummi dan Allah kinsan har yanzu yarinya ce”
“Ba batun yarinta Jawwad tsabar rashin hankaline kawai
” adai yi hakuri Ummi “
Haka dai sukayi sallama Jawwad ya dafe kai
“Ohhh my God sisy ba dai rigima ba”
“Ya dai meyafarune?”
Jalal ya tambayeshi, Jawwad ya kwashe komai ya gayawa Jalal,
Dariya Jalal ya dinga yi kaman wani tababbe
“Kan bala’i wannan yarinyar Yar bala’ice wallahi, kaga zancena ko Jawwad, nagaya maka mata matsalane, mussaman irin wannan kanwar taka zama da ita seda panadol”
“Hmm haba Jalal kaima kanwarka ce, Jalila bata son raini bata yadda da wulakanci ba nidai fatana Allah yasa kar baban yarinyar yayi mata wani abu”
Wata dariyar Jalal yakumayi
“Kamar ya kar yayi mata wani abu “yarsa fa ta Daka, aigara suko yamata hankali yadda gobe bazata kuma ba,”
Yayi maganar yana dariya
“Haba Jalal Yar gidan Abee ce fa, in duniya da gaskiya bekamata kace haka ba”
“Hakane Jawwad kaima kace wani abu amma kasani bataji, in mutum yana rashin kunya in besamu dai² da shiba baze dena ba
“Wow tauraro a cikin taurari kaina mussaman ne ban taba tunanin kana dariya haka ba, bakaga yadda dariya kemaka kyauba”
Gaba daya suka waiga domin ganin me maganar Hannah ce budurwar dasuka hadu da ita wancan karon, tayi maganar tana karasowa inda suke guri tanema ta zauna
“Jarumin maza meyabaka nishadi kake wannan dariyar haka ka fi ko yaushe kyau ko dan uwan ne yake baka nishadi”
Ta karasa maganar tana kallon Jawwad
“Uban wa yace kizo inda nake, me kike Nema a gurina ne kin uzzuramin kindami rayuwata meye hakane, waima wayagaya miki ina nan da kike bina”?
Wani kasaitaccen murmushi Hannah tayi
“Call me by my name Hannah, or any special name u choose,
Kasan ita zuciyoyin masoya kaman wireless ne, our hearts and souls are always connected, dan hakazuciyarkace tagayawa tawa zuciyar kana nan shiyasa nazo kuma nayi sa’a nasameka zuciyarka kawai nake bukata Jalal, in har kabani zaka huta da nacina, akasin haka kuwa zan cigaba da hanaka sukuni cikin dare ko rana har sekabani abunda nakeso”
Wani wulakan taccen kallo Jalal yai mata ya watsar da ita bece mata komai ba
Jawwad ne ya danyi gyaran murya
“Kinaji Hannah already Jalal akwai wadda takeson Sa kanwarsa ce kuma kinga…..
Dagawa Jawwad hannu Hannah tayi
” haba dan uwan masoyina meye laifina anan dan ina kokarin cikawa zuciyata burinta, kowa iya allonsa ya wanke, tayi nata kokarin nima inyi nawa wadda tai galaba ta kafa soyayyarta a zuciyarasa shikenan, ni Hanna babu macen data isa tayi takara dani akan soyayya,
Jawwad son danakewa dan uwanka ko matansa hudu sena kori biyu ya aureni saboda space din daya yamin kadan,
Kar ace rashin adalcin nawa yayi yawane da se ince seya kori kowa ya aureni saboda shidin nawane ni kadai”
Saroro Jawwad yayi yana kallonta
“In kagama jin tatsuniyar kazo mutafi inada abunyi” Jalal yafada yana mikewa
Hanna ma mikewa tayi tazo gabansa kaman zata shige jikinsa se wani irin fitinannen kamshi take
“Babyna kabani dama ko sau dayane in gwada maka yadda nake sonka mana, kuskurewa bukatata shizesa incigaba da uzzura maka har gidanku nasani zaka iya ganina a kowani lokaci, karkayi mamaki nasanka farin Sani a yadda kake a haka nake sonka, zan iya komai akanka, kagayawa kanwarka ta janye kudirinta na sonka ta barmin kai in bahakaba”
Ta kashe masa ido daya daga nan tai tafiyarta,p babban abunda yabawa Jalal mamaki dayakasa yimata komai
Jawwad ne ya janyo hannunsa suka hau motarsu suka nufi Gida
“Jawwad ka yadda mata matsalane, abunda zuciyarsu ta raya musu kawai shi sukeyi, yanzu ga haukan da wannan tayi min, amma zan dau mataki akai”
“Kabi komai a hankali Jalal, kasan in mutum yana kan ganiyar so makancewa yake so ba karyane ba, ka dena wulakanta Wanda yace yana sonka kai baka san a ya zaka fara taka soyayya ba,
Amma wannan Hannah ka nemi tsari da sharrinta because Dana kalli cikin idonta ya tabbatar da she mean what she said”
Haka suka cigaba tattaunawa har suka iso gida
Bayan sallar isha’i Jawwad yaje part din Abba ya tarar dashi shi ka dai, yagaya masa abunda ya faru jinjina kai Abba yayi
“Hmm Jalila iya rigima, halin mahaifinta ta dakko bata son raini Allah ya kaimu goben, zan San yadda za ayi”
Da asuba Abba ya taho kano be gayawa maama abunda ya faruba ya dai cemata zeyi fitar asuba zashi wani guri
Still wannan Daren ma messages din Hannah suka dinga shigowa wayarsa seda yagaji ya kashe wayar
Washe gari da safe Jalila ta shirya ta tafi makaranta, Daren ranar addu a ta kwana tanayi
Ba wai Allah ya sassauta fitinar da ta dakko ba, se dai Allah yasa kar Ummi ta korata kano
A hanyar makaranta ta hadu da yayan lubabatu data tsokana ranar akayi Sa a ya ganeta, ta Ganshi sarai amma taki guduwa tacigaba da tafiya a hankali,
Zuwa yayi ya sha gabanta
“Ke karamar Mara mutunci ni kika zaga ranan ko waike Yar iska”
“Wallahi kasake ka tabani sena tara maka jama’a nace zaka lalata ni shekara goma sha hudu ce zakayi a gidan yari bayawa”
“Au tunaninki barazanar ki zata hanani in casaki senaga uban da ya tsaya miki”
“Bari kaji in gaya maka idan kana shan kwayarka tagaya maka karya kayiwa mutane hauka, to karkayi gangancin gwada kwayarka akaina,
Dan wallahi sena kulla maka sharrin dazaka kare rayuwarka a prison”
Kafin kace meye wannan Jalila ta ware murya ta fara ihu iya karfinta hankalin jama’a ne yafara dawowa Kansu ana fara taruwa ta silale ta gudu ta nufi makaranta
Abunda yasa ta guduma gudun kar takuma shiga wata cakwakiyar bata fita daga wadda take ciki ba ga Ummi tace zata maida ita gidan su Jawwad da setasaka anmasa duka
Tana zuwa ajinsu ta tafi taje gurin zamanta ta hakimce ba tareda ta kula kowaba, “Allah ya biya Queen J Dama tunda yarinyar nan tazo kanta yake hayaki, se wani takama take, malamai ma kaman wani tsoronta sukeji segashi kinyi maganinta”
Haka dai seatmates dinta suka dinga zigata ita dai Jalila hankalinta yana kan batun Ummi
Bayan anfita break an dawo ba dadewa Hanan ta shigo ajin tana kallon kowa a wulakance ga malami a ajin amma Hanan batabi takan malamin ba ta tako
Tazo gaban Jalila
“Sannu uwar rashin kunya, dama na miki alkawarin kawo karshen rashin kunyarki,
Yau zakigane kin taba Yar gidan bullet kizo office bullet yazo da kansa”
“Amma kin bani kunya da kikazo da bullet kawai, ai na dauka barikin zaki dakko gaba daya su taho da egwa yadda in sun markadeni baza ageneniba dan dai bullet, ai bullet yayi kadan aga bayana dashi”
Jalila takarasa maganar hade da tsaki”nonsense “
Mikewa Jalila tayi tai gaba ta wuce hanan
Wato Jalila Yar bala’ice babu alamar risina a tare da ita tun tasowar Hanan take taka Wanda taga dama take jefa tsoro a zukatan duk Wanda yai kuskuren shiga hanyarta saboda takamar ubanta wani ne amma yau ta hadu da wadda tafita rashin mutunci
Haka ta bi bayan Jalila suna zuwa harabar ofishin director Jalila sukayi clashing da malama ramatu aikuwa Jalila ta tsaya
“Ita wutar munafiki ko tana karkashin jahannama ne,
Kekam baki dace da malamar makaranta me bada tarbiyya ba kema kina bukatar me baki”
Jalila ta gayawa malama ramatu sannan tai gaba abinta