Uncategorized

ABDUL JALAL PART 1 HAUSA NOVEL

Washe gari Ummi ta tursasata ta shirya ta tafi makaranta, ta wannan layindai na gidan nan Jalila tabi dan takuma ganin gidan nan kuma ko Allah zesa taga mutumin nan
Tanata kallon gidan wani soja ya kalleta
“Ke me kike kallo wuce ki tafi makarantar ki”
Ya mutsa fuska Jalila tayi
“Ina ruwanka da makaranta ta?kallo kawai zanyi in tafi”
“Ba a son yawan ganin mutane a arear gurin nan saboda tsaro dan haka wuce ki tafi”
“Did I look like criminal, da uniform dina na makaranta balle kace wani abun zanyi, sekace gidan shugaban kasa naga dai gidan mutum ne ba aljan ba in me gidan yasan bayaso a dinga wucewa ta hanyar gidan ai da seyaje duniyar wata ya Gina gidan ba duniyar mutane ba”
“Kut wace irin yarinya ce wannan?”
Aikuwa sojan nan beyi wata² ba ya zare beilt da nufin ya koya mata hankali se su kaga wasu motoci suna shigowa Latin manyan motoci ne glasses din duk tint ne mutumin jiya da ya sai mata chocolate ne ya fito daga daya daga cikin motocin
Wannan sojan da ya zare belt ne ya kame yana saramasa da ido yai masa magana sojan ya tsaya
“Laa baba ina kwana”
Jalila ta tsuguna tana gaisheshi “lafiya kalau Yar baba, meyahada ki da wannan”
Ya nuna mata sojan nan da ya biyota
Bata boye masa komaiba ta gayamasa murmushi yayi a ransa yace lallai wannan yarinyar Yar rigima ce amma a fili yace
“Yar baba yanzu kin makara ki tafi makarantarki rabu da shi
Kai baka ganin Yar makaranta ce kawai daga kallon Gida se a ce za a bigeta ina nema mata afuwa”
Jalila tasaka hannun a Jakarta ta dakko wallet din nan ta mika masa
“Jiya ka yaddashi bayan kafito daga kantin nan”
Hannu yasa ya karba tasan ce kuwa yana ta dubawa tun jiya be ganta ba yayi zaton yayi miss placing dinta ne
Murmushi yayi “nagode sosai Yar baba Allah ya albarkaci rayuwarki “
“Ameen nagode”
Ta juya ta tafi hanyar makarantar su ta makara sosai amma taci sa’a ba malami a ajinsu dan haka ta shige tanufi ajinsu
Class dinsu ne ya kaure da hayaniya ga Queen ta dawo nickname dinta kenan a makarantar boko Queen J
Kai tsaye bayan sungama murnar ganin juna da yan ajinsu gurin zamanta ta nufa amma me setaga wata hakima ta hakimce mata a seat Jalila dai bata Santa a ajinsu ba maybe newcomer ce dan haka Jalila tace
“Sannu dai excuse me gurin zama nane ina bukatar zan zauna”
Banza yarinyar tayiwa Jalila
“Ko kurma ce ne? Nace kifito nan gurin Jalila ne fada tace”
“Wallahi mun gaya mata har malamai sun San nan gurinkine amma tace ita kuma dole anan zata zauna”
Cewar wata daliba
Ita kuwa sabuwar zuwan nan bata da niyyar magana balle Jalila tasa ran zata tashi sema wani kashingida tayi ta kurawa Jalila ido tana hura hanci tana kallon Jalila up and down
“Ke yau kome kikeji zan sauke miki shi yau koda uban me kike yawo wallahi sekin bar seat din nan uwarkice ni a rashin mutunci”
Dariya yarinyar tayi “ok yi abinda zaki iya nikuma na miki alkawarin kawo karshen rashin kunyarki a yau base gobe ba”
“Queen J dan Allah kiyi hakuri ki kyaleta babanta fa babban sojane ranar Monday aka kawota”
Wata dalibar tai maganar tana kokarin Jan hannun Jalila
dukan benci Jalila tayi
“Wallahi ko Yar gidan bullet ce, ke Allah yasa baban tane AK47 wallahi seta tashi this is my kingdom, in ubanta ya tsaya mata ni Allah ya tsayamin, Kafin kiyi maganina ni zan fara maganin wannan izzar taki, ko kina wa kowa hauka ba ayiwa Jalila”
Hannu biyu Jalila tasaka ta fizgo yarinyar nan daga cikin benci aikuwa yarinyar nan ta wankawa Jalila mari,
Wasu daga cikin dalibai suka tafi kirawo malamai domin raba fadan nan
Amma tuni Jalila ta rama marin nan ta kara mata wani, Jalila ta dage ta hankada yarinyar nan kan bencina nan take goshinta ya fashe jini yashiga fita

Share please
More comments more typing…….

Proud of you my fans INA jin dadin adduoinku nagode kwarai Allah yabar kauna
❤❤❤❤❤
Team JALILA kunga abinda yau ta dakko to ni ba ruwana????????

????️????️????️????️????
[9/12, 6:02 AM] +234 816 830 7871: ????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????

_ABDUL  JALAL_
       (2020)

  _WRITTEN BY AISHA HUMAIRA_
(Daddy's girl)

           PAGE-  24

PART 1

_Bismillahir Rahmanir Rahim, da sunan Allah me Rahma me jin kai, Allah ka yi salati a bisa shugaban mu Annabi Muhammad (salallahu alaihi wassalam)
Bayan haka, ban rubuta wannan littafi domin cin zarafin wani ko wata ba, na yi shine domin nishadantarwa, da kuma wa’azantarwa, ku biyoni domin jin me wannan labarin ya kunsa.
Yanda nafara Allah yabani ikon kammala shi

Ina maraba da shawarwari, sharhi, ko kuma gyara, nagode.

Domin Samun karanta wannan littafin yi magana ta what’s app akan wannan lambar

07063065680
Kokuma addanna wannan link din domin samun novel din

????https://chat.whatsapp.com/EtB4KI52K0v5FQc2ELhidL

I want comments not stickers or just thanks????????????????
Your comments give me courage

    -My First Novel-

Not Edited

Yayan Hanan se kallon Abba yake kaman yasan shi.

Tunda Jalila ta shiga office din taje tasamu guri ta durkusa kanta a sunkuye kai kace wata mutumiyar kwarai ce
Ga director na makarantar, ga Ummi, da Abban su Jawwad, sekuma baban Hanan da yayanta, se mukarabbansa da suke waje bakin office din sekuma Jalila da hanan dasuka shigo yanzu
Baban Hanan Bin Jalila yayi da kallo sannan yayi Murmushi a zuciyarsa indai wannan ce zata aikata don bata da tsoro

Kanta a sunkuye tace “Abba ina kwana”
“Lafiya kalau Jalila ya rashin ji”?
Shiru tayi ba tace komaiba
“Abbanki kawai kikasani ko Jalila,?”
Director ya tambayeta batace komai ba still shiru tayi

“Was nake gani haka kadai ace Yar baba ce wannan?”
Da sauri ta dago ta kalleshi dan murmushi tayi se yanzu ta ganeshi mutumin nan ne daya hana wannan sojan zaneta, Wanda ta tsinci wallet dinsa
“Sannu baba ina kwana”
“Lafiya kalau Yar baba”
“Dake akayi fadan kenan, dama haka kike da fada, ai wannan sister dinki ce” ya nuna hanan

“Ni ba sister na bace nikadai Ummi ta Haifa, se kanwata daya Nana” Jalila tai maganar ba tare data dago ba
Dariya tabasu gami da mamaki babu nadama a tare da Jalila ita haryanzu a ganinta ba laifi tayiba tunda ita aka takala da fada
“Daddy wai kasantane”?
Yayan Hanan yai tambayar yana kallon mahaifinsu
“Eh nasanta ‘yata ce shekaranjiya Allah yabani ita”
Baban Hanan yabada amsa
Ya kalli Abba da Ummi
“Ai Dana San itace ma bazanzo ba yarinyarku mutuniyar kirkice, fitina CE kawai ta yara kuma ga dukkan alamu bata son wargine ko Yar baba?”
Ya tambayeta yana murmushi
“Komai ya wuce amma Yar baba kidena Neman magana kinji yarinyar kirki kin dagawa mamanki hankali da babanki, gaskiya suna sonki dayawa”
Gyada masa kai Jalila tayi

“To baba na dena insha Allah”
A ranta kuwa tace dama wai wannan shine captain din da ake ta fada wani salihi dashi haduwar mu biyu be tabamin rashin mutunci irin na sojoji ba
Ni na daukama zanga tunda ga bakin office anfara kwallo dani

“Daddy wai yanaga ka maida abun jokes jini fa ta fitar min kuma ta zageka”
Hanan tai maganar cikin shagwaba da hawaye a idonta
“Ohh sorry dear itama yata ce daga yau na hadaku kawance”
“What ba dai dani ba wallahi, Allah ya kiyaye”
Hanan tai maganar cikin tsiwa
“Baba nikuma na karbi kawancen nagode sosai daga yau tazama kawata”
Jalila tai maganar tana murmushi tare da kallon hanan
“Allah yayi miki Albarka Yar baba”
Abun ya daure musu kai yaushe mutumin nan yazo anguwar amma har yasan Jalila gaskiya a sojojin ma yana da matukar kirki, gaba daya kasa cewa komai sukayi

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button