Uncategorized

ABDUL JALAL PART 1 HAUSA NOVEL

Jalila tabi bayan JAWWAD da kwanukan abinci zuwa part dinsa, oga Jalal yana zaune yana kallo sekace dakinsa, Jalila ta ajiye kayan abincin tareda fadin “wash” JAWWAD ya Dan kalleta “kai baby har kin gaji”
“Niba gajiya nayiba”
“Hmm dagaske?”
“Eh mana”
“OK tunda bakgajiba serve us”
Seda ta kalli Jallal ta Dan hade rai
Ta dau plate tayi serving Jawwad, ta kalli JAWWAD “sekuma me?
“Baby Jalal fa, serve him too”
Yamutsa fuska tayi
“Ni na gaji”
“No Jalila, kefa kikace Baki gaji ba, hakan ba halinki bane”
Kafin tayi magana Jalal ya taso daga inda yake cike da gadara, yasa hannu ya dauke plate din gaban Jawwad da Jalila tayi serving din Jawwad, ya dau spoon ya samu guri ya zauna, ya fara cin Abincinsa

Bayan sun fitane yaseera ta kalli Ilham
“Tab wai yanzu kina nufin wannan itace budurwar JALAL din”
“Hmm gata nan kin dai ganta ko?
” ai ko ta hadu”
“Kamarya ta hadu, kinsan dai na fita kyau ko?”
“Ke dalla wayake ta wani kyau Ilham, duk kyanki akwai qualities din da in kika rasa, to kyan yazama shirme, banda abinki ma dame kika fita, hasken fatarne kawai amma wallahi kyakykyawa CE”
“Au yaseera hakama zakice dame ta fini?”
“Kallifa mu matama kalli da yadda take mana magana INA ga in agaban namijine, gashi ta iya iyayi da siyasa, kincemin fada kuke, amma dukda munzo tare kalli yadda ta mutuntani, gata Yar gayu”
Ilham ta hade rai sosai sannan tace
“Ni duk ban iya wannan abubuwan ba kenan?”
“Bahaka bane ba, amma kin San meyake cutarki”
Ilham ta girgiza kai
“Rashin hakuri, saurin fushi, ga garaje, gaki da sakaci, kinga in bakiyi dagaskeba akwai matsala kina ganin yanda take wani juya ido in tana magana”
“To yazanyi yaseera,?”
“Waima tukuna naji yayan Nana yana batun akai musu abinci shida Jalal, Abincin ma ita take kai musu”
“To inaga ita take kaimusun mana” Ilham tai maganar cike da damuwa
“Cab wato ita take kaimusu abinci, lallai ILHAM da sauranki, gaskiya akwai tendency na JALAL yafara soyayya, kuma abinda kike gudun yafaru”
Ilham ji tayi kaman ta Dora hannu a ka ta fashe da kuka
“Yaseera ya zanyi, nikam indai nabari shirin mami ya rushe batareda ta dau fansar nan ba nayi asara
Wallahi yaseera se yanzu nagane son gaske nakewa Jalal, wallahi zan iya komai akansa”
“Kina wannan sakalancin zaki iya komai akansa? Malama ki dage Dan wallahi wannan yarinyar da bariki zatayi zata Tara abun duniya,
Yanzu ki saurareni, batun kice kin gaji be taso ba, duk masifar daze miki kidena zuciya da shi, sannan kidena jin tsoransa, sannan kidinga kokari kema kina dafa abinci ki bashi, in wataran beci ba wataran zeci”
Ilham ta Dan girgiza kai
“Yaseera gani kike shawo kan Jalal abune me sauki ko? Mugun Dan taurin Kaine, ga shi jarababbe, yaseera tsawon shekarun nan danayi a gidansu ko inda yake bayaso inje, am about to give up”
“Ita Jalilan dayake daga mata kafa ba mace bace kamarki, iya bariki kawai tafiki, ki bar wani batun seya soki malama kawai ya aureki a wuce gurin”
“To yaseera insha Allah zan kuma jajircewa, Wallahi nida zuciyata tafara bani kawai inyi duk me yiwuwa kawai inyi me gaba daya”
Da sauri yaseera ta kalleta
“Baki da hankaline? Inkuma aka samu akasi fa”
“Nima abunda yasa nafasa kenan”
“Karki kuskura ki fara, kibi komai a hankali”
“To shikenan yaseera, zan cigaba da kokari”
Haka yaseera taita zigata sannan sukayi sallama, Ilham ta shiga Gida yaseera kuma ta tafi
Hannah ta kira wayar Jalal harta gaji dama seyaga dama yake amsa wayarta, yau ta kudurce wa ranta kome ze faru sedai yafaru Dan Gida zata bishi, lokaci yayi da yakamata tafara wasan kwallo dashi daga shi har kanwar tasa dole sugane wace Hannah,

Jalila bin Jalal tayi da kallo, wannan akwai Dan rainin hankali, shima Yaya Jawwad sekace Jaraba kowa da gidan ubansa ya zauna a can amma shi inbe bishiba shi ze biyo shi, a ranta tace kacigaba zan rama ne wannan wulakancin da kakemin bakaci bulus ba
A zahiri kuma ta ba sar ta kuma serving din Jawwad
“Yawwa Yar Baby, mungode sosai”
“To yayan Baby, permit me to leave”
“U can leave dear”
Tana komawa cikin Gida Maama ta kuma aikenta gidansu Jalal, waita karbo kaya anjima wasu customers zasuzo tun safe Jalila take aiki bata huta ba gashi bata son abunda ze hadata da Ilham, ba tayi musu ba ta juya ta kuma tafiya aiken da akayimata,
Tana fitowa taga wata mota a tsaye a kofar gidansu Jalal, harta gifta mortar, aka danyi reverse da motar saitin inda Jalila take, sauke glass din motar akayi wata matashiyar budurwa ce a cikin motar
“Sannu dai” tacewa Jalila
“Yawwa sannu”
“Dan Allah tambaya nake”?
” Allah yasa nasani”
“Naga kamar cikin gidan nan zaki shiga”
“Au kamace baki tabbatarba”
“Ohh sorry Dan Allah Jalal nake nema”
Kallonta Jalila tayi, tayi nazarinta na wasu yan mintuna sannan tace
“Me Jalal ze miki”?
” inason ganinsane”
“Baki da lambarsane?”
“Nakira bata shiga”
“Injiwa zance masa”?
“Kawai kice masa yayi bakuwa”
“Bahaka nakeba, inkina son ganinsa kifadi sunanki”
“Hannah ce, koke ce Ilham din da Jawwad yake gayamin kanwarsa da kike sonshi”
Da sauri Jalila ta kalleta, ta Dan kuramata ido wasu yan mintuna sannan tai murmushi
“Hannah”
Jalila ta maimaita
“Yeah I am Hannah”
Jalila ta kuma murmushi
“Zata iya yuwuwa nice Ilham kuma zata iya yuwuwa bani baceba, for now bazaki ga Jalal ba ki tafi kawai inma kin tsaya bazan bari ya fitoba, kune masu kara ingiza lalacewarsa, kalleki, kalli shigar jikinki a matsayinki na ya mace kina yawo half nicked, kinzo gurin namiji saboda abun kunya, me kike tsammani in mutane suka ganshi da ke, kibari in yaje inda kuke haduwa kya Ganshi amma ba anan ba, juya kikoma inda kika fito” Jalila ta hade rai tareda nuna mata hanya

Share please
More comments more typing…………………….
Masoyana abun alfaharina comments dinku yana kayatar dani Allah yabar kauna

????️????️????️????️????️
[8/31, 8:30 AM] Safiyya: ????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????

_ABDUL  JALAL_
       (2020)

  _ STORY & WRITTEN BY AISHAHUMAIRA_
(Daddy's girl)

           PAGE- 37

PART 1
Share please

_Bismillahir Rahmanir Rahim, da sunan Allah me Rahma me jin kai, Allah ka yi salati a bisa shugaban mu Annabi Muhammad (salallahu alaihi wassalam)
Bayan haka, ban rubuta wannan littafi domin cin zarafin wani ko wata ba, na yi shine domin nishadantarwa, da kuma wa’azantarwa, ku biyoni domin jin me wannan labarin ya kunsa.
Yanda nafara Allah yabani ikon kammala shi

Ina maraba da shawarwari, sharhi, ko kuma gyara, nagode.

Domin Samun karanta wannan littafin yi magana ta what’s app akan wannan lambar

07063065680
Kokuma addanna wannan link din domin samun novel din

????https://chat.whatsapp.com/EtB4KI52K0v5FQc2ELhidL

Special thanks to my group members ina Alfahari daku comments dinku na bani karfin gwiwa
ABDUL JALAL NOVEL FANS
Love u all guys ❤❤❤❤❤

      -MY FIRST NOVEL-

Karewa Jalila kallo tsaf Hannah tayi, ta tabbatar Jalila Sa ar kanwarta ce, badan kartayi karyaba setace kanwa ta biyu ma, bude motar tayi sannan ta fito ta kalli Jalila sama da kasa, ta danyi murmushi sannan tace
“Ni kike kora kike cewa in tafi in bar nan gurin”
“Au tambayata ma kike, lallai na fuskanci saboda irinku ake double period a class, saboda ba kwa dauka a daya”
Mamakine yacika Hannah, tace
“Bari in gaya miki wani abu dabaki saniba ni…..
Jalila ta dakatar da ita ta hanyar daga mata hannu tareda fadin
” NO need saboda babu wani abu me amfani ko me mahimmanci Wanda ze amfaneni dazaki fada, as I said it before, kibar nan gurin in ba hakaba zan baki mamaki”
“Ni Hannah zaki bawa mamaki”
“Kwaraikuwa kedin”
Nuna Jalila tayi da Dan yatsa zatayi magana, batayi maganarba Jalila tasa hannu ta sauke yatsan Hannah
“Duk wata magana muyita amma ba a nunani da Dan yatsa, daga haka nagama magana dake, nabarki lafiya, inkin gadama kicigaba da tsayuwa”
Jalila na zuwa nan a zancenta ta shige gidansu Jalal tabar Hannah tsaye sororo tana mamaki
Jalila ta shiga cikin gidan da sallama, Ilham tana palourn tana danna waya tayi mata banza, Jalila ta kuma nanata sallama amma Ilham mirsisi taki amsa sallamar Jalila
Karasawa Jalila tayi tasa hannu ta fizge wayar hannun Nana
“Haba kekuwa, kome nayi miki a rayuwa be kyautu inyi sallama kimin banza ba”
A fusace Ilham ta kalleta
“Bani wayata malama”
“Kiramin mummy, seki karbi wayarki”
“Ke kin isa kisani aiki,”
“Ban isaba alfarma na nema”
Sannan ta bawa Ilham wayarta,
Ana haka mummy tafito da alama unguwa zata fita
Suka gaisa da Jalila, Jalila ta gayamata Aiken da akayi mata, mummy tace taje yanzu fita zatayi in ta dawo zata aiko,
Da haka Jalila ta fito ta tafi gida,.data fito ta tarar Hannah ta tafi, Jalila a ranta tace kin kyautawa kanki dakika tafi ai
Hannah tana barin gurin takira wayar Jeje ta tambayeshi ina zasu hadu yagaya mata, ta nufi gurin kai tsaye, tana zuwa ko tasameshi a can, yanayin fuskarta kawai ya nuna masa akwai matsala, saboda yadda take huci
“Me idon zinare, lafiya kuwa”?
” ina fa lafiya, gidansu Jalal naje, saboda yan kwanakin nan baya daga wayata, naje nasamu wata a kofar gidansu, wata yarinya taci min mutunci”
“Kamarya taci miki mutunci, miye hadinki da ita?”
“Ina kyautata zaton itace budurwar tasa, da Jawwad yake fada Ilham take kowa, hada cewa bazata bari ya fito ba, sedai injira muhadu inda mukasaba”
“Jalal din, to karya takeyi barazana ce kawai, uwar da ta haifeshi ma bata isa ta hanashi abinda yyi niyya ba, balle wata Ilham, gayen da soyayya bata gabansa, kema kinciri tuta ne da yake sauraronki, amma ya akayi kika San Ilham dince”?
“Na tambayeta amma ta rainamin hankal, Amma nayi mamaki, yanda nake zaton Ilham din na dauka wadda zanyi maganice a take amma naga itama a tsaye take Dan bata da kunya”
Dan shiru Jeje yayi sannan yace
“Tabbas Ilham ma masifaffiya ce amma bana tunanin ta kai yadda kike fada haka”
“Hmm, bakaga wulakancin datayi minba kuma na girmeta, sena raina rashin kunyata Dan fafur hanani magana tayi, mamaki da takaici suka cikani”
“Gaskiya Hannah kin bani kunya duk bakin naki, kinsan a duniya Jalal ya tsani mace ta dinga juyashi”
“Ba a nan takeba Jeje hausawa kance yaki Dan zamba ne Dan haka, zan nuna mata duk Wanda yarigaka kwana ze rigaka tashi, idan takamarta rashin kunya, nikuma takamata bariki, zan daga shi har ita zan basu mamaki”
Jalila ta sanar da Abba zuwan captain Rasheed da yayansa domin kawo musu ziyara, Yaya farinciki sosai da jin haka, Jalila ji take kamar ta janyo ranar Saturday su Hanan suzo, se murna takeyi
Daren yau dai Jalal yasaci jiki ya tafi gurin shan giyarsa, yaje babu dadewa be fara shaba, mayyar tasa tazo wato Hannah, tazo ta nemi guri ta zauna tai shiru batace komaiba
Ya Dan kalleta, yanayin fuskarta ya nuna tana cikin damuwa,
“Ya akayine sarkin matsala, mekuma ya faru?”
Ta dago ta kalleshi, tayi kalar tausayi sannan tace
“Jalal kwana nawa ina kiranka kaki ka daga wayata, naturomaka messages kaki reply haba Jalal, gashi aka cimin mutunci saboda kai, yakamata ka tausayamin”
“Ya akayi aka cimiki mutunci sabodani?”
“Kanwarka mana”
“Wake nan?”
“Wace kanwar kake da ita, banda wadda Jawwad yacemin tana Sonka?”
Shiru ya danyi yana kallon Hannah, tacigaba da magana
“Ranar nakiraka baka dagaba, ita ta daga ta min rashin mutunci ni kana cemin Mara kamun kai amma me kanwarka take a gurinka shabiyun dare, har tana gayamin bacci kake ta zageni hadda cemin mayya”
Shikam Jalal kasa cewa komai yayi se ido da ya zuba mata,
“Har yanzu ni banga cin mutuncin dakike fada tayi miki ba”
Kallonshi tayi
“Au hakama zakace? Metakeyi a gurinka shabiyun dare harta daga wayarka?”
“Meye kuma na bin diddgi ina ruwanki dame take a gurina shabiyun dare?”
” haba Jalal,Yauma nakasa jurewa da rashin ganinka Dan haka naje gidanku, na hadu da ita a kofar Gida daga tambayar kana ina ta dinga zagina
Harda cewa baka isa tahanaka abu kayi ba Dan haka bazata bari ka fitoba, saboda baka tsallake maganarta, tana juyaka yadda taga dama, haka ta dinga fadar maganganu, abun ya dauremin kai”
Dan dagowa yayi da sauri
“Inji Ilham din?”
“Eh mana, ni babban bakin cikina yadda ta dinga gayamin miyagun maganganu saboda kai, wallahi Jalal ba Dan kanwarka bace senasa ankoyamata iya magana, harni zata cewa mutuniyar banza? Ita ma ai ta banzarce tunda zata iya zuwa dakinka shabiyun…….
” Enough malama, karki kuskura ki zagi kanwata, kuma wallahi duk abunda yasameta a kwanan nan kikuka da kanki, Ilham ba mutuniyar banza bace, ni shedane, ki kiyaye baki isa ki zageta a gabana ba, and then zanje gidan in sameta, zatayi bayani”
Yana zuwa nan ya tashi ya tafi yabar Hannah baki a bude, saboda mamaki se yanzu takuma tabbatarwa kanta tsawon wannan lokacin, har yanzu Jalal be fada tarkon sonta ba kenan tunda har ya fifita Yar uwarsa akanta kenan ya fara son Ilham, amma ko ba komai tasan abunda ta fada din nan ze tunzirashi, gaba dayanku, sena nuna muku ni gogaggiyace a bariki

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button