ABDUL JALAL PART 1 HAUSA NOVEL

Jawwad yafara gajiya da zaman jiran Jalal
“Kome ya tsaya yi oho”
Jawwad yai maganar tareda duba wayar Jalal don ganin lokaci message ne yake shigowa wayar
“Yau kaki daga wayata, ka jefa Zuciyata cikin matsala, ko Abinci nakasa ci dan haka Kaima zan saka taka zuciyar a damuwa Ina hanyar zuwa gidanku
Zakazo ka sameni a gidanku
Cikin dakinka, kuma komai
Ze iya faruwa in aka ganni a
Dakinka, in baka son hakan
Ya kasance mu hadu a
Restaurant din damuka hadu
Da farko mintuna goma sha
Biyar kawai kake dashi
From your lovely bae
(Hannah)
Wannan wace irin jaraba ce, haka Jalal yai maganar hankalinsa a tashe, bayaso sunan Jalal ya kuma baci, da sauri yayi dialing number da aka turo message din da ita amma taki dagawa,
Yasalam Jalal ina ka tafine ana shirin jefaka cikin matsala
Daren ranar ma Jalila batayi ishashen bacci ba ko abinci taki sakin jiki taci, Ummi se rayuwarta take ita kadai ba tare da ta shiga sabgar Jalila ba dukda a cikin zuciyarta bata jin dadin abinda takewa Jalilan amma yazama dole ta nuna mata bacin ranta akan abunda Jalilan takeyi
Washe gari da safe Jalila haka Jalila ta shirya ta tafi makaranta, tana zuwa yan ajinsu yan son jin gulma sun so su tambayeta yadda akayi amma ba fuska ta hade rai se muzurai take, suna tsoron su tambayeta suma ta juye musu kwandon bala’i
Mummy Hanan dakanta tare da wasu sojoi Guda biyu suka kawo Hanan makaranta cikin wata CRV me tint glass, sojoji guda biyu na gaban motar, sun dan jima a kofar makarantar koza suga wucewar Jalila amma basu ganta ba daga baya, mummy tace Hanan ta shiga school ita tasan abunyi
Tsakanin Jalila da Hanan ba Wanda ya kula wani, duk yanda yan aji sukaso jin gulma basu samu dama baa
bayan tafiyar Hanan ba dadewa sega malama ramatu an sauketa a napep zata shiga cikin makarantar
Dan sauke glass mummy Hanan tayi
“Sannu dai”
Mummy Hanan tafada cikin ISA da iyayi
Malama ramatu na ganin mota
Ta washe baki da durkusa
“Yawwa sannu madam ina kwana”
A dan wulakance mum Hanan ta amsa
“Yawwa lafiya, if u don’t mind please I have an issue to discuss with you”
“A a ba wata damuwa, madam ina jinki”
Alama tayiwa malama ramatu data shigo cikin mota
Ba tayi tunanin komai ba ta shiga
Mummyn Hanan ta numfasa
“Da alama kema staff ce a school din nan ko?”
“Yea of course”
“Good, kinsan case din da akayi a school din nan da akayi fada tsakanin dalibai biyu aka daki yarinya Yar gidan captain rasheed “
Se a lokacin malama ramatu ta kalli suwaye a gaban motar taga sojoji nan take ta sha jinin jikinta
“Emm…e..eh nasani madam amma wallahi bana gurin akay….”
“Inma kina gurin ke kikasani tambayarki zanyi kikamin karya, zaki gane kurenki ne”
“Zanma fadi gaskiya wallahi”
“Wacece Jalila Aliyu Imam Yar uban waye ita?”
Nan take malama ramatu ta karkace ta dinga rattaba bayanin karya da gaskiya
“Ba Yar uban kowa bace ba, a sanina ma bata da uba, amma naji ana wai ya mutu ko karya akema ohoo, daga ita se uwattta suke zaune baata da wani gata, se tsabar iskanci da Neman rigima”
Haka taita zuba, kaman ruwa ba comma ba full stop
“Ke surutun ya isa haka bani address din gidan su”
Malama ramatu ta bata address
Maman Hanan Tabawa malama ramatu 5k a wulakance sukaja mota sukayi gaba
Kuma trying lambar Hanna Jawwad yayi da wayar Jalal
seda taja aji, azatonta Jalal ne sannan ta daga cikin yanga tafara magana
“Baby lokacinka ya fara karka dauka da wasa nake wallahi dagaske nake in samu haduba gidanku zanje”
“Amm Hanna ba JALAL bane nine Jawwad dan Allah karkiyiwa Jalal haka, dama yan anguwa sun samasa ido, yanzu in kikayi haka zaki kara bata masa suna kisa akuma tsanarsa dan Allah karkiyi haka duk abun Jalal baya bin mata kuma mahaifinsa yana gari in ya ganki bazeji dadi ba”
Nisawa Hannah tayi
“Jawwad dan uwanka yafiye taurin kai yaki karbar bukata ta, gara in biyo masa ta inda yakamata, mintuna sha biyar ne kacal daku, in bakuzoba wallahi zanyi shigar danaga dama ince karuwarsa ce ni kuma har Gida xanje, ko dayake nasan hakan ba lallai yabata masa ba but at least ze gane da gaske nake, ganinsa kawai nakeso nayi in samu sauki a raina, zabi ya rage naku dan uwa na gari”
Ta kashe wayar
“yasalam wannan wane irin abune, Allah ya fidda kai sharrin wannan yarinyar Jalal, ohhh gara muje mu sameta karta bishi Gida daddy bazeji dadi ba dama ga yan unguwa sunsawa Jalal ido, inaga kuma aga karuwa taje gurinsa “
Jawwad ne Ya bude motar da sauri ya fita Neman Jalal
Ko islamiyya Jalila ba taje ba, kuma Ummi batace ta shirya taje ba, ta kyaleta idonta duk ya kumbura saboda kuka
“Allah sarki baby na banajin dadin ganinki a haka amma kedin ce Zuma seda wuta, gara in horaki” Ummi tayi maganar a zuciyarta
Da yamma likis su Jalila sukaji tsayuwar mota a kofar Gida, Jalila tana tsakar Gida ta zurawa Ummi ido kaman bata Santa ba, Ummi tanaa shan fura,
Cikin izza sukaji sallama
Ummi ce ta amsa sallamar tare da jiran shigowar Wanda yayi sallama
Jalila tana zaune bata amsa sallamar ba balle ta motsa daga inda take,
“Sannu da zuwa shigo”
Ummi tayi maganar tana mikewa tsaye bata gane matar ba tayi zaton irin customers dinta ne
“Ba zamane ya kawoni ba”
“To lafiya meyafaru?”
Ummi ta tambaya
“Nasan baki sanni ba nice Hajiya Safiyya Mrs. Captain Rasheed “
Da sauri Jalila ta daga kai tayi arba da Hanan da mamanta
Maman Hanan ce ta janyo hannun Hanan
“Kalli duba ta’addancin da y”arki tayi kina tunanin kunci bulus ne?”
Gaban ummine ya fadi da taga Hanan
Share please
More comments more typing…………
Ina alfahari da masoyana da masu yi min addua ina godiya ❤❤❤
Masu bukatar shiga group dina akwai link din group din Asama amma akwai dokoki
????️????️????️????️????️
[9/12, 6:02 AM] +234 816 830 7871: ????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????
_ABDUL JALAL_
(2020)
_ STORY & WRITTEN BY AISHAHUMAIRA_
(Daddy's girl)
PAGE- 26
PART 1
_Bismillahir Rahmanir Rahim, da sunan Allah me Rahma me jin kai, Allah ka yi salati a bisa shugaban mu Annabi Muhammad (salallahu alaihi wassalam)
Bayan haka, ban rubuta wannan littafi domin cin zarafin wani ko wata ba, na yi shine domin nishadantarwa, da kuma wa’azantarwa, ku biyoni domin jin me wannan labarin ya kunsa.
Yanda nafara Allah yabani ikon kammala shi
Ina maraba da shawarwari, sharhi, ko kuma gyara, nagode.
Domin Samun karanta wannan littafin yi magana ta what’s app akan wannan lambar
07063065680
Kokuma addanna wannan link din domin samun novel din
????https://chat.whatsapp.com/EtB4KI52K0v5FQc2ELhidL
Gaskiya comments nakeso ba sticker ba kokuma Just thanks in bahaka ba zan dena typing kullum
Special thanks to my group members ina Alfahari daku comments dinku na bani karfin gwiwa
-MY FIRST NOVEL-
Wani mugun kama Ummi taga Hanan tanayi da Jalila, ciwon goshin Hanan ta kalla
“Eyya kiyi hakuri ai munje makaranta akan case din, mun bada hakuri, babanta yace komai ya wuce kiyi hakuri Dan Allah”
“Keda kinsan da bada hakurin kika haifi Yar da bata da tarbiyya, kika haifi yarinyar Datafi karfinki ni na dauka ma Yar wata hamshakin ce Ashe ba Yar uban kowa bace face Mara galihu?”
“Duk me ya kawo wannan maganar, haba ke kuwa Jalila tana da tarbiyya rashin ji ne kawai na yara, kuma batun gata kowa gatansa Allah,”
Wani abune yakawo wa Jalila iya wuya motsa baki tayi da niyyar rashin mutunci cikin tsiwa sukayi ido hudu da Ummi seta hadiye maganarta tayi shiru
“Da wallahi niyyata ubanta zansa akoyawa hankali in yaso gobe yabawa yarsa tarbiyya ya banbance mata matsayin yayan gata da marasa galihu”
“Kar a kuma sakomin uba, a barshi ya kwanta cikin aminci a kabarinsa, ni nayi laifi ba shiba”
Jalila tayi maganar tana jujjuya idanu
“U see mummy wannan yarinyar bazata yi nadama ba memakon tabaki hakuri rashin kunya zatayi miki, in bakiyi Sa a bama zaginki zatayi, kawai kisa a dauketa a je a horata”
Hanan tayi maganar tana kallon Jalila
Da yarabanci Ummi tayiwa Jalila magana, Jalila ta yamutsa fuska ta Dan kara hade rai
“Naji yata ba Yar uban kowa bace bamu da gata se Allah mu bamu su arziki bane, amma kiyi hakuri batun a dauki Jalila a horata be taso ba, bazata karaba”
“Tsiyar talaka kenan ko ince matsiyaci, ya dakko abunda yafi karfinsa, karshe yazo yana karya murya,”
Ta maida idonta kan Jalila
“Kekuma kinci Sa a da ubanki zan Sa akama, wannan uwataki ce ma tabani tausayi, ba dan haka ba da sena Sa an sauya miki halittu, kibari kitaka wani matsayi kisamu me tsaya miki in kinyi rashin mutunci, a yanzu dabaki da galihun nan wahala zaki sha Mara tarbiyya kawai”
“Nice ma ke saboda rashin tarbiyya kuma kar……
Jalila ce tafara magana ummi ta dakatar da ita
Ummi ta kalli mummy Hanan sannan tace,
” nace kiyi hakuri ko, se magana kike akan gata se dai ko nan gaba amma a yanzu dai banajin kinsamu gatan dana samu a rayuwata, sannan yata ba Mara galihu bace ba, da gatan ta, daliline yasa kiga ganmu a haka, amma bazan gazaba Allah yabaki hakuri”
Tsaki mum Hanan tayi taja Hanan suka fita, ga magana fal abakin Jalila amma Ummi ta hanata magana,
Wata kwallar bakin ciki ce ta taru a idon Jalila, meyasa Ummi ta hanata magana daki ta wuce ta kyale Ummi a tsakar Gida