ABDUL JALAL PART 1 HAUSA NOVEL

Hanan ce ta shiga tangamemen palour tana kuka wata babbar mace ce zata yi shekaru arba’in da takwas amma Hutu yasa in ka ganta seka zata batafi shekaru talatin da biyu ba, gefenta kuma ga wani babban mutum shima yana shan tea
“Ke Hanan meke faruwane ne yasameki haka a fuska”
Matar Tai maganar cikin iyayi da isa
Mutuminne ya kalli hanan shima
“Auta meyasami goshinki haka meyafaru?”
Hanan kuma fashewa da kuka tayi ta kwashe abinda yafaru da karya ta fada tace Jalila tamata duka ta dinga gwarata da bango tana zaginta
“Amma auta kin bani kunya kamar ba Yar Dana Haifa a cikina ba ki tsaya wata yarinya tamiki duka hada fasa miki goshi kamata yayi insa bulala in zaneki ai”
“Wannan wace irin magana ce kakeyi haka a dakar min yarinya haka daga shigarta makarantar, wace Yar marasa galihun ce ta isa tayiwa y”ata haka in kyaleta wallahi senaga gatanta a gurin nan senaga uban da ya tsaya mata, se nasa an kulleta daga ita har ubanta”
“No ban yadda ba kinsan ita Hanan din metayi yarinyar tayi mata haka mubi komai a hankali ki bari gobe in Allah ya kaimu da kaina zanje makarantar indai yarinyar ce bata da gaskiya semusan abinda yakamata muyi’
” daddy ance mata baba na soja ne fa amma secewa tayi wai ko Yar gidan bullet ce, Allah yasa Kaine AK47″
Abun ma dariya yabawa baban Hanan
“Lallai yarinyar nan tana da karfin hali”
Itakam Maman Hanan iya wuya ta kulu taso ace baban Hanan ya kyaleta data nunawa yarinyar banbancin civilian da kuma kaki, zata so taga uban daya tsayawa yarinyar nan ko baban Hanan be saniba seta koyawa yarinyar nan darasi seta nuna mata banbancin dake tsakanin yayan farar hula dakuma “ya’yan rainon bullet.
Tun kafin a tashi daga school wannan malar taje gidansu Jalila tagayawa Ummi abunda Jalila tayi bayan haka hadda cewa itama Jalila ta zageta tsaf
Hankalin Ummi yayi matukar tashi da jin abunda Jalila tayi taita bawa malamar hakuri
Ilham ta dawo daga makaranta amma har taje ta dawo bata fuskanci komai ba, kamar yadda Daren jiya batayi bacci ba tunda Jalal ya nuna mata messages din wayarsa da yake tuhumarta akai, hankalinta yaki kwanciya tun jiya take takura kwakwalwarta domin kokarin gano wadda ke turowa Jalal wannan sakon amma takasa tuna komai, a iya saninta ba ya muamala da mata, to ta Yaya? wacece wannan take kokarin rusa nawa shirin ita ta kafa kanta,
Jikinta a sanyaye taje tayi wanka amma takasa cin abinci “ko gurin Nana zanjene ko zata tayani gano wacece ta, tambayi kanta
Kodayake yanzu ta dawo daga makaranta kar in takuramata koma inje tana wayar da wannan sha³ Yar uwatta ta
Da sauri Ilham ta mike JALILA tafada a fili, tabbas JALILA ce itake turomasa wannan sakonin dan babu Wanda yakewa Jalal shishshigi in ba itaba iya sanina Jalal baya kula mata ko a family
Amma indai na kara bincike na tabbatar Jalila ce sena yi maganinta babu wata “ya mace data isa tayi takara dani a soyayyar Jalal, wallahi JALAL nawane ni kadai, duk macen datayi yinkurin yin takara dani senaga bayanta
se yanzu nagane wato duk wannan shishshigin da take masa Ashe sonsa take
To ba ta isaba wallahi
Koda aka tashi daga makaranta Jalila hankalinta kwance ta taho gida tare da kudurcewa a zuciyarta setaje gidan malaman nan data ce mata ‘Yar mace ta mata warning dan bata hakura ba,
Gida ta tafi ta shiga da sallama amma Ummi bata amsa mata ba dan haka kai tsaye dakin Ummi ta nufa
Ummi nakan sallaya ta idar da salla tana lazimi Jalila ta wuceta ta canza kaya zuwa towel taje tai wanka tai salla tasaka uniform din islamiyya amma still Ummi bata kulata ba
“Ummi wai baki ganni bane, yau ko sannu dazuwa bakice minba se fushi kike wai mena mikine?”
Still Ummi batace mata komai ba gaban Ummi taje ta zauna
“Ummi wai meyene”?
Janyota Ummi tayi gabanta ta zuba mata kyawawan maruka guda biyu
” wato Jalila duk kokarin danake akanki inkika fita abinda zuciyarki tagaya miki shi kikeyi,
Kin fasawa Yar mutane goshi, kinzagi malamanki wannan itace tarbiyyar danayi miki ko?
To yanzu zankira Abban Jawwad in aka kashe case din nan gobe in Allah ya kaimu,
Koshi ko Jawwad wani yazo ya daukeki sukoma can kanon dake,
Lokaci yayi dazan koma dangina kema kikoma hannun wan ubanki tunda ba kya tausayina,
“Yar gidan babban captain fa na sojoji Jalila me nake dashi da Zan iya wannan rigimar dakika dakko, kano zaki koma nagaji, gaskiyar mahaifinki kafin yarasu da yace tarbiyyar mace seda tsayayyen namiji bazan iyaba Jalila nagaji”
“Har anzo angaya miki karya da gaskiya kekuma kin yadda ko Ummi to walla…..
” rufemin baki Dan ubanki”
Da sauri Jalila ta kalli Ummi bata taba jin Ummi tayi zagiba
“Akan kujerar zama ko? kikayi wannan aikin ko ubankine ya sassaka kujerar kokuma akai na haifeki dazaki daki Yar mutane akai kujerar banza,
Kuma saboda baki da kirki ki dubi malama ramatu Dan an miki magana ki zageta ko Jalila”
Se yanzu Jalila ta gane malama ramatu CE tazo tagayawa Ummi
“Wallahi Ummi malama ramatu munafuka ce bafa haka..
” Ai bazaki canza ba, hali indai nakine bazaki canza ba agaban nawa ma kuma zagin malamar ki kike ko?
“Wallahi niba malama ta bace yan primary take koyarwa bata taba koyamin uwar komai ba”
“Yayi miki kyau ina fada kina fada”
“A’a Ummi Dan Allah kiyi hakuri karkiyi fushi bazan karaba”
“Aini nagama yanke hukunci Abbanku zan kirawo azo a maidake kano, nima gurin nawa dangin zan koma”
“Ummi wai dagaske kike, dan girman Allah kiyi hakuri nace mikifa bazan karaba ni wallahi bazan koma kano ba”
“Sekuma kiyi ai tunda ni kin rainani gara kikoma gaban Zainab itace daidanki”
“Na shiga uku wallahi Ummi kafata kafarki ko bangon duniya zaki tafi ko a kafa sena biyoki, wallahi bazan kuma ba dan Allah Ummi, wallahi banason zuwa kano”
Banza ummi tayi mata ta dakko wayarta tana kiran Abba yayinda Jalila ke gabanta tanata faman kuka
Jawwad ne ya dawo daga makaranta ya gaji matuka kaya wanka yayi yai salla ya tafi gurin Rabin ran nasa wato Jalal
“Dan uwa ka dawo daga makarantar kenan sannu da zuwa”
“Yawwa bros Sannu da hutawa”
Jawwad yafada yana Neman gurin zama
“Nagaji sosai Jalal,”
“Nagani a idonka ai yau kukayi tests din ko?”
” eh yaune Alhamdilillah test din duk se godiyar Allah sunyi sauki sosai kuma hada jajircewar ka da addu’arka proud of you dan uwana rabin jiki”
“Kajika kaifa kake karatunka bani nake maka ba wannan kan naka akwai ja mutumina i wish nike da kwanyarka”
“Amma fa ka zageni Jalal, kasan ban isa inyi karatun dakayi a bayaba in kana waje wayake Neman irinmu, Jalal wai yaushe zaka koma makaranta ne kai?”
“Zan koma amma ba yanzuba, bana son wannan zancen zomuje muci abinci”
“A ina kuma ga abinci can a Gida zuwa nayi muje mu ci”
“koma inane muje daganan kasha ice cream ka dan huta, ka huce wannan gajiyar “
“Kaikake koyamin kwadayi fa”
Dariya sukayi gaba daya
“Kasan wani abu Jawwad?”
“A’a seka fada?
” wallahi wata mayyace take uzzurawa rayuwata gashi tayi hiding number balle insata a black list, kullum seta kirani kota turomin messages ni na rasa yadda zanyi, wallahi na gane wacece setayi Dana sanin wannan gangancin da take min”
Dariya sosai Jawwad yayi
“To kai meye abun damuwa aciki, dan ance ana sonka”?
“Mtseww kai kafiya shirme Jawwad ni bani da lokacin wannan shirmen, inyi rayuwata ni kadai ya fiyemin, duk yayinda ka gayyoto mata cikin rayuwarka kamar ka gayyatowa kanka matsalane”
Dariya Jawwad ya dingayiwa JALAL seda Jalal yafara jin haushi sannan ya dena
“Jalal wayagaya maka mata matsalane, mata ni’ima ne, tabbas akwai daga cikinsu masu matsala, amma akwai na kirki sosai, soyayya akwai dadi mussaman in kayi dace da mosoyi na kwarai, bazaka gane hakan ba seka fada tarkon soyayya”
“Hmm mata duk matsalane indai irinsu Ilham ne duk matsalane”
“Hmm bazaka gane ba Jalal”
“Eh naji bazan ganeba”
“Lokaci ze ganar da kai ai”
“Eh naji mutafi”
Jeje ne yakira Jalal yana son su hadu Jalal
Shikuma yace masa ya fita shida Jawwad bazeyiwu su hadu yanzu ba
Gurin cin abinci suka tafi shida Jawwad
Bayan sungama cin abinci ne suna hira aka kira Jawwad lambar Ummi yagani ya kara nutsuwa ya dau wayar
“Salamau alaikum Ummi barka da rana”
“Yawwa barka Jawwad ya kake ya mutan gidan”
“Kowa lafiya Ummi ya Jalila”
“To lafiya kalau za a ce meyasamu lambar abbanku nakira bata shiga”
“Inaga inda yake ne ba network, amma lafiya Ummi”
Ajiyar zuciya Ummi tayi ta kwashe kaf abunda yafaru tagayawa Jawwad
“Yasalam Ummi kiyi hakuri insha Allah komai zezo da sauki, yanzu bana Gida idan na koma zanwa Abban bayani insha Allah, kiyi hakuri Ummi dan Allah kinsan har yanzu yarinya ce”
“Ba batun yarinta Jawwad tsabar rashin hankaline kawai
” adai yi hakuri Ummi “
Haka dai sukayi sallama Jawwad ya dafe kai
“Ohhh my God sisy ba dai rigima ba”
“Ya dai meyafarune?”
Jalal ya tambayeshi, Jawwad ya kwashe komai ya gayawa Jalal,
Dariya Jalal ya dinga yi kaman wani tababbe
“Kan bala’i wannan yarinyar Yar bala’ice wallahi, kaga zancena ko Jawwad, nagaya maka mata matsalane, mussaman irin wannan kanwar taka zama da ita seda panadol”
“Hmm haba Jalal kaima kanwarka ce, Jalila bata son raini bata yadda da wulakanci ba nidai fatana Allah yasa kar baban yarinyar yayi mata wani abu”
Wata dariyar Jalal yakumayi
“Kamar ya kar yayi mata wani abu “yarsa fa ta Daka, aigara suko yamata hankali yadda gobe bazata kuma ba,”
Yayi maganar yana dariya
“Haba Jalal Yar gidan Abee ce fa, in duniya da gaskiya bekamata kace haka ba”
“Hakane Jawwad kaima kace wani abu amma kasani bataji, in mutum yana rashin kunya in besamu dai² da shiba baze dena ba