ABDUL JALAL PART 1 HAUSA NOVEL

Ilham ce take ta kaiwa tana kawowa a dakinta tana tunanin me yakamata tayine, dan tayi Alkawarin fitinar Jalal tako ina bazata bari yafara soyayya da wata banza ba, ba itaba Dan hakan dai² yake da rushewar shirinmu ana samun kuskure komai ze lalace, dabara ce ta fado mata
Dan haka gaban mudubi taje ta zauna, ta fara shafa mayuka a jikinta, tareda fara tsara simple make up a fuskarta, dogon wando tasaka skin tied se wata karamar Riga body hook, ta dakko wannan turaren ta shafe jikinta da shi, parking din gashinta tayi ta Dan Dora mayafi akanta ta nufi hanyar fita
Jeje ne yakawo Jalal gida a buge part dinsa ya kaishi ya kwantar da shi
Jawwad da yake kofar gida yaga wucewar motar Jalal koba a gaya masa ba yasan Jeje ne yakawo Jalal, kuma ba makawa a buge yake, girgiza kai Jawwad yayi cikin bacin rai yakoma cikin gida
Bayan jeje ya kwantar da Jalal ne yazo fitowa daga part din Jalal sukayi clashing da Ilham
“Wow so cute, common beb u look so beautiful”
Jeje yai maganar yana mata wani shedanin kallo
“Kai kashiga hankalinka, ka kiyayeni, bani hanya”
“Meyasa kikeso in baki hanya me zakije kiyi masa? Gaskiya na kyasa ya za ayine?”
Wani mugun kallo Ilham tayi masa
“Eh kaman ba gidan ubanka bane nan, meye na tambayata me zanyi masa kai me kayi masa, ka kiyayeni ka fita hanyata, niba Sa arka bace sakarai kawai”
Ta hankade Jeje ta wuce ajiyar zuciya Jeje yayi “gaskiya yarinyar nan ta hadu I have to do something”
Yasa kai ya fice, Ilham har cikin bedroom din Jalal ta shiga ta ganshi kwance yayi dai² akan gado yana bacci. Murmushi Ilham tayi ta shiga cikin dakin ta samu gefen Jalal ta zauna hannu tasa ta Dan shafa sajensa zuwa cikin sumarsa
Dan jijjigashi take
“Yaya Jalal wake up please”
Share please
More comments more typing…………….
????️????️????️????️????️
[9/12, 6:02 AM] +234 816 830 7871: ????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????
_ABDUL JALAL_
(2020)
_ STORY & WRITTEN BY AISHAHUMAIRA_
(Daddy's girl)
PAGE- 27
PART 1
_Bismillahir Rahmanir Rahim, da sunan Allah me Rahma me jin kai, Allah ka yi salati a bisa shugaban mu Annabi Muhammad (salallahu alaihi wassalam)
Bayan haka, ban rubuta wannan littafi domin cin zarafin wani ko wata ba, na yi shine domin nishadantarwa, da kuma wa’azantarwa, ku biyoni domin jin me wannan labarin ya kunsa.
Yanda nafara Allah yabani ikon kammala shi
Ina maraba da shawarwari, sharhi, ko kuma gyara, nagode.
Domin Samun karanta wannan littafin yi magana ta what’s app akan wannan lambar
07063065680
Kokuma addanna wannan link din domin samun novel din
????https://chat.whatsapp.com/EtB4KI52K0v5FQc2ELhidL
Gaskiya comments nakeso ba sticker ba kokuma Just thanks in bahaka ba zan dena typing kullum
Special thanks to my group members ina Alfahari daku comments dinku na bani karfin gwiwa
-MY FIRST NOVEL-
A hankali ya bude idonsa da sukayi jawur, saboda buguwa ya mayar ya lumshe sannan ya fara magana a cikin mayae
“Ni wannan yarinyar bana sonta, narasa meyasa Jawwad yayi min hakane, nace masa bana so amma shi……se wani”
Sekuma yayi shiru, Ajiyar zuciya Ilham tayi tace”munafukan banza daga Jawwad har kanwar tasa, zasu gane kurensu
Matsawa takuma yi ta kwanta a jikinsa sannan ta Dan dago ta kalleshi
“Meyasa baka sonta”
“Mtseww nifa bana son tambaya, bana sonta kawai bata da hankali,” ya Dan girgiza kai ya yamusta fuska warin turaren nan yaji da yabaya so
“Itakuma Ilham meyasa baka sonta?”
Dan bude ido yayi ya mayar ya lumshe”wannan fa kanwata ce, meyasa zanyi wani soyayya da ita, kanwata ce kawai”
Shigewa jikinsa ta kumayi sosai
“But I love you, karkayi soyayya da wata bayan ni, Ilham ce kawai take sonka, sauran duk bamasu kaunarka bane, Ilham tana sonka kaima kasota kaman yadda take sonka”
Dukda yana cikin maye setaga yayi murmushi”ka yadda zakaso Ilham”
“Bacci nakeji ki kyaleni da wannan mafarkin”
“Mafarki kake?”
Ya gyda mata kai “ya kusa faruwa a zahiri”
Tai maganar tana shafa gashin kirjinsa ya mutsa fuska yayi ya rike mata hannu”kidena bana so”
“Meyasa bakaso?”
Shiru yayi be ce mata komai ba
“Shikenan tunda bacci zakayi bari in tafi,”
Durkusowa tayi da nufin tayi kissing dinsa se ya juyad da kansa alamun baya so, kallonsa tayi
“Why?”
“Ki tashi ki bani guri nace miki bacci zanyi”
Gabanta ne ya fadi dataji yayai normal magana ba tare da maye ba, kallonsa tayi taga ya bude idonsa fes akanta, sekuma ya mayar ya lumshe yacigaba da bacci Ajiyar zuciya tayi tare da fading”Allah ya temakeni na dauka giyar tasakeshi ne”
Kissing dinshi tayi akan lips dinsa sannan ta mike ta fita ta nufi cikin Gida, me gadi ya hango fitowarta daga part din Jalal
“Kai me yarinyar nan take a bangaren yaron nan a wannan tsohon daren,
Allah ya kyauta bayan shan giya kuma yafara biye² mata, abun kunya kuma da kanwarsa Allah ya shirya”
Da safe Jalila tanata shirin makaranta, wata makwabciyarsu bata wuce sa ar Jalila ba ta shigo tacewa Ummi Dan Allah ta sammata abunda ta girka ita tayi girkin takasa ci dayake tsohon ciki ne da ita
“Allah sarki hawwa’u Allah yaraba lafiya bari azuba miki
Jalila zubomata abinci”
Jalila kam zuwa yanzu Hawwa haushi take bata gani take tsabar kwadayine da iskanci komai bazata iya Ciba sena gurin ummi, Ummi kuma bata taba hanata ba ko kyararta
Jalila tana zumbura baki taje ta zubomata dataga ummi bata kallonta ta dungurar mata da kwanon da kayan tea
“Gashi nan kwadayayyiya seki hada Sa kanki niba Yar aikinki bace”
“Eh naji kwadayaiyiyyar ce ke in naki yazo maga yadda zakiyi”
“Bawani nan komai kidorawa ciki, dayana da baki se yace karya kike masa”
Dariya Hawwa tayi ta hada abincinta ta fara ci suna hira da ummi tana gama ci ta kama aman abincin nan dataci seda ta amayar tsaf
“Kai kekam kin banu sekace akanki aka fara ciki ga rakin tsiya ni bari in bar gidan nan tun kafin nima kisani aman”
Jalila tai maganar tareda daukar jakar makarantarta tayi waje
Girgiza kai ummi tayi indai Jalila ce bazata canza ba
Wajen karfe Tara sannan Jalal ya tashi daga nannauyan baccin da yayi kansa yana ciwo, jiyayi yana warin turaren Ilham tsaki yaja yafara tunanin abunda yafaru wannan wane irin sha³ mafarki yayi kuma ma da Ilham (shi a zatonsa abunda yafaru mafarkine)
Mikewa yayi yaje yai wanka ya fito yayi sallar asuba karfe Tara na safe
Jalila tana kokarin shiga makaranta taji ana tayimata horn bata waiga ba ta koma gefe akakuma tahowa inda take a fusace tajiyo tana masifa
“Wai meye hakane anyi Horn na canza hanya ankuma biyoni if you like bi ta kaina komawaye”
Bude motar yayi ya fito tana dariya Allah yabaki hakuri Yar baba,
Yayan Hanan ne Abdallah yakawo Hanan makaranta murmushi Jalila tayi
“Au ai bansan kai bane ina kwana”
“Lafiya kalau ya mamanki”
“Tana lafiya”
Juyawa yayi ya kalli motar yace”ke Hanan fito mana kin wani Zauna a cikin mota”
Sannan ya dawo da kallonsa kan Jalila “Yar baba kaman kuwa kinsan daddy yace agaisheki har yabada sako abaki”
Hanan ya kalla wadda se wani cika take tana batsewa
“Hanan bani sakon nan”
A wulakance ta bude Jakarta ta miko masa wata Leda
Ya karba yabawa Jalila
“Kai amma nagode sosai Yaya Abdallah ka cewa baba Yar baba ta gode, Allah yasaka masa da Alkhairi yabashi abunda yake nema duniya da lahira, Allah yabashi ladan kyautatawa marainiya”
Ba Karamun burge Abdallah tayi ba,”zangaya masa insha Allah”
Tsaki Hanan tayi ta wuce abunta cikin school, Jalila ma cikin makaranta ta shige, duk zafin kan Hanan bata kuma kallon seat din Jalila ba balle takuma sha awar zama a gurin,
Zama Jalila tayi ta dakko abunda akabata chocolates ne kala² a ciki murmushi tayi gaskiya mutumin nan yana da kirki
Bayan anfita break Jalila taje seat din Hanan ta zauna a kusa da ita kawata ya kike
Wani mugun kallo Hanan tayi mata ta dauke kai, bude chocolate dinta tayi tafara sha sannan ta kalli Hanan kawas
“Bismillah”
“Abun ya fito daga gidanmu sannan kice insha ke dai da kike kwadayaiyiyya seki sha dama Dan talaka akwai iya shishshigi,”
Murmushi Jalila tayi sannan tace “duba ajin nan akwai yayan Wanda sukafi mahaifinki dukiya, amma abun be baki mamaki ba ina Yar talaka amma nake makarantar yayan attajirai kaman Hanan rasheed, ashema Baku wani Tara ba tunda har Yar matsiyata kamar Jalila Aliyu take a irin makarantar Ku”
Mike kafa Jalila tayi ta Dora a saman bencin
“In ana batun gata Hanan, be kamata kisaka baki ba, Dan baki da gatan da Jalila take dashi”
Jalila se gayamata bakaken maganganu take tana shan chocolate dinta, Hanan tana fargabar ramawa saboda gani take Jalila bata Risina ba zata iya maimaita mata abunda tai mata amma duk da haka ta dake tana ramawa