ABDUL JALAL PART 1 HAUSA NOVEL

Gaba daya sukashiga cikin gidan kowa se fara a yakeyi ana mass sannu dazuwa
Daka ganinshi kasan mahaifin Jalal ne saboda tsabar kamar dasukeyi,
kaman yadda yake dabi’ar Jalila, har kasa ta durkusa ta gaisheshi,
Da sakin fuska ya amsa mata tareda cewa
” wannan fa?”
“Ai Yar wajen marigayi ce kanin babansu Jawwad” mummy tabashi amsa
“Allah sarki, Ashe takwarar Jalalce ta girma haka, tubarkallah
gata nutsatsiya
Allah yaraya ma naku gaba daya”
Suka amsa da “Ameen” gaba daya
Banda Jalal dayake ta cin magani a ransa yace “wai wannance nutsatsiya munafuka Mara kunya yarinya”
Watsewa suka farayi a hankali domin Barin daddy ya huta
Ilham ta tafi dakinta tashiga wanka saboda tagaji,
Jawwad yakoma Gida
Shikuma Jalal yatafi part dinsa
Jalila da Nana Suma suka nufi hanyar Gida har sun fito Jalila ta tuna wayarta tana gidansu Jalal inda ta kwaso labulaye daga Shanta
“Au Nana wayata rakani in dakko please”
“Gaskiya nagaji bazan koma b”
“Dan Allah ki rakani, inkuma Jalal yakamani fa?”
“A gabanki fa Yakoma part dinsa baya cikin gidan inajiranki anan jeki dakko”
“To bari inje”
Tashiga ba kowa a palourn Dan haka da sauri tashiga ta dakko wayar,
tana zuwa corridor din daze sadata da waje taganshi a tsaye yabawa inda take baya yana waya na Shiga uku inya kamani na shiga uku, wata dabara ta fado mata
Ta tako da gudu zata wuce tabayansa caraf ya riketa
“Haba karamar Mara kunya kinzaci bansan da shigarki bane yau babu me kwatarki zanga karyar rashin kunya”,
” meye haka dalla malam cikani”
Tafada tana kiciniyar kwace kanta
“Ooh har kin manta da maganar mune
Zan maidake Irina ne kawai in samu abokiyar shaye²”
“Dalla ka cikani ni ba Yar iska bace “
“Nima ba Dan iska bane kawai Mara tarbiyane, kema kuma hka nakeso kizama,
yanzu sigari kawai zaki sha kema kizama salansa kaman ni kullum bakinki cikin hayaki”
Wani mugun kallo tayi masa
“Allah ya kiyaye in zama irinka kai halinka har wani abun sone mara………..
Bata karasaba yasaka sigarinsa a baki ya zuka hayakin a bakinsa
Ya rikota yasa hannunsa daya ya toshe mata hanci, yasa bakinsa a nata ya dure mata hayakin nan tas a bakinta,
aikuwa take numfashinta ya sarke,
Yakuma zuka ya dura mata sau uku
Sannan yasaketa ta zube tana wani irin tari tana Jan numfashi da kyar, idanun ta sukayi jawur, numfashinta yana sama yana kasa kaman me asthma
Share please
More comments more typing…………
????️????️????️????️????️
[8/31, 8:26 AM] Safiyya: ????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????
_ABDUL JALAL_
_WRITTEN BY AISHA HUMAIRA_
(Daddy's girl)
PAGE- 7
PART 1
_Bismillahir Rahmanir Rahim, da sunan Allah me Rahma me jin kai, Allah ka yi salati a bisa shugaban mu Annabi Muhammad (salallahu alaihi wassalam)
Bayan haka, ban rubuta wannan littafi domin cin zarafin wani ko wata ba, na yi shine domin nishadantarwa, da kuma wa’azantarwa, ku biyoni domin jin me wannan labarin ya kunsa.
Yanda nafara Allah yabani ikon kammala shi
Ina maraba da shawarwari, sharhi, ko kuma gyara, nagode.
Domin Samun karanta wannan littafin yi magana ta what’s app akan wannan lambar
07063065680
Is a free book
I want comments not stickers????????????????
Comments dinku shine kwarin gwiwata
_My first novel_
Aimin afuwa
Today’s page isNot Edited
“To wai Yaya mairo me kikeso inyine yaje ya taho da ita yace anan zatayi Hutu to korarta kikeso inyi ko kuma yazanyi
Kinsan halin Abban su Jawwad yanason Dan uwansa akan yarinyar nan beki yamin wulakanci ba”
Maama tayi maganar cike da damuwa
“Seki hade mata fuska yadda nan gaba in ance tazo miki Gida bazata zo ba akan me azo akoyawa yaranki dabi’un arna kinsan ba kunyace dasu ba har kibarta da danki su kwana daki daya da yarinyarki”
Jikin Jalila a sanyaye ta saki handle din kofar ta koma da baya idanunta na zubda hawaye bazata iya cigaba da jin wannan miyagun maganganun da cin fuskar ba
Wai itace dangin arna ababen kyama to shikenan su arna ba mutane bane
Kaman wadda kwai ya fashewa a ciki haka taja kafarta ta nufi dakinsu ta shiga ta tarar Nana da wata budurwa wadda batafi sa’arsu ba (wadda sukazo da yaya mairo)
sallama tayi a hankali
Nana na ganinta ta mike ta rungumeta
“Oyo yo Jalilana sannu ya jikin”
Murmushin dole Jalila tayiwa Nana Wanda iyakarsa bakinta “
da sauki Nana nasaku wahala sannuku Nagode”
” shhhh meye kuma wahala anan bana son irin wannan zancen gaskiya babu haka a tsakaninmu”
“To na dena Ashe bakuwa kikayi”?
” baki ganeta ba Sa’ada cefa Yar gidan Anty mero”
“Eyya banganeta bane sannunki”
Jalila tafada
Sa’ada ta Dan dubeta a yatsine “yawwa sannu”
“Nana bari in Dan watsa ruwa”
“To a fito lafiya kiyi a hankali inda wani abu daba zaki iya ba kimin magana ” Nana tafada cike da kulawa
“Karki damu zan iya komai da kaina”
Towel ta dauka ta shiga toilet dayake toilet din a cikin daki yake
Tana shiga bandakin Sa’ada ta gyara zama cike da gulma
“Ke Nana yanzu Dan Allah wannan danginsu arna ne?kuma kike zaune tare da ita ko kyamarta ba kyayi?”
A fusace Nana ta kalleta
“Mene haka Sa ada ina ruwanki?
Waima tukuna ubanwa yagaya miki haka karki karamin irin wannan maganar bana so” Nana tai maganar a fusace
“Daga fadan gaskiya se ki kama min jaraba, ai dai kinsan mamanmu bazatayi karya ba ke Yar uwata ce bazanso kishiga wani hali ba ni warin arna ma naji tanayi”
“Ke Yar uwata ce Jalila ma Yar uwata ce ta shi kibarmin daki”
Jalila kam taji komai duk zancen da sukayi taji a bayan kofa ta jingina jikinta tana zubar da hawaye me kona zuciya
Jiki a sanyaye tayi wanka tafito wankan dabata da tabbacin tafita
Tana fitowa Nana ta kalli Jalila cike da damuwa zatayi magana saboda tasan taji abinda Sa’ada tafada
Amma Jalila cikin karfin hali da dakewar zuciya tace
“Nanancy yau me za a girkamana ne ne yau?”
“Kinga Jalila Dan Allah………
Jalila katseta tayi ta hanyar cewa
” yau muyi dambu kinsan mutumina ne amma Allah yasa kin iya Dan kinsan nafiki iya girki”
Duk yadda Nana taso suyi zancen maganganun da Sa’ada tayi domin tabata hakuri Jalila taki se ta basar da zancen
Jawwad kam yakada ya raya Jalal ya bishi suje masallaci yaki yace shi inyaje Gida yayi sallarsa
Haka Jawwad ya tafi massalaccin shikadai
Bayan yadawone yace bari yaje cikin gida yakuma duba Jalila Dan haka ya nufo cikin gidan
Nana ta kalli Jalila tace
“Maama kuwa tasan kindawo”?
“A’a naga tayi bakuwa shiyasa banjeba kar in takuramata” Jalila tabata amsa
” bafa wata bakuwa bace Yaya mairo ce yakamata tasan kin dawo ai “
“Hakane bari inje”
Yana shigowa palourn ya ga Yaya mairo da Sa’ada gefe ga Maama a zaune
“Yau manyan baki mukai kenan Anty mairo ina wuni”
“Eh kace haka mana yausha rabonka da gidana baka da zumunci Jawwad Sam wannan halin naka a dangin ubanka ka samo shi Dan mu bahaka muke ba”
Tafada cike da isa
Shikam har ga Allah Jawwad baya zuwa gidan yaya mairo dukda kasancewarta yayar mahaifiyarsa irin matan nanne masifaffu Wanda basa raina abin magana ga ta da mugun Sa ido kuma intana guri kawai so take abinda ta yanke shiza a yi ga shiga abinda ba ruwanta
Shiyasa Jawwad baya kaunar zuwa inda take yanzuma komeye na sako dangin babansa oho?
“To yanzu Dai Allah yabaki hakuri insha Allah hakan bazata sake faruwa ba insha Allah zaki dinga ganina har kigaji da zuwana”
“Kaji dashi dai”
“Maama ya jikin Jalilan kuwa?”