ABDUL JALAL PART 1 HAUSA NOVEL

“Daddy ni gani nayima tana kama da Hanan wallahi”
Yayan Hanan ya fada yana kuma kallon Jalila
“Nima nagani Abdallah”
“Kinsan Aliyu Usman Imam”
Yayan Hanan ya tambayi Jalila
Dagowa Jalila tayi ta kalleshi
“Kai Yaya Jawwad kake nufi ga Abbanmu nan” ta nuna masa Abba “no wonder naga suna kama kuma ance shine abbanki shine class ref dinmu a BuK yana da kirki ga kokari amma gaskiya shi ba fitinanne bane kamarki”
“Waze hada ma shi Jawwad yaron kirkine kaman ma ba sunansa Aliyu ba amma wannan sekace kura saboda fada”
Ummi tayi maganar tana nuna Jalila
“Dan Allah kuyi hakuri bazan karaba Insha Allah”
Takoma gaban Abba shima ta tsuguna
” Abbana Dan Allah kaima kayi hakuri nadena insha Allah, Dan Allah kuyi hakuri”
Kara birge baban Hanan tayi tasan tayi laifi kuma ta bada hakuri, ita damuwar iyayenta ce bata so yaji inama Hanan ce keda wannan tarbiyyar tayi laifi tabada hakuri ai sedai in kaga dama ka kasheta ko ka barta da rai amma bata laifi ta bada hakuri indai Hanan CE
Director ko a ransa yace lallai wannan yarinyar ita fushin iyayenta ne a gabanta bata damu data bawa su Hanan hakuri ba suda akayiwa laifi a fili kuwa yace
“To Alhamdilillah tunda itama ‘yarka ce mungode da wannan karamci naka yallabai,
Kamar yadda ka fada Jalila yarinyar kirkice saboda a dalilinta makarantarmu tasamu awards, tana da kokari ga hazaka, muna alfahari da ita a cikin dalibai, ita babba damuwarta ita da dalibaine, shima kuma insha Allah daga wannan shikenan tace bazata karaba”
Director yayi maganar yana kallon Captain Abdurrasheed
“Hakane dama dan Adam Tara yake be cika goma ba, muna kara bada hakuri dai ayi hakuri”
Abban Jawwad ne yai maganar yana kuma kallon baban Hanan
Itakam Jalila bataga dalilin bada hakurin dasu Abba suke tayi ba
“Karku damu ba komai yariga ya wuce ai, Allah ya shiryamana yara gaba daya, yayi musu albarka”
Suka amsa da Ameen gaba daya
Haduwar da akayi domin hukunta Jalila da yin sasanci se yakoma haduwar hada zumunci inda hira ta barke a office din director
Malaman da suke ta jira suga an fara casa Jalila se sukaga akasin haka
Daddyn Hanan ne yagaya musu yadda yasan Jalila daga ranar da ya saimata chocolate zuwa tsintar wallet dinsa, har exchanging lambar waya captain yayi da Abba, sukayi sallama kowa ya watse
Ummi ta saka Jalila a gaba Abba ya dauke su zuwa Gida
“Impossible wallahi a fitarwa da yata Jini sannan kace wai ba komai ka kyale yarinyar ta daki banza akan me?
” look safiyya shi da na kowane, kinsan halin Hanan sarai itama wani lokacin ta fiye fitina, da wulakanta mutane, for now ayi hakuri na rufe wannan case din”
“Aikuwa be rufu ba ni a gurina, dan mene Za a daukarmin yarinya sannan kace ka rufe case, waye uban yarinyar da yatsaya mata ta dokarmin yarinya”
“Ohhh my God mum Abdallah kinfiye rikici fa, wallahi ba Yar wani bace ba kawai dai she’s so kind, yarinyar and she regrets what she did, ni yarinyar ma tausayi tabani wallahi mamanta duk ta damu, gashi kuma kanwar abokin Abdallah ce”
“Kaga ya isa haka bana bukatar jin wani abu ya isheni haka, ko uwar abokin Abdallah ce senasa an koyamata hankali balle wata kanwar aboki, in kai ka hakura ni ban hakuraba wallahi…
” Enough “
Ya daka mata tsawa nan take ya juye ya koma sojansa fuskar nan kaman be taba dariya ba
“Idan kika kuskura kikayi wani abu akan yarinyar nan kinsan meze biyo baya kinsanni sarai”
Yayi maganar cikin tsawa sannan ya fice ya bar mata dakin
“Wai Jawwad meyake damunka ne tun dazu ka kasa zama, ka kasa tsaye se zagaye kakeyi”
Jalal ne dake kwance akan gadon Jawwad yai maganar yana kallon Jawwad
“Ta yaya zan iya zama bansan wani hali akeciki ba ko sojan da Jalila ta dakarwa yarinya ya hakura, bansan me ake cikiba nakira wayoyinsu gaba daya basu daga ba Allah yasa dai lafiya, Allah yasa basuyi mata wani abun ba”
Jawwad yai maganar cikin damuwa
Dariya Jalal yayi “to meye abun tada hankali in suka karairayota se ka tafi Kaduna jiyya”
Jalal ya karashe maganar yana dariya
Tsaki Jawwad yayi Wanda yayi dai² da ringing din wayar Jawwad
Da sauri ya dakko wayar yadaga a zatonsa Abbana
“Hello hey Aliyu yakake”
“Ina lafiya Alhamdilillah , amma ban gane me magana ba”
“A Rasheed ne”
Aka bashi amsa
“Ohhh Abdallah ban dauki muryarka bane, kuma bani da wannan lambar taka”
“Wallahi kuwa na canza layine”
“Allah sarki ya kake ya mutan gidan”
“Kowa lafiya Alhamdilillah, yau naga kanwarka”
“Kanwata wacce kenan ai Nana tana kano”
“Ba itaba wata Jalila”
Gaban Jawwad ne yafadi
“A ina kaganata ya akayi kasan kanwata CE?”
“Sabani suka samu da Hanan mummy ta daga hankalinta mukaje nida daddy, har muka hadu da abbanku”
Ajiyar zuciya Jawwad yayi sanan yace
“Alhamdilillah Abdallah ya ake ciki Dan Allah kuyi hakuri kabawa daddy hakuri,”
“Karka damu, ai ba abunda yafaru daddy yace “yarsace itama, kanwartaka ce Yar daruce Aliyu bata da tsoro”
“Nagode sosai Abdallah,”
“Ba komai Aliyu, nima kanwata CE, kuma wani abun mamaki suna matukar kama da Hanan din”
“Allah sarki Dan Allah kayimin godiya agurin daddy”
“Ba komai Aliyu girmankane “
Sukayi sallama, nannauyar ajiyar zuciya Jawwad yayi tare da fadin
“Allah gatan bawansa, kaga abun mamaki Jalal, Allah ya tsallakar min da baby, basuyi mata komai ba, Ashe kanwar abokina CE sukayi rigimar da ita, kanwar A rasheed CE yarinyar”
Dariya Jalal yayi
“U escape this time around, se Ku kiyayi gaba, Dan ba kullum ake kwana a gadoba”
“Eh munji, for now we are safe, se dariyarka ta koma ciki”
Jawwad yayi maganar yana kallon JALAL yai murmushi tareda shafa sumarsa
Jalila CE da umminta se Abban Jawwad a parlour
“Inaga lokaci yayi dazaka cika wasiyyar mahaifin JALILA, ka dauketa ta koma gabanka, nima in koma Gida, JALILA ba ta jin magana, kullum cikin Neman magana take, bataji Sam abunda zuciyarta ta raya mata shi takeyi, ayi mutum ba hakuri kullum cikin Neman magana”
“Haba ummina tun jiyafa nake baki hakuri ashe baki hakura ba
Nace fa bazan kara ba”
Jalila tayi maganar idonta taf hawaye
“Yi min shiru bazan hakuranba, ke banda Allah yasa mutumin kirki ne baban yarinyar nan da yanzu wani zancen ake ba wannan ba,
Ke ba Yar uban kowa ba, amma har kina ikrarin ko Yar gidan bullet ce ko,
Kanaji har wallet ya Yar ta dauka, da sunyi bincike suka ganota a gurinki sunanki barauniya, wannan halin naki in kika cigaba a haka to wahala zaki sha, ayi mutum fada kaman kura”
Abba ne ya nisa ya danyi murmushi sannan yace
“Haba ummu Jalila, babynki fa ba haka kwai takeyiba,
Kin manta marigayi shima haka yake baya daukar raini, gashi na jama’a kinfi kowa sanin halinsa ba wasa”
“Amma be kai wannan yarinyar ba, JALILA fa da kudinta seta saka ta sai rigima koda uban waye,
Duk rigimar Abu Jalila mutumne simple kuma yana da kawaici, amma ita sun raba hanya da hakuri”
“Ummu Jalila kenan kin manta biyuce ta hadarwa Jalila, kefa jinin sarauta ce akwai wannan izzar ta sarauta a jikin Jalila, haka zalika mahaifinmu, babansa shine sarkin Fulani a rigarsu, kinga ba yadda za’ayi Jalila ta yadda, da raini Jinin sarauta na zagayawa a jikinta
Mikewa Jalila tayi ta bar dakin ta koma dakinta ta kifa akan katifa tana kuka, bataji sallamar Siyama ba saboda kukan da takeyi se kawai ganinta tayi a gabanta, dafa Jalila Siyama tayi
“Aminiya meya faru? Garinya haka ta faru a school? Jiya da yau banjeba bana jin dadi dazu ake gayamin abunda yafaru tsakaninki da hanan nasanta babanta abokin Abba ne Sam bata da kirki Yar gadarace”
Siyama tayi maganar cikin damuwa
“Kinga ni ba itace agabana ba
Aminiya kinji wai Ummi sena koma kano gidansu Yaya Jawwad nikuma wallahi bazan komaba bana son zaman garin nan”
“To aminiya saboda me? Meye a ciki Dan kin koma?”
“Au haka zakice ko? Dama ba kya sona, hmm Dan bakisan abunda dangin Maman su Nana din nan sukemin ba, ga wannan mugun abokin Yaya Jawwad din, Siyama bana son rabuwa da Ummi wallahi tun jiyafa nake bata hakuri amma taki hakura yanzuma zancen takeyiwa Abba fa”
“Ki kwantar da hankalinki aminiya, nasan kawai dan kin bata mata Raine amma bazata bari kikoma yanzu ba”
Mikewa Jalila tayi ta dakko wayarta ta fara kiran wayar Jawwad
Lokacin Jawwad ya tafi masallaci yabar wayar a dakin
Dan haka Jalal ya duba wayar cwt sisy ya gani akan screen din wayar
Tsaki Jalal yayi, ya daga wayar amma yayi shiru bece komai ba
“Yayana dan Allah ka kira Ummi kabata hakuri, tun jiya nake bata hakuri amma taki hakura, tace sena dawo kano, dan Allah yayana, ka tayani bata hakuri maybe kai inka bata hakuri ta hakura wallahi nadena sata magana, bazan iya rayuwa babu ita ba “
Tai maganar cikin sheshshekar kuka
Bece komai ba ya kashe wayar
“Fitinanniya kawai yanzu ma kin kira danki kuma daga masa hankali, shikuma duk yabi ya wani rude ya biyemiki, kina son ummin kike daga mata hankali “
Yai maganar cikin mita bayan h ya katse wayar, kuma kira Jalila tayi amma yayi rejecting kiran ya kashe wayar gaba daya,
Jalila ta dubi Nana
“Nana Yaya Jawwad yayi fushi dani, yaki cewa komai, kuma ya kashe wayar Sa”
Share mata hawaye Siyama tayi
“Calm down Aminiya, seta yiwu beji dadin abunda kikayi bane, amma shima ze huce”