Uncategorized

ABDUL JALAL PART 1 HAUSA NOVEL

Maman Hanan ce hakimce akan kujera dauke da remote a hannunta, yayinda Hanan ta kwanta akan cinyarta tana kallon TV
Sallama Abdallah yayi yayan Hanan
Sannan yasamu guri ya zauna
“Da girman kujerarki mum barka da Gida”
Ya mutsa fuska tayi ta nisa
” “Yar uban waye ta dakarmin yarinya kunje kaida daddyn Ku amma ba wani mataki daya dauka, waye ubanta a garin nan”
Kallonta Abdallah yayi da mamaki
“Ohh I think dad has already closed this case, meyasa kike kokarin dawo da maganar nan, an sulhunta komai”
“Dalla yimin shiru, a gurina be wuce ba tambayarka kawai nayi Yar inace waye ubanta?”
Tai maganar cikin fushi
“Amm Mum Dan Allah kiyi hakuri zancen nan ya wuce wallahi kanwar abokina CE, kuma mum dinta tabada hakuri sosai, tundaga kano Wan babanta ya taho yau duk Dan subada hakuri fa, to mu suwaye daba zamu hakura ba”
“In kaga ma yimin nasihar tashi kabarmin parlour”
Be kuma cewa komaiba ya fice
Hanan ce takuma fashewa da kuka “mummy ciwon zafi yakemin kaina se ciwo yake wallahi ni ban hakura ba”
Tayi maganar tana kuka
“Yi shiru mana sannu, nima ba hakuran nayiba ai, ai jininki baze zuba a banza ba nasan matakin dazan dauka”

Abbane ya fito ze tafi, Jalila tafito da sauri daga dakinta tana kallonsa domin jin wani hukunci aka yanke akanta
Siyama ce tabiyo bayanta itama
“To se yadda ta yuwu, ummu Jalila ki hada mata kayanta in Allah ya kaimu sati me zuwa koni ko Jawwad zamuzo mu tafi da ita, tunda bata jin magana”
Abban Jawwad yayi maganar yana kallon Ummi
Kuma fashewa da kuka Jalila tayi
“Ummi nace na dena fa bazan kuma ba Dan Allah kiyi hakuri”
Girgiza kai Abba yayi
“A a senaga kindena din tukuna, a yanzu dai ban yaddaba zuwa sati me zuwa insha Allah in kin canza halinki, shikenan ta fiya kano bayan zuba”
Gyada kai tayi tana goge hawaye itakam Ummi banza tayi mata taki kulata
“Abba insha Allah bazata karaba ta dena”
Cewar siyama
“Anya kuwa wannan kawar taki batta kawai akwai rashin ji”
Abba yafada yana nuna Jalila
Haka Jalila ta cigaba da kuka tana magiya akan suyi hakuri
Abba yayi musu sallama ya koma, kano yayinda still Ummi taki kula Jalila
Abun duniya ya ishi Jalila, Jalila tayi trying lambar Jawwad har tagaji amma akashe
“Haba Yaya Jawwad kaima Fushin kake dani haka, shikenan kowa ya tsaneni”
Haka dai Jalila ta cigaba da sakeĀ² aranta tana kuka

Hannah ce take ta trying lambar Jalal taki shiga tayi messages din ba adadi amma shiru
Layin Jeje ta kira
“Da girman kujerarki, gimbiya sarautar mata farar mace Alkyabbar mata, Zara acikin mata, daya tamkar da goma, tauraruwa me wutsiya ganinki ba alheri ba”
Murmushi Hannah tayi da jin wannan kirari da jeje yake mata
“Jeje ya akayi ne dazu muna cikin waya da Jalal naji ta dauke nayi trying tun dazu wayar bata shiga”
“Wow har ya fara yadda ya amsa wayarki kice tarkon ya fara kamashi”
“Ina fa da sauran aiki Ja wallahi, shammatarsa kawai nake naji ya daga wayar, yanzu dai yana ina ne?”
“Nima bansan inda yake ba rabona dashi tun last week, wannan mayen ya hanashi zuwa inda nake”
“Allah sarki simple dashi abokin nasa da akansa zanyi aikin nan da yanzu nakusa nasara, shikam taurin Kaine dashi”
Dariya jeje yayi
“Lallai baki San Jawwad ba zahirinsa kika gani, tsawon shekaru shiya hana aikinmu tafiya yadda ya kamata anyi masa barazanar amma, bashi da niyyar hakura duk abunda kikayiwa Jalal, kai tsaye kamar kinyiwa zuciyar Jawwad ne”
“Tab amma gaskiya yana kaunar JALAL, yanzu dai ka bincikomin inda Jalal yake, inason zuwa”
“To bari in jarraba”

Jawwad ne yabi bayan Jalal
“Yanzu dai kayi hakuri zomuje se a siyo wata wayar”
Bece komaiba yabi Jawwad sukaje suka siyo sabon waya, yabada wadda Ilham ta tarwatsa aka gyara, domin ya kwashe abubuwansa masu mahimmanci na kan wayar, wayar ta daku, Dan karfinta Ilham tasaka ta buga wayar,
Jawwad ne ya dakko wayarsa don kiran Abba yaji koya dawo, seyaga wayar tasa akashe, be tunanin komaiba ya kunnata Abba ya kira yaji ko yakaraso, yace masa yana hanya.
Ya kashe kiran kenan message ya shigo wayarsa
Jalila ce ta turomasa message,
“Yaya kaima fushi kake dani
Shikenan kowa yatsaneni
Abba yayi fushi, Ummi ta
Dena kulani, Dan Allah kai
Kar kayi fushi dani”
“Allah sarki sisyna ni Sam bana fushi dake”
Jawwad yai maganar a fili Jalal da yake driving ya Dan kalleshi ya basar
Jawwad ne yaketa kokarin kiran Jalila amma taki dagawa, be fushiba haka ya dinga kiranta har daga karshe ta daga tana daga wayar sautin kukanta yaji
“Yaya Jawwad kaima fushi kake dani ko? Nakiraka dazu ka daga kaki magana daga baya kuma ka kashe wayarka”
“Nidin Jalila? Ni na isa in miki haka sedai matsalar network, a duniya banga laifin dazakiyi min in ki daga wayarki ba baby”
“Yaya Jawwad Ummi sunyi fushi dani wai se sun dawo dani kano, Dan Allah kabawa Abba hakuri,”
“Kai sisy to meye a ciki kinga seki dawo kusa damu naji dadin hakan”
Cikin shagwaba tace
“Ni wallahi, Yaya bana son zaman kano, ni nafi son zama a gurin Ummi”
“Hmm mune ba kyason zama damu ko”?
“A a Yaya nifa bahaka nake nufi ba, Ummi tace wai in na dawo kano garinsu zata koma”
“No, calm down sisy, dena kuka nan is OK ko so kike nima kisani kukan, bana son kukan nan”
Jalal da haushi ya isheshi Hannu yasaka ya fizge wayar daga hannun Jawwad
“Kana ta shirme da yarinya ko kunya bakaji, se wani shagwaba take kana lallabata”
Jawwad ne ya bishi da kallon mamaki
“To ina ruwanka dani so kake in kyaleta taita kuka in kanta yayi ciwo fa?”
“A’a bindiga kan nata zeyi ba ciwo ba, kukan dadi take da sojoji basu karairayota sun zubowa Abba a boot ba yakawo maka”
“To naji ban wayata”
Kashe wayar Jalal yayi,
“Na hana in munkoma Gida idan nabar gurin seka cigaba, kokuma in baka wayarka in tsaya ka sauka, seka samu gurin zama a titi, ka cigaba da shiriritar”
“Yanzu kiriĀ² bazaka bani wayata ba”?
“Eh bazan bayar ba”
“Allah sarki baby, nasan kukan zata cigaba, Dan Allah kabani in rarrasheta”
“Aiko sedai ta mutu, in seka rarrasheta zata dena”
“Shikenan zan ramane”
Haka suka tafi Gida suna tafe suna fad’a
Memakon Jalal ya kaisu Gida se ya canza hanya
“Ina kuma zamuje”
Jawwad ya tambayeshi
“Yunwa nakeji ice-cream kawai zan siyo ko fura”
“Kwadayayye kawai”
“Eh naji kwadayayyen ne nasan duk haushina kake ji Dan na hanaka waya, kuma bazan bayarba”
Yasa hannu ya dau wayar Jawwad, ya bar wayoyinsa sabuwa da tsohuwar a cikin mota ya bude motar ya fita

Dan murmushi Jawwad yayi
Jalal kaima ai rigimammen ne
Jawwad ya furta hankali

Jeje tun dazu se trying lambar JALAL yake amma baya shiga
Yanzun ma kuma trying yayi by luck wayar ta shiga
Jawwad dake kashingide a cikin mota yaji wayar Jalal tana ringing da ya duba ba suna ya daga yasa a kunnensa ba sallama ba komai Jeje yafara magana
“Ina ka shigane tun dazu nake kiran wayarka amma yaki shiga”
“Sorry ba shi baneba wayarsa ce ta Dan samu matsala”
Jeje yagane muryar Jawwad amma alamu ya nuna shi Jawwad be gane shiba Dan da ya ganeshi baze daga wayarba ma
“OK Dan Allah yana ina yanzu”
“Mun Dan fita dashi, yanzu muna kabuga ya Dan fita ne yanzu zamu karasa Gida insha Allah”
“OK nagode”
“Wa zance masa?”
“No bakomai zan kuma kira”
“OK”
Jawwad ya katse kiran

Jeje ne ya kira Hannah a waya
Bugu biyu ta dauka
“Ya”?
” ke kin ban wahala gaskiya tun dazu nake kiransa a waya se yanzu na same shi a waya, shima ba shi ya daga ba mayensa ne ya daga wai wayar Jalal dince ta lalace, sun Dan fita yanzu zasu koma Gida”
“Au nice ma nasaka wahala kamanta aikin naka ne?”
“Hakane fa tuba nake me idon zinari”
Murmusawa Hannah tayi
“Weldon yanzu kuma zanyi nawa aikin, zan Dan jefa masa fargaba a zuciyarsa”
“Meye shirin naki?”
“Ba ruwanka kai dai zuba ido”

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button