ABDUL JALAL PART 1 HAUSA NOVEL

“Ke Nana lafiyarki kike gudu haka? sekace wata karamar yarinya mene haka”
Jawwad ne yayi maganar a Dan fusace
“Yaya Jalila CE”
“Me yafaru da ita?”
Yafada hankalinsa a tashe
Nima bansaniba yaya tana gidansu Yaya Jalal yanzu muke tare da ita takoma dakko wayarta yanzu kuma ta suma bata iya numfashi sosai
“Suma kuma”
Ai bejira tagama bayanin ba yayi hanyar waje da sauri
Wani Dan guntun murmushi Jalal yayi sannan yabi bayan Jawwad
Itama Ilham ta karasa cikin Gida dan ta sanar da maama abinda yake faruwa
Suna zuwa suka tarar da Jalila kwance akan cinyar mummy bata numfashi, se kadan²
“Subhanallah Jalal bani key din motarka mu kaita Asibiti” Jawwad yafada da sauri
Key din ya danka masa
memakon ya raka Jawwad sema ta shi da yayi yai ficewarsa
Jawwad beyi wata² ba ya dauki Jalila yayi waje da ita yasaka ta a mota ya tada motar kenan
Nana ta shigo gidan ya tsaya ta Shiga motar
“Yaya maama tace muyi gaba zata taho in Abba ya dawo”
Be amsa mata ba yaja motar
“Ilham ki bisu mana kirakasu ko Asibitinne kinga ni badamar in fita yau babanku ya dawo” maama tayi maganar tana duban Ilham
“Ba inda zani wallahi Allah ya bata lafiya in nabisu ai bani zan bata lafiya ba”
“Haba Ilham amma ai a gidanmu abun yasameta”
“Ni wallahi mummy a gajiye nake ba inda zan iya zuwa yadda nagajin nan hutawa nake sonyi”
Ta wuce daki abunta
“Ohh ni hadiza yaran nan se a hankali kowanne da halinsa
Suna zuwa Asibitin aka karbesu aka shiga da Jalila emergency don ceto rayuwarta
Wajen karfe Tara na dare Maama sukazo asibitin ita da Abba
Wanda yai dai²Da fito da Jalila daga emergency aka basu daki
Alhamdilillah numfashinta ya dawo dai² se dai tanata bacci ga drip da aka saka mata
” Allah sarki diyata Allah yabaki lafiya, Amma nayi mamaki iya sanina bata da wani ciwo makamancin haka”
Abba yafada cike da damuwa yana kallon maama
Dan tabe baki maama tayi
“A’a to ai ba dolene kasaniba watakila tana dashi mune bamu saniba kasan uwatta bakomai zata gaya mana ba tunda….”
“Ya isa haka Zainab..” Abba ya katse maama
“Yanzu lafiyarta muke fata ba wani surutu ba”
Likitan ne ya shigo domin kara dubata
Jawwad ne yayi gyaran murya
“doctor meyake damunta ne?”
“Eh blockage ne akasamu a airways dinta maybe ta kwarene ko kuma ta shide da wani abun,
Zatasamu lafiya insha Allah munyi mata allurai zatayi bacci karku damu Allah yabata lafiya” suka amsa da Ameen
Guraren sha daya na dare
Abba da Jawwad suka tafi Gida akabar Nana da da maama suka kwana a gurin Jalila
Washe gari da sassafe Jawwad ya tashi ya shirya da nufin ya koma Asibiti, dayake motar Jalal a hannunsa ta kwana kafin ya wuce ya maida motar gidansu Jalal,
Jawwad ya tsaya suka gaisa dame Gadi yayai masa yame jiki dayake yasan meyafaru,
ya” amsa da sauki,”
Jawwad ya juya zefita se yadawo da baya ya kalli me gadin
“Jalal yana nan ne”
“Eh yana nan yana bangarensa”
“Nagode”
Jawwad ya juya ya nufi part din Jalal Lamar kullum ya na kwance yayi dai² yana bacci babu alamar yayi salla
Jawwad ya daddaki pillown da Jalal yake kwance
A hankali Jalal ya bude ido
“Tashi kayi sallah Dan nasan bakayi ba”
Seda yadan ja seconds sannan ya tashi zaune yana hamma bece masa komai ba ya mike yaje
Yai alwala yagabatar da sallar asuba karfe 7:30am
“Jalal fushi nake da kai”
Jawwad yafada tare da Dan hade rai
Jalal ya kalleshi
“Why”
“Kanwata ba lafiya rai a hannun Allah amma ko ka tambayeni ya jikinta talk less of kace zaka min kara ka dubota to ni na roki arziki ka rakani Asibiti”
Dabeyi niyyar zuwa ba amma yaga in yai haka be kyautawa amininsa ba wato Jawwad Dan haka yace
“Sorry bross karkayi fushi dani bari in shirya muje”
“Seda na roka?” Jawwad yafada yana Dan hada rai
Murmushi Jalal yayi “to koma mene ai nace zani in kuma bakasone in koma baccina”
“Kai ka isa ni yi Sauri karmu makara ni sonake tana farkawa tafara tozali da fuskata”
Girgiza kai kawai Jalal yai a ransa yace ka dorawa kanka wahala saboda wannan banzar yarinyar Mara kunya
Kafin Jalal yagama shiryawa Jawwad yakira maama
A waya bugu seda ta kusa tsinkewa sannan ta daga
” salami alaikum maama barka da safiya “
“Yawwa barka ya daddynaka”?
“Muna lafiya dama tahowa zanyi nace ko kuna bukatar wani abun?
” a’a bama bukatar komai ka hanzarta dai inaso indawo Gida in huta nibana son zaman Asibiti “
“To maama yanzu zan iso insha Allah, nace ya kuwa Jalilan ta farka ne”
“Ban saniba in kazo kaganewa idonka kaita wani rawar kai akan yarinyar nan ka kiyayeni wallahi”
Ta kashe wayarta
Shidai a iya tunaninsa beyi wani abu dabe daceba amma meyasa maama ta dau zafi haka yayi ta zancen zuci har Jalal yagama shiryawa suka tafi
Sun isa asibitin dukda Jalal ya Dan bata musu lokaci
room din da aka kai Jalila suka nufa
Jawwad ne ya bude kofan tare da sallama
Maama ce ta amsa dayi musu sannu da zuwa,
yawwa tunda kunzo bari mu je Gida dama ruwa zasu karasa mata da allurai kawai su sallameta,
Ninazata tun dazu zakazo Abbanku yazo ya dubata yanzu ya tafi.
shikam gogan kujera ya janyo ya zauna abinsai be kula kowa ba
Alhamdilillah jikin Jalila yayi kyau sun sameta tana rama sallolin dabatayiba
“In ta idar Jawwad ka kira nurse din suzo su karasa mata abinda zasuyi mata seku taho Gida” Maama tafada tana shirin tafiya
Sukagama abinda zasuyi maama da Nana suka tafi Gida.
“Yaya ina kwana”
Jalila ta gaisheshi
“Lafiya qalau ya jikinnaki?”
Jawwad yafada cike da kulawa
da sauki Yaya
“Waime yafaru dakene? Ya akai haka tafaru”?
seda ta kalli inda Jalal yake suka hada ido, tai sauri ta dauke kanta
Ta maida kallonta ga Jawwad
“Kwarewa nayi” tafada a takaice
“Kwarewa kawai numfashi ya dauke ko kinada asthma ne?”
“A’a Yaya banida asthma”
Duk abun nan Jalal danne² wayarsa kawai yake, ba Wanda ya kula a cikinsu
“To tunda kin idar bari inje inkira nurse suzo su miki alluran dafatan kinci abincin?”
“Eh naci abinci, amma ban idar da sallah ba zanyi walhane”
“Kai sisyna bakida lafiya fa ai Allah yaga zuciyarki”
Jawwad ya danyi maganar a shagwabe
Jalal ji yayi kaman ya shake Jawwad yaga yanata wani lallabata hada yiwa mace shagwaba saboda shirme
(Niko nace a ganinka ba)
Itama a shagwaben tafada maganar
“Nifa zan iya Yayana kasan sallah haske ce me girrma kuma tana hana mutum aikata wasu laifukan,
Yayana abune mawuyaci kaga Wanda ya tsaida sallah yana aikata wasu miyagun laifuka da baya kunyar yinsu agaban mutane,
Koda ze aikata yana kunyar mutane suganshi
Kaga inka tsaida salloli biyar seka kara da nafila bakasan abinda Allah ze duba a ayyukanka ba yai maka rahama”
“Nice one sisyna proud of you
Allah yasa iliminki ya amfaneki ya amfani al Umma”
Jawwad tafada yana murmushi
“Proud of u too bros”
Jalal yasan da biyu tayi wannan maganar amma yai kaman besan me sukeba
Seda ta idar da sallah takoma kan gadon sannan
Jawwad ya kalli Jalal
“yace brother zomuje induba nurse din suzo susa mata ayi ai sallamemu”
“Jeka dawo ina nan” abinda Jalal yace kenan
“OK to bari inje”
Gaban Jalila ne yafadi ta kalli Jalal idonsa yana kan wayarsa ba ita yake kallo ba
To in yayi min wani abun fa
Jawwad nafita Jalal ya kalleta
“
Kina tsoron in kumayi miki wani abun ne?”ya mike daga inda yake yadawo kujerar gaban gadonta
“Meyasa baki gaya musu gaskiya cewa taba kika shaba,
rashin sabone kawai, in bahakaba daga shan sigari seki suma kikusa shekawa lahira?”
yafada yana murmushin mugunta
Banza taymasa taki kallon sa
“Yanzu sauranki giya da kwayoyi tunda ina sha kema sekin sha,
Kwanan nan kema zaki fara zuwa mashaya”
Yafada yana hade rai