Uncategorized

ABDUL JALAL PART 1 HAUSA NOVEL

Yamma nayi Jalila ta shirya ta dau kudin safa da Jakarta tayi waje
Kai tsaye inda ake fadan gidan sojan nan ta nufa daga waje ta karewa gidan kallo
Aranta take fadin gaskiya gidan nan ya hadu saura kuma inshiga inga meye a ciki yadda ya hadu daga wajen nan cikin kuma ai nasan yafi haduwa
Daga nan ta mika ta nufi inda zata sayi jaka amma seta hango wani kanti da sojoji a bakin gurin dan haka ta yanke shawarar zuwa taga meye akeyi a gurin
Kai tsaye ta kutsa cikin kantin wani soja ne ya daka mata tsawa yace ta tsaya a waje se sungama sun tafi tukuna
“Dan Allah kabari abu zan siya kawai in tafi ni ba gurinka nazo ba “
Zekuma magana wani sojan yace ya batta ta shiga
Tana shiga taga wani babban mutum a zaune akan kujera fuskar nan tashi murtuk babu annuri
“Ina wuni”
Jalila ta gaisheshi be amsa ba
“Baba gaisheka fa nake nace ina wuni”
Dan juyowa yayi ya kalleta ya danyi murmushi jin takirashi da baba
“Lafiya kalau sannu yan mata”
“Yawwa”
Ta sai chocolate dinta ta mutumin nan yace abawa Jalila shize biya
Seda ta risina sannan tace
“Baba nagode sosai”
“Bakomai adinga shan chocolate din a hankali yana kashe hakori”
Murmushi Jalila tayi ta fito “aikin banza na daukama wani abun ake a gurin to me sojoji suke anan ko gadinwa suke oho”
Ta siyo Jakarta ta fito dayake kusa da kantin ake saida jakunkuna
ta hangi mutumin dazu ya fito daga kantin nan ze shiga mota se ya yadda wallet dinsa da sauri ta je ta dauka, amma tuni sunyi nisa sun bar gurin sun nufi layin gidan wannan sojan
Ta dinga jujjuya wallet din nan kawai ta tafi Gida da wallet din
Bata nunawa Ummi ba ta boye wallet din
Ta faki idon Ummi taje ta dau wallet din ta bude kudin kasar wajene a ciki da ID card bata tsaya bin ta ID card dinba ta aje wallet din cikin sabuwar jakar makarantar ta cikin litattafanta

Washe gari Ummi ta tursasata ta shirya ta tafi makaranta, ta wannan layindai na gidan nan Jalila tabi dan takuma ganin gidan nan kuma ko Allah zesa taga mutumin nan
Tanata kallon gidan wani soja ya kalleta
“Ke me kike kallo wuce ki tafi makarantar ki”
Ya mutsa fuska Jalila tayi
“Ina ruwanka da makaranta ta?kallo kawai zanyi in tafi”
“Ba a son yawan ganin mutane a arear gurin nan saboda tsaro dan haka wuce ki tafi”
“Did I look like criminal, da uniform dina na makaranta balle kace wani abun zanyi, sekace gidan shugaban kasa naga dai gidan mutum ne ba aljan ba in me gidan yasan bayaso a dinga wucewa ta hanyar gidan ai da seyaje duniyar wata ya Gina gidan ba duniyar mutane ba”
“Kut wace irin yarinya ce wannan?”
Aikuwa sojan nan beyi wata² ba ya zare beilt da nufin ya koya mata hankali se su kaga wasu motoci suna shigowa Latin manyan motoci ne glasses din duk tint ne mutumin jiya da ya sai mata chocolate ne ya fito daga daya daga cikin motocin
Wannan sojan da ya zare belt ne ya kame yana saramasa da ido yai masa magana sojan ya tsaya
“Laa baba ina kwana”
Jalila ta tsuguna tana gaisheshi “lafiya kalau Yar baba, meyahada ki da wannan”
Ya nuna mata sojan nan da ya biyota
Bata boye masa komaiba ta gayamasa murmushi yayi a ransa yace lallai wannan yarinyar Yar rigima ce amma a fili yace
“Yar baba yanzu kin makara ki tafi makarantarki rabu da shi
Kai baka ganin Yar makaranta ce kawai daga kallon Gida se a ce za a bigeta ina nema mata afuwa”
Jalila tasaka hannun a Jakarta ta dakko wallet din nan ta mika masa
“Jiya ka yaddashi bayan kafito daga kantin nan”
Hannu yasa ya karba tasan ce kuwa yana ta dubawa tun jiya be ganta ba yayi zaton yayi miss placing dinta ne
Murmushi yayi “nagode sosai Yar baba Allah ya albarkaci rayuwarki “
“Ameen nagode”
Ta juya ta tafi hanyar makarantar su ta makara sosai amma taci sa’a ba malami a ajinsu dan haka ta shige tanufi ajinsu
Class dinsu ne ya kaure da hayaniya ga Queen ta dawo nickname dinta kenan a makarantar boko Queen J
Kai tsaye bayan sungama murnar ganin juna da yan ajinsu gurin zamanta ta nufa amma me setaga wata hakima ta hakimce mata a seat Jalila dai bata Santa a ajinsu ba maybe newcomer ce dan haka Jalila tace
“Sannu dai excuse me gurin zama nane ina bukatar zan zauna”
Banza yarinyar tayiwa Jalila
“Ko kurma ce ne? Nace kifito nan gurin Jalila ne fada tace”
“Wallahi mun gaya mata har malamai sun San nan gurinkine amma tace ita kuma dole anan zata zauna”
Cewar wata daliba
Ita kuwa sabuwar zuwan nan bata da niyyar magana balle Jalila tasa ran zata tashi sema wani kashingida tayi ta kurawa Jalila ido tana hura hanci tana kallon Jalila up and down
“Ke yau kome kikeji zan sauke miki shi yau koda uban me kike yawo wallahi sekin bar seat din nan uwarkice ni a rashin mutunci”
Dariya yarinyar tayi “ok yi abinda zaki iya nikuma na miki alkawarin kawo karshen rashin kunyarki a yau base gobe ba”
“Queen J dan Allah kiyi hakuri ki kyaleta babanta fa babban sojane ranar Monday aka kawota”
Wata dalibar tai maganar tana kokarin Jan hannun Jalila
dukan benci Jalila tayi
“Wallahi ko Yar gidan bullet ce, ke Allah yasa baban tane AK47 wallahi seta tashi this is my kingdom, in ubanta ya tsaya mata ni Allah ya tsayamin, Kafin kiyi maganina ni zan fara maganin wannan izzar taki, ko kina wa kowa hauka ba ayiwa Jalila”
Hannu biyu Jalila tasaka ta fizgo yarinyar nan daga cikin benci aikuwa yarinyar nan ta wankawa Jalila mari,
Wasu daga cikin dalibai suka tafi kirawo malamai domin raba fadan nan
Amma tuni Jalila ta rama marin nan ta kara mata wani, Jalila ta dage ta hankada yarinyar nan kan bencina nan take goshinta ya fashe jini yashiga fita

Share please
More comments more typing…….

Proud of you my fans INA jin dadin adduoinku nagode kwarai Allah yabar kauna
❤❤❤❤❤
Team JALILA kunga abinda yau ta dakko to ni ba ruwana????????

????️????️????️????️????️
[8/31, 8:26 AM] Safiyya: ????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????

_ABDUL  JALAL_
       (2020)

  _WRITTEN BY AISHA HUMAIRA_
(Daddy's girl)

           PAGE-  22&23

PART 1

_Bismillahir Rahmanir Rahim, da sunan Allah me Rahma me jin kai, Allah ka yi salati a bisa shugaban mu Annabi Muhammad (salallahu alaihi wassalam)
Bayan haka, ban rubuta wannan littafi domin cin zarafin wani ko wata ba, na yi shine domin nishadantarwa, da kuma wa’azantarwa, ku biyoni domin jin me wannan labarin ya kunsa.
Yanda nafara Allah yabani ikon kammala shi

Ina maraba da shawarwari, sharhi, ko kuma gyara, nagode.

Domin Samun karanta wannan littafin yi magana ta what’s app akan wannan lambar

07063065680
Kokuma addanna wannan link din domin samun novel din

????https://chat.whatsapp.com/EtB4KI52K0v5FQc2ELhidL

I want comments not stickers or just thanks????????????????
Your comments give me courage

    -My First Novel-

Not Edited

Jinine ya wanke mata fuska ta fasa kara yarinyar tayi, itako Jalila ko ajikinta, hakan yayi dadi² da isowar class mastern su Jalila hankalinsa ne ya tashi ganin duk saurin da yayi Jalila ta riga tayi aika² be kara tsurewa ba seda ya tabbatar da wadda aka fasawa goshi salati yayi, Hanan Abdurrasheed Yar gidan babban captain din sojan ruwa da aka kawo ranar litinin ita Jalila ta fasawa kai shi kansa ba yadda beyiba ya canzawa Hanan gurin zama saboda yasan me gurin tafi kashi doyi wato queen J, amma hanan yarinyar akwai izza da jin kai, tace ita dole nan gurin takeson zama,
yanzu yasan ba Jalila ba su Kansu makaranta Ta janyo musu
“Jalila mene haka kika aikata, wannan wane irin shirme ne, yaushe ma kika dawo ne bansaniba memakon kizo kigayamin seki dauki doka a hannu kalli haukan da kikayi”
“Niba hauka nayiba daba ta mareni ba inaga da hakan bata faruba”
“Shut up zaki gane kuranki ubanta sojane insuka casaki inaga daga yau kindena Neman magana”
“Wai da anyi magana se afara maganar babanta sojane,
Allah sarki mukuma ‘ya’yan Allah bani marasa gata, wallahi ko Yar gidan rocket ce bata isa ta mareni in kyaleta ba”
Ya fuskanci babu alamar nadama tareda Jalila Dan ko kadan bata tsorata da abinda tayi ba itakuwa Hanan tuni aka tafi da ita school clinic akaimata dressing daga nan Hanan bata saurari kowa ba ta fice daga makarantar duk yadda akayi a dakatar da Hanan amma tayi waje ta tafi gida
Jalila aka kira office din director
Aka dinga mata fada kowa da abunda yake fada a cikin malamai wasu abun kirkinta wasu akasin haka ciki hadda wata malama ta zage ta dinga zagin Jalila matar a bayan layinsu Jalila take, Jalila ta taba fada da Yar malamar, Dan haka dama tanajin haushin Jalila
“Dama wannan yarinyar ba tarbiyyace da ita ba, bata da mutunci Sam dama ina za a samu wata tarbiyya a gurin Yar mace”
Jalila ce ta daga kai da sauri ta kalleta
“A’a madam adinga hakuri Jalila yarinyar kirkice, tana da tarbiyya ita dai matsalarta da students ne ga tarin alkhairanta ga makarantar mu dabazamu manta ba”
Cewar director
“Hmm yallabai baka San yarinyar nan bane uwatta Sam bata son laifinta ita ta sangarta ta lalace, amma yarinya sekace Yar daba, takama Yar mutane ta fitar mata da jini, dama charity begins at home duk abunda yarinya takeyi to haka taga uwatta tanayi”
“Sir kaimata magana kartakuma zaganmin uwa duk zaginta ta tsaya kaina takuma zagina sena rama, uwa ba tafi uwa ba”
“Innalillahi wa inna ilaihi rajiun Jalila ta daban ce
Jalila koma class dinku yanzu”
Cewar director ita kuwa Jalila ta mike ta koma ajinsu
“Dan Allah kalli yadda take ikrarin zata zageni yarinyar nan kawai a koreta shine mafita”
Inji malamar dazu
“Korarta ba shine mafita ba yarinya ce me matukar kwazo in muka koreta munyi asara babba”
Cewar wani malami
“Hakane kam wan mahaifinta abokina ne bazan taba korar masa ya ba, kuma duk fitinarta bantaba ganin tayiba se yau yanzu dai mahifiyarta zamu gayyota tazo mu zauna da ita dakuma wakilinta Dan na tabbatar, Yar gidan sojan nan se sunzo makarantar nan”
“Allah yasa suci kaniyarta sumata dukan tsiya”
“Haba madam in “yarkice fa baza kice haka ba ai shi da na kowa ne addu’a yakamata ayi mata Allah ya shirya Allah kalli dai yasan abunda zata zama nan gaba”
Inji director

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button