Uncategorized

ABDUL JALAL PART 1 HAUSA NOVEL

Jalila tana daki tana gugar uniform zasu koma makarantar boko Ummi kuma tayi bakuwa
Jalila taji kaman ana harbe² a waje da sauri ta fito tsakar Gida
“Ummi bakiji karan bindiga ba”
Bakuwar Ummi tace
“Wani captain ne na sojoji yake tarewa a anguwar nan bakiga wani kerarren Gida ba da aka gama kwanan nan ai nasane wallahi gidan ya keru kaman a kasar waje “
“To shine kuma za a zo a cikamana kunne da karar bindiga saboda shirme, ni gidan ma nakeso in gani inga iya keruwarsa”
“Allah yabaki sa’a kije Neman magana duk yadda zasuyi dake se dai suyi dan ba abunda zan iya indai sojojine zaki yabawa aya zakinta”
Ummi tai maganar cikin bacin rai shiru Jalila tayi ta koma daki

Jawwad ne yakema Jalal fada akan fitar da yayi daga samun saukinsa
Yayinda Jalal ke bashi hakuri
“Ai gani dai na dawo ban zauna a can ba hankalinka ya kwanta”
“Bawani hankalina ya kwanta kabata min raine ka dinga sassautawa kanka wannan abubuwan dakake durawa cikinka”
Hade rai Jalal yayi “naji kuma ina nace kayi hakuri “
“Haka ka iya ai saura ka kara fita”
Jawwad yayi maganar da alamun gargadi
Dariya Jalal yayi
“Sorry yayana bazan kuma fitaba a yau insha Allah”
Murmushi Jawwad yayi sannan ya fita
Bayan fitar Jawwad
Jalal ya saka wayarsa a caji ya mike yatafi cikin Gida part din daddy yaje suka sha hira
Cikin hikima daddyn yake masa nasiha
“Daddy nima bana jin dadin abunda nake amma kacigaba dayimin addu’a wataran zakaga kaman banyiba”
“Nima ina fatan hakan yaron kirki”
Se kusan shabiyundare Jalal ya fito daga part din daddy shima mummy ce taje part din daddy shiyasa ya fito
Ilham tana kwance akan kijerun parlour tana kallon Bollywood
Waiwayawa tayi taga Jalal
“Sannu Yaya ya jiki?”
“Da sauki”
Rannan a hade Yabata amsa ya fice
Yana zuwa dakinsa ya tarar missed calls kusan takwas
Da wannan unknown number din
Tsaki yayi yaje yayi wanka yazo ya nemi gurin kwanciya ya dakko wayarsa hotonsa ne da Jawwad akan wallpaper dinsa kallon hoton yayi sunyi kyau a hoton matuka murmushi yayi ze bude what’s app dinsa message ya shigo wayarsa budewa yayi

"Haba baby at least ko sau daya yakamata ka dau wayata kasan kuwa yadda zuciya ta takeyi I feel u in my every heart beat, nayi missing innocent face dinka gashi kaki yadda ko muryarka inji help me baeb na damu da kai
       From ur lovely Bae"

“Wai wannan wace irin Jaraba ce haka, wace ce wannan take Neman yimasa kutse haka a cikin rayuwarsa shi baze iya wannan shirmen ba wannan soyayyar duk haukane da bata lokaci”
Yana cikin wannan mitar ne wayarsa kuma takama ringing unknown number din ce dai
Dagawa yayi a fusace
“Waike wace irin mahaukaciyace karfe nawa yanzu nibana wannan haukan ki kyaleni tun kafin ta kaimu ga bata miki rai”
“Wow komai naka birgeni yake baby jin muryan nan taka kawai ta isheni bacci me dadi,
Mark you ba abunda zakamin Wanda ze batamin rai
Love u…….
Katse wayar yayi ya kasheta gaba daya ya jefa wayar kasa nonsense yafada a hankali

Washe gari bayan sallar asuba Ummi taga Jalila ta koma bacci
” ke baby ba ankoma school ba kwana biyu da komawa amma kina nade a Gida tashi ki shirya yau makaranra zaki tafi”
“Ummi bangama shiryawa ba in nagama zan koma”
“Aikuwa sekin koma yau din nan”
“Ummi bani da socks fa, kuma ni sekin canzamin school bag zan koma”
“Kibari inzo gurin nan baki tashi kinyi shirin makaranta ba ni da kene”
Ummi ta fita daga dakin Ummi na fita Jalila tacigaba da baccinta har kusan karfe bakawai Ummi tazaci Jalila ta tashi amma tana zuwa ta tarar da ita a cikin bargo
Ran ummjne ya baci ta yaye bargon ta Dala mata duka tashi dan kaniyarki dama baki tashi ba tashi kisa uniform kitafi
“Ummi dan Allah kiyi hakuri, banga socks dina bane”
Girgiza kai Ummi tayi
“Allah ka shiryamin yarinyar nan, ai tunda baki gadama ba nasan bazakiba zakiga tsiya”
Wunin ranar Sam Ummi taki kula Jalila
Ta dinga binta tana bata hakuri tana mata magiyar ta saimata wata jakar daga karshe seda Ummi ta bata kudin Jaka da socks din hankalinta ya kwanta
Amma Ummi tace bazata fita ba seda yamma

Washe gari se bayan sallar la’asar sannan Jalal ya kunna wayarsa amma yana kunnawa sakonine sukacika masa waya wasu na bin wasu
“Wannan wane irin Jaraba ce haka”
Sakonta na karshe ya duba “Baby in baka bude wayarka ba zanzo har inda kake, tun safe nakasa nutsuwa ko har yanzu baka da lafiya ne?
Na damu da kai baby
From your lovely Bae”

“Wannan wace irin Jarababbiya ce da take uzzurawa rayuwata ne”
Yana cikin wannan tunanin Sega Ilham ta shigo da kayan abinci ta samu guri ta ajiye
“Yaya ga abinci inji mummy
Harta mike zata fita ya kira sunanta
“Ilham”
“Na’am”
“Zo nan” seda cikinta yayi kara gabanta ya fadi Allah yasa ba wani abun nayi masa ba jiki a sanyaye ta nufi inda yake guri ya nuna mata kusa dashi ta zauna wayarsa ya dakko ya shiga messages din nan ya nunamata
“Ke kike turomin wannan shirmen ko?”
Gabanta ne yafadi ita ba tuhumar dayake matane ta sata faduwar gaba ba se fargabar wace wannan take shirin yi mata kutse
“Tambayarki fa nake”
Jiki a sanyaye ta daga kai ta kalleshi
“Bani bace ba”
Jawwad ne ya shigo
“Inyee yau zumunci ake jine Yaya da kanwa”
Basu kulashiba ya karasa ciki ya zauna yaga ran Jalal a bace Yana ma Ilham magana

“To waye?”
Jalal Ya tambayeta
“Ya za ayi in sani yaya, nidai nasan bani bace”
Tabashi amsa hawaye na gangarowa daga idonta
“Uban me na miki zakimin kuka”
Wani irin kallo tayi masa
“Yaya Jalal tambayata kake meyasa nake maka kuka ko?
Ina nuna kulawata akanka, baka damu dani ba bakajin me nake ji a raina hasali ma ka tsaneni, amma wata a waje tana shirin rusani ga sakonin da take turomaka, kuma kake tuhumata ni ina naga fuskar da zan turo maka wannan sakonnin “
Cikin hargowa ya mike ze zazzaga mata bala’i
Jawwad ya ga tsananin kishi kwance a idon Ilham, tausayinta ne Yakama Jawwad dan haka ya dakatar dashi
“Ilham gaskiya ta fada Jalal”
Jawwad Ya kalli Ilham yace
“Tashi kikoma ciki”
Sannan ya kalli Jalal

Yamma nayi Jalila ta shirya ta dau kudin safa da Jakarta tayi waje
Kai tsaye inda ake fadan gidan sojan nan ta nufa daga waje ta karewa gidan kallo
Aranta take fadin gaskiya gidan nan ya hadu saura kuma inshiga inga meye a ciki yadda ya hadu daga wajen nan cikin kuma ai nasan yafi haduwa
Daga nan ta mika ta nufi inda zata sayi jaka amma seta hango wani kanti da sojoji a bakin gurin dan haka ta yanke shawarar zuwa taga meye akeyi a gurin
Kai tsaye ta kutsa cikin kantin wani soja ne ya daka mata tsawa yace ta tsaya a waje se sungama sun tafi tukuna
“Dan Allah kabari abu zan siya kawai in tafi ni ba gurinka nazo ba “
Zekuma magana wani sojan yace ya batta ta shiga
Tana shiga taga wani babban mutum a zaune akan kujera fuskar nan tashi murtuk babu annuri
“Ina wuni”
Jalila ta gaisheshi be amsa ba
“Baba gaisheka fa nake nace ina wuni”
Dan juyowa yayi ya kalleta ya danyi murmushi jin takirashi da baba
“Lafiya kalau sannu yan mata”
“Yawwa”
Ta sai chocolate dinta ta mutumin nan yace abawa Jalila shize biya
Seda ta risina sannan tace
“Baba nagode sosai”
“Bakomai adinga shan chocolate din a hankali yana kashe hakori”
Murmushi Jalila tayi ta fito “aikin banza na daukama wani abun ake a gurin to me sojoji suke anan ko gadinwa suke oho”
Ta siyo Jakarta ta fito dayake kusa da kantin ake saida jakunkuna
ta hangi mutumin dazu ya fito daga kantin nan ze shiga mota se ya yadda wallet dinsa da sauri ta je ta dauka, amma tuni sunyi nisa sun bar gurin sun nufi layin gidan wannan sojan
Ta dinga jujjuya wallet din nan kawai ta tafi Gida da wallet din
Bata nunawa Ummi ba ta boye wallet din
Ta faki idon Ummi taje ta dau wallet din ta bude kudin kasar wajene a ciki da ID card bata tsaya bin ta ID card dinba ta aje wallet din cikin sabuwar jakar makarantar ta cikin litattafanta

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button