Uncategorized

ABDUL JALAL PART 1 HAUSA NOVEL

Tana shiga office din director ta tarar da mutane ba Wanda ta kula kuma bata kalli suwaye a ciki ba ta shige

Share please
More comments more typing………….

????️????️????️????️????️
[8/31, 8:26 AM] Safiyya: ????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????

_ABDUL  JALAL_
       (2020)

  _WRITTEN BY AISHA HUMAIRA_
(Daddy's girl)

           PAGE-  20&21

PART 1

_Bismillahir Rahmanir Rahim, da sunan Allah me Rahma me jin kai, Allah ka yi salati a bisa shugaban mu Annabi Muhammad (salallahu alaihi wassalam)
Bayan haka, ban rubuta wannan littafi domin cin zarafin wani ko wata ba, na yi shine domin nishadantarwa, da kuma wa’azantarwa, ku biyoni domin jin me wannan labarin ya kunsa.
Yanda nafara Allah yabani ikon kammala shi

Ina maraba da shawarwari, sharhi, ko kuma gyara, nagode.

Domin Samun karanta wannan littafin yi magana ta what’s app akan wannan lambar

07063065680
Kokuma addanna wannan link din domin samun novel din

????https://chat.whatsapp.com/EtB4KI52K0v5FQc2ELhidL

I want comments not stickers or just thanks????????????????
Your comments give me courage

    -My First Novel-

“Meyasa kikace kar ya sha”
“Nidai kawai kahana shi sha kar ya sha tea din nan”
Jawwad ji yayi gaba daya ta firgice masa
“Amma meyasa kikace kar ya sha?”
Sekuma tarasa mezata ce masa
“Am…emm.. Idan ya sha ze iya yin amai gara kaimasa tofi na ayoyin Qurani ya sha kafin kabashi abinci in Bahaka ba, ze iya bashi matsala eh..m.. In…nima malaminmu ne yafada mana a Islamiyya”
Da Jawwad yaji haka da sauri yasa hannu ya karbi cup din tea
Daga hannun Jalal
Jalal ne ya kalleshi
“Meye haka kuma?”
“Kanwarka tace karka sha tukuna, Dan huta ina zuwa”
“Kaga ni bani yunwa fa nakeji yaushe zan tsaya biye maka yarinya Karama tana juya ka”
ya yunkura ze karbi cup din tea daga hannun Jawwad yaji kansa ya kara nauyi dan haka ya koma ya zauna yana jujjuya kan
“Sannu bros”
Jinjina kai kawai Jalal yayi
Kamar yadda Jalila ta gayawa Jawwad yaje fridge ya dakko ruwa ya karanta ayoyin Qurani ya busa masa a ruwan yazo ya tsiyayo a cup ya bashi
Hannu yasa ya karba ya shanye ya ajiye kofin, ko minti biyar beyi da shan ruwan ba ya mike ya tafi bandaki ya dinga wani irin bakin amai
Jawwad ne ya bishi yana masa sannu ya kwashi mintuna yana amayar da wani bakin abu
Seda Jawwad ya Dan tsorata

“Jalal mutafi Asibiti your condition is getting worst jin ciwon nan nake kaman a jikina”
Ture Jawwad yayi ya tafi ya kwanta gaba daya jikinsa ya mutu ga wani mugun Jiri dayakeyi
Jawwad ya biyo bayansa, Dan kura masa ido yayi yaga jijiyoyin kan Jalal duk sun mike fuskarsa tayi Ja
Gefen gadon ya zo ya zauna yasa hannunsa akan Jalal yana masa karatun Qurani a hankali
Wani baccin wahala ne ya kuma awon gaba da Jalal abun mamaki a cikin baccinsa ya dinga Jin sautin karatun Jalila Wanda ya dinga jin nutsuwa tana saukar masa

Jawwad ne ya mike ya nufi gida don tafiya masallaci lokacin salla la’asar yafara gabatowa
Cikin Gida ya shiga ya tarar da Nana tana video game maama kuma ta Dan kwanta a akan kujera tana kallon Nana
Sallama yayi suka amsa gaba daya
“Maama sannu da Gida”
“Yawwa ya jikin Jalal din”?
“Da sauki maama”
“Allah ya sawwake”
“Ameen”
Ya amsa
“Nana babu abunda kika iya se shirme,
Jalila tana can tayi abun arziki ke kam shirirtarki ta fiye miki”
Attention dinta gaba daya Nana ta bashi
“Allah Yaya me Jalilan tayi”
“Gasar karatun Qurani sukaje abuja jiya, tazo na biyu, amma se rikici takewa Ummi wai ita na daya take so”
“Dan Allah Yaya dagaske amma naji dadi, ga fitina ga kwanya Allah sarki Jalila Allah yakara hasken makaranta”
“Ameen kema se ki dage kidena wannan shirmen”
Duk abun nan maama bata ce uffan ba
“Amma shine ko ta gayamin amma kai ta gaya maka dani take zancen”
Nana tafada tana Dan bata rai
“Aini kullum se munyi waya da ita”
“Ai Yaya dole muje Kaduna we have to celebrate the victory of my great sister bari Abba ya dawo”
Nana tai maganar tana murmushi
“Karki fara, kwata² yaushe ta bar gidan nan kike zancen, wani zakuje to babu inda zaku, nasake naji kin tambayi abbanku zakije sena bata miki rai sha³ kawai,
Kaikuma naga zakewarka akan yarinyar nan yafara yawa ka kiyayeni Jawwad in bahakaba daga kai har ita senaci mutuncinku,”
Maama ce tayi wannan maganar cikin fada da fushi gaba daya suka bita da kallo
Ajiyar zuciya Jawwad yayi ya dan girgiza kai
“Allah yabaki hakuri ya huci zuciyarki za a kiyaye insha Allah”
Ya Fita yabar parlour itakuwa Nana zunbura baki tayi itama ta barwa maama parlour
“Lallai in ban dageba maganar Yaya mairo na shirin zama gaskiya zakuci kaniyarku sena raba Ku da yarinyar nan”

Se bayan magariba Jalal ya kuma ta shi wannan karon seya jishi sakayau babu ciwon kan se rashin kwarin jiki
Wanka yaje yayi ya rama wasu daga cikin sallolin dabe ba ya bar wasu Jeje ya kira a waya yaji yana ina yagaya masa
Kaya ya canza ya dauki motarsa ya bar gidan kai tsaye club din da yake haduwa da Jeje ya tafi kamar kullum yauma club din cike yake da “ya’yan da suka rasa mafadi maza da mata kowa na sharholiyarsa matan nan wasu sunyi shiga half nicked wasu na rawa yayinda wasu suka kama daki suna shagalinsu
Jeje naganinsa ya washe baki yana masa sannu da zuwa gaisawa sukayi Jalal yasamu guri ya zauna Jeje ya tafi kawo masa mutuniyar tasa wato giya
Duk gigin matan gurin nan basa zuwa inda Jalal yake saboda sun San halinsa basa gabansa shidai ze sha giya yayi mankas amma be yadda yayi zina ba
Jeje ne yasamu guri ya kira Hanna
” kina ina ne?”
“Ina Gida mana”
Hanna taba shi amsa
“Muna tare da mutuminki fa yanzu haka”
“Dan Allah dagaske dazu Dana kirashi abokinsa yace min bashi da lafiya”
“Ke dalla rabu da wannan sakaran kilma karya yakeyi”
“I wish in samu dama in fito yanzu inzo in ganshi”
“Ke rufamin asiri yanzu ma abu zan karbo masa ke dai kicigaba da kokari”
“Karka damu kaman yazo hannuna ya gama ne”
“That’s good seda safe”
Sukayi sallama da jeje ya tafi bar domin karbo giya
Bayan ya karbo ne yazo ya nemi guri ya zauna ya Tarar da Jalal yanata salansa yana bawa sama hayaki tabarsa kawai yake sha
Jeje ne ya tsiyayawa Jalal giya a cup ya tura masa gabansa
Wayar Jalal ce ta fara ringing ya Dakota seyaga unknown number seyaki dagawa ya cigaba da abunda yake haka wayar taita ringing
“Maza wayarka fa ake kira”
Sedayaja wasu seconds sannan yabawa Jeje amsa
“Nagani”
Dan tabe baki Jeje yayi yacigaba da shan giyarsa
Messages ne suka dinga shigowa wayarsa
Tsaki yayi ya dau wayar yafara duba messages din
“Haba fitilar rayuwata meyasa zakamin rowa, just want hear your sweet voice
I really care for u, bazan iya bacci ba in banji muryarka ba love u baby
From your lovely bae”

Ire² wannan messages dinne ake ta turomasa tsaki yayi sannan ya danyi shiru yana zancen zuci anya kuwa Ilham ce take turo masa wannan messages din, wacece ta kira dazu sukayi waya da Jawwad?
Ya tambayi kansa still wayar ce tafara ringing da Sauri Jalal ya yinkurin dagawa domin yiwa ko wacece rashin mutunci seyaga Jawwad ne yake kiransa dan zaro ido yayi sannan ya daga wayar
“Jalal kana ina?”
Jawwad ya tambayeshi
“Na dan fitane”
“Hmmm daga samun saukinka harka fita ko ka tafi gurin Wanda sukafi kowa mutumci a idonka shikenan seda safe”
Jawwad ya katse kiran mikewa Jalal yayi yadauki mukullan motarsa ze fice
Jeje ya kalleshi
“Ya dai ba dai tafiya zakayi ba?”
“Tafiya zanyi mana dama bana jin dadi Jawwad yaje bana nan naji ransa a bace dole in tafi inje ba shi hakuri”
Wani bakin cikine ya tokarewa jeje ji yayi kamar ya rufe Jalal da duka,
Yadda Jalal baya son bacin ran Jawwad da iyayensa yakewa haka da ya dace
Anya ba asiri Jawwad yayiwa Jalal ba jeje yayi maganar a zuciyarsa
Shikam Jalal besan yanayi ba dan tuni ya bar gurin

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button