Uncategorized

ABDUL JALAL PART 1 HAUSA NOVEL

Share please
More comments more typing……………………..

????️????️????️????️????️
????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????

_ABDUL  JALAL_
       (2020)

  _ STORY & WRITTEN BY AISHAHUMAIRA_
(Daddy's girl)

           PAGE- 40

PART 1
Share please

_Bismillahir Rahmanir Rahim, da sunan Allah me Rahma me jin kai, Allah ka yi salati a bisa shugaban mu Annabi Muhammad (salallahu alaihi wassalam)
Bayan haka, ban rubuta wannan littafi domin cin zarafin wani ko wata ba, na yi shine domin nishadantarwa, da kuma wa’azantarwa, ku biyoni domin jin me wannan labarin ya kunsa.
Yanda nafara Allah yabani ikon kammala shi

Ina maraba da shawarwari, sharhi, ko kuma gyara, nagode.

Domin Samun karanta wannan littafin yi magana ta what’s app akan wannan lambar

07063065680
Kokuma addanna wannan link din domin samun novel din

????https://chat.whatsapp.com/EtB4KI52K0v5FQc2ELhidL

Special thanks to my group members ina Alfahari daku comments dinku na bani karfin gwiwa
ABDUL JALAL NOVEL FANS
Love u all guys ❤❤❤❤❤

      -MY FIRST NOVEL-

Suka karasa inda Hanan take waya, tagama wayar ta juyo ta kallesu, sannan tace
“Lafiya naga kunzo kunsani a gaba”?
Yaseera tayi murmushi
” baki gane niba ne”?
“Eh ban ganekiba, yauma nafara ganinki”
Aikuwa Ilham a fusace tace “kingani ko yaseera tsabar
rainin hankali wai bata ganeki ba, nagayamiki muguwar Yar rainin hankalice”
“Haba Ilham meye hakane? Meye Dan bata ganeni ba seta iya yuwa ta manta ne”
“Kizo shekaran jiyan sannan yau tace ta mantaki”
Hanan ta kallesu
“In Baku da abin cewa, ni ina da abunyi”
Yaseera tace “A a Jalila, Yaseera ce fa, da mukazo shekaranjiya”
Hanan ta fuskanci basu San ba Jalila bace, Hanan a ranta tace wannan ce Ilham kenan, hada ita a cikin labarin da Siyama tabata, na Jalal
Ta kallesu tai musu kallon tsaf sannan tace “wannan Hanan ce ba Jalila ba”
“Kamar ya?”
“Kamar yadda nagaya muku mana”
Yaseera tace “Dan Allah Jalila a dena Jokes din nan gurinki mukazo zamuyi magana”
Hanan tace
“Maganar Me?”
“Akan abunda yafaru jiya har Jalal ya huce akan Ilham, abunne yabamu mamaki kwarai”
Hanan a ranta tace lallai wannan basu da hankali su nan gaba daya sun yadda Queen ce,.to ni mema zance musu nida bansan meya faruba,
“Nima abun yabani mamaki kam, amma yanzu ina wani abunne, kubari anjima,.semu hadu”
“To shikenan ina Nana?”
Yaseera ta tambaya
“Nana tayi bakine tana part din Jawwad”
“OK mungode se anjima”
Suka juya suka fita
Ilham ta kalli yaseera “ji wani sabon iyayi, ga yadda ta canza magana, tanawa mutane magana da isa sekace wata basarakiya”
“Nima nagani Ilham ai wannan se munbi a sannu”
Suna fita Hanan ta dinga dariya sannan tace amma gaskiya wannan sakarkarune,
Takoma ta tarar sunata cin abincinsu banda Jalila da take ta tsakura duk a takure take
Hanan ta danyi murmushi sannan tace
“Yaya Jalal kufa ci Abincin nan sosai, inba hakaba Abdallah cinyewa ze ya barku”
Jalal yai murmushi,
“Meyasa kika takurawa yayankin nan haka”?
” Abdallah yace tambayeta dai, ni dai ba kunyarku zanjiba Dan in ban koshiba zan karane”
Hanan tace “Nima ai haka kake min kaita kunyatani a gaban mutane”
Jalila tace
“To suda uwar magana ki zauna kici abinci ni bansan yadda akayi bakinki ya bude hakaba, kika koyi surutu”
“Hh au haba zama dake ne yasa na koya, ni na manta ma kinyi baki fa, yanzun nan”
Jalila tace mata “suwaye”?
” ban sansu ba,.wasu matane su biyu suka ganni a waje sun dauka kece suka faramin surutu, nikuma nace sutafi aiki nake sudawo anjima”
“Dan wulakanci gaskiya baki kyautaba”
Cewar Abdallah, Hanan ta kalleshi ” Abdallah bana son ganin gushewar wannan farincikin da nake gani a fuskokinku, nasan in Jalila ta tashi tsareta zasuyi da surutu, Dan daganinsu ba wani abun kirkinne yakawosuba”
JALILA tace
“Ni mamakima nakeyi suwaye haka?”
Hanan tace “wata fara dai me kwalakwalan idanuwa, se wani kallon banza takemin da wata kuma me surutu, se magana take wai lallai sena ganeta sunzo shekaranjiya ko baseera kowa oho dai”
Jalila ta kalleta “kai Hanan meyasa kikace su tafi”
“To me zasuyi miki, wannan me kwalkwalan idanuwan sewanj kallon banza takemin, shine ya tabbatar min ba abun arziki ya kawosuba”
Nana tai dariya
“Kanwar Yaya Jalal ce fa, Ilham ko?”
Dan zare Ido Hanan tayi,
“Dagaske amma basa kama, wata Mara.. Sekuma tayi shiru
Jawwad yace ” Hanan kanwar Jalalce cousin dinshi ce”
“Sedai cousin din Dan basa kama, gashi se wani..
Bata karasaba Jalila ta janyota
” haba Hanan zubar ya isa kici Abinci mana”
“To nayi shiru”
Suka cigaba da cin Abinci
Jalal a ransa yake jin wani nishadi, Wanda rabon dayaji shi har ya manta, a ransa yake jin inama a ce wadan nan duk yan uwansa ne shima yace yau yanada yan uwa amma shikadaine kamar rai
Suka gama cin Abincin sannan su Hanan suka kwashe kayan suka tafi cikin gida
Suka koma dakin su Nana, Nana ta tafi dakin Maama don basu guri Naja se masifa take wai Nana ta rike bare ta manta da ita
Hanan ta kalli Jalila “Queen do you believe now Jalila, nagaya miki Jalal yana bukatar kulawane kawai, kadaici yana taka rawa a rayuwarsa”
“Hanan gaskiya nayi mamaki, bantaba ganinsa cikin nishadi ba, koyana dariya kullum fuskarsa babu fara a, kinga wadda sukazo nemana din nan farar, cousin dinsa ce a gidansu take itace take sonshi bakiga dukan dayaake mata ba baya shiga harkar mata, Nima fada muke, yabani mamaki danaga ya kulaki”
JALILA ta kwashe labarin Jalal zuwa yadda suke fafatawa dashi, halayensa dayakewa mahaifiyarsa, har zuwa mafarkan da takeyi dashi”
Hanan ta kyalkyale da dariya
“Jalila ta kalleta, meye haka kuma, Maya baki dariya”
Hanan ta sassauta dariyarta
“Ashe bani kadai rashin kunya ba taiwa ranaba, kut naso inga idonki lokacin daya baki sigari, kut gaskiya Jalal Dan duniyane yayi maganinki”
Tafada tana kuma kyakyata dariya
“Mtseeww nifa bana son wulakanci”
“Yi hakuri queen, let’s be serious, Jalila kiyi wani abu, zaki iya temakon rayuwar Jalal”
“Ta yaya zan iya wannan Jarababben Dan taurin kan”
“Bashi da taurin kai Jalila, he is simple, yanzu dai yakamata kisan meyasa bayason mahaifiyarsa, ki gano wayeshi, Jalila ke Alkhairi ce a duk inda kikaje, kiyi wani abu sannan kidingayi masa addu a kidena yi masa rashin kunya naga alamar bayason rainin”
“Hmm mugun Dan rainin hankaline Hanan bazaki ganeba”
“To kicigaba dayimasa rashin kunya randa yabaki giya, kya kirani kibani labari”
“Allah ya kiyaye”
Halima tayi sallama suka amsamata
Ta kallesu sannan tace “wacce ce Jalilan ne tunda tazo na dena ganeki”
JALILA tayi dariya
“Ya akayi leemart”
“Dama Cewa akayi wai kushirya in anyi sallar la asar, Hanan zasu tafi”
“To shikenan”
Sukayi sallar LA asar Hanan tanata Nanatawa Jalila, ta temaki rayuwar Jalal,.sannan duk abunda ake ciki ta kira ta a waya tagaya mata,
Hanan ta fito tayi sallama da Maama, Maama tabata kyautar agogo, sannan Sukafito
A harabar gidan suka tarar dasu Jalal Suma sun fito
Abdallah ya kallesu, yace “Yakamata muyi hotuna fa, domin tarihi”
“Gaskiya kam” cewar Jawwad
“A fara yimana nida JAWWAD”
Inji Hanan
Ta tafi kusada Jawwad akayi tayi musu
Sannan akaimata itada Jalal, da Abdallah dakuma Nana
Takalli Jalila “Queen come forward”
Ta janyo hannun Jalalila zuwa kusada Jalal,
Kallon Jalila yayi, Jalila kuma ta hade rai
Hanan tace “Haba queen meye haka kiyi dariya mana, kin wani hade rai kamar wata boss”
Dariya sukayi, Hanan tai musu photo, a haka aka dinga hotunan nan, Naja ce ta fito harabar gidan tai tozali da Abdallah gaba daya ta rikice tarasa nutsuwarta, kai Allah yayi Halitta a nan, basu kula da itaba sukaji gaba da hotunansu,
Nana ce suka kuma dawowa da Yaseera suka tarar anata budurin hotuna Jalal kamar bashiba, se fara a
Se yanzu suka gane, ashe dazu ba Jalila suka ganiba tsabar kamace kawai dasukeyi, Jalal na ganin Ilham ya hade rai, suka karaso inda su Jalal Suke, Yaseera ta kalli Jalila tace”dazu munzo gurinki Ashe bake bace” Jalila tayi dariya tace “bani bace Hanan ce”
“To shikenan bari muje naga kunada baki,”
“A a bakomai bari inzo”
“A a ki bari zamu dawo”
Jalila tace”to shikenan “
Ilham, Jalal kawai take kallo da mamaki, ya kalleta, maganar Hanan ya tuna wai fara me kwalakwalan idanuwa
Kawai yadanyi murmushi.
Su Hanan sukayi haramar tafiya har bakin mota su Jalila suka rakasu, Hanan ta kallesu
“Kamar kar mu rabu, haduwar nan tayimin dadi, muna fatan kuma wataran zaku kawo mana ziyara”
“Insha Allah, muma zamu kawo muku ziyara”
Ta kalli Nana sannan tace
“Nana zanyi missing din murmushinsa, Dan Allah kibani shi”
Nana tace “wa kenan?”
Ta kalli Jawwad
“Gashi nan”
Gaban Jalila yafadi, shikansa Jawwad sedaya kalli Hanan,
Abdallah yace
“Aliyu kaga ku kyale Hanan, wani lokacin bata da hankali”
Ya bude mata mota “wuce muje”
Ta rike murfin motar sannan ta kalli Jalal
“Yaya Jalal da Nana da Queen bakinsu daya naga kamar bazasu bani ba, Dan Allah kai kabani shi”
Jalal ya kalli JALILA ya kalli Jawwad yaga duk Jikinsu yayi sanyi kaman Wanda akace za a kashe se yayi murmushi
“Yace indai Jawwad ne nabaki shi,”
Abdallah ya kalleshi
“Tab Jawwad kar ka yadda ka auri fitsararriya wannan, kyanta tsayayyen soja Wanda ze zaneta in tayi ba dai² ba”
Dariya sukayi amma banda Jalila
Hanan ta shiga gaban mota ta sauke glass ta kalli Jawwad,
“I will miss you Yaya Jawwad dina, keep me close to your heart”
Juyawa Jalila tayi ta shige cikin Gida, saboda ji tayi wani abu ya tokaremata a kirji, takasa tsayuwa
Hanan ta jingina da Jikin kujera, tayi murmushi tareda lumshe ido a hankali ta furta “am sorry queen”
Abdallah ya kalleta “ya dai uwar magana”
“Ba komai, ina cikin farincikine kawai”

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button