ABDUL JALAL PART 2

ABDUL JALAL PART 2

Comments nakeso ba sticker ba, kokuma just thanks,
A kullum ina alfahari daku masoya wannan novel
Daga alkalamin Aysher cool
????️????️????️????️????️????️????️????️????️????️
07063065680

????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????

          _ABDUL JALAL (2020)_

   _Story and written by_
  AISHA HUMAIRA (daddy's girl) 

PART 2
PAGE 9️⃣/62

Bismillahirrahmanirrahim, da sunan Allah me rahama me jinkai, Allah yakara tsira da aminci ga shugabanmu Annabi muhammadu salallahu alaihi wassalam.
Bayan haka bazan gajiba da mika gaisuwata da godiya ga yan uwa da abokan arziki ba, bayan haka
Banyarda a juyamin littafi ba ko amfani da wani bangare ba tareda izinina ba.
Domin gyara, shawara ko sharhi, za a iya tuntubata akan what’s app number dina
07063065680
Or email address @ www.humaira17@gmail.com

          _MY FIRST NOVEL _

Seda gaban Jalila ya fadi, kirjinta ya buga da karfi, amma ta dake ta maze, ta lallaba Nana suka kwanta, amma bacci ya gagari Jalila, gaba daya abubuwa sun cunkushe mata ta rasa menene mafita, dan haka ta tashi taje tayo alwala ta tada salla.
Washegari da safe seda Jalila takusa sasu su makara sannan suka tafi makaranta, yauma sir hafiz yashiga ajinsu Jalila, har yayi lectures yagama hankalinsa yana kanta, ita kam ko a jikinta, abubuwan dasuka dameta kawai take lissafawa, na farko damuwar Jalal, ga abunda Hanna tace, Hanan ma ta dage akan son datakewa Jawwad tana lika mata Jalal, ga abunda Nana tagaya mata jiya da daddare, gaba daya zuciyarta a cunkushe take tanason sanin waye Alhaji Kabiru ta hanyar yarsa dake ajinsu wato saleema, kallo daya zakayi mata kasan tana cikin damuwa, sir hafiz yana monitoring din duk moves dinta sam attention dinta baya kansa, dan haka yace ta tashi tsaye, ba musu ta mike, ya dinga yimata tambayoyi amma taki kulashi tayi masa shiru, lamarin yarinyar nan ba karamin daure masa kai yake ba, daya dameta ma kawai seyaga idonta ya cika da kwalla, tana nema tafara kuka. Dan haka ya kyaleta yacigaba da lectures dinsa ba tareda yace ta zauna ba, yagama tsaf sannan yace ta biyoshi office, banza tayi masa, tanemi guri tai zamanta ta kifa kai, tarasa meyake mata dadi, hawaye tafarayi tanayi tana gogewa, zahra ta dafata tace “Kiyi hakuri kidena kuka, nikaina banajin dadin abunda lecturer din nan yake miki, nasan ba dadi amma dan Allah kidena kuka kinji” sam zahra batasan meye damuwar Jalila ba dan haka tabita a haka, zahra tace “bari inje in siyo miki ruwa kisha ki wanke fusakarki” Jalila ba tace komai ba, zahra tafita taje siyo ruwa, a hanyarta ta dawowa, Su Samira suka datseta, suka sha gabanta, samira ta kalleta sama da kasa sannan tace “A tunaninki tarayyarki da wannan dakikiyar yarinyar zesa in fasa bibiyarki ne, wallahi yazama dole ki amince da bukatata, komai kike bukata na more rayuwa zanbaki shi, amma muddin kika cigaba dabin yarinyar nan, ina tausaya miki abunda ze biyo baya, saboda rayuwar taki dakike takama da ita, ita zansa a tarwatsa yadda sekin wulakanta a idon duniya ” a firgice Zahra ta kallesu, Saleema tace “Zahra dama ce a gareki kina ganin su zee da salma duk asirinsu a rufe sunata hutawa, keme yasa bazaki yadda ba, waike ta Allah ko, wallahi duk matakin data dauka akanki kekika jawa kanki, sannan yazama dole kiyi gaggawar rabuwa da wannaan dakikiyar yarinyar. Daga nan suka wuce suka batta a gurin, a hankali ta furta” Nashiga uku, Allah ka tsareni daga sharrin wadannan mugayen” jiki a sanyaye tafara motsa kafarta
“Ke! Ke!!” taji ana mata magana a baya, tsayawa tayi ta waigo, setaga sir Hafiz, “kigayawa kawarki kice mata bataji kiran danayi nata bane” jinjina kai kawai tayi, ta tafi aji ta kaiwa Jalila ruwa ta sha ta wanke, fuskarta Jalila ta kalleta, a sanyaye zahra tace “sir hafiz yace meyasa bakije kiran da yayi miki ba” jin maganar zahra a sanyaye yasa tace “lafiya naganki wani iri, me yafaru” zahra bata boye mata komai ba tagaya mata, “Jalila inaga dole mudena hulda tunda suka sakoni gaba, inacikin tashin hankali” ran Jalila ba karamin baci yayi, ta kalli zahra “har yanzu babu uwar datayi nakuda ta durkusa ta haifi wata shegiya dazata sa inyi wani abu ku indena wani abu dan ina tsoronta, dan haka nasiyi wannan rigimar koni kosu, musamman Saleema, bada ita zanyiba sa makyankyashinta zanyi” mamakine yacika zahra kaman ba Jalilan da take kuka ba yanzu abun tausayi amma yanzu itake masifa haka “Jalila meye kuma makyankyashi?” “ba ruwanki, kuma bazan dena hulda dakeba sedai kibar department din nan, in yaso ba tarwatsawa ba in sunga dama susakawa rayuwartaki bom, ba abunda ya shafeni bane tunda kedai bakida wayo bakusan yancinkiba, seki zauna wasu yan kwaya suna raina miki hankali saboda bukatarsu” tanagama fadin haka tatashi ta dau Jakarta tabar ajin, tabar zahra baki bude.
Office din sir hafiz ta tafi, tana zuwa su samira na fitowa, kallon Samira tayi ido cikin ido tace mata “Kiki yayi shiga hurumina, karki yadda kisanni a ainihin kalata” ta juya ta nufi office din, tayi knocking yace ta shiga, yana zaune yana breakfast yana shan tea, dan kuramata ido yayi ya dauke kai yacigaba da abunda yake, har kasa ta durkusa ta gaisheshi dan dagowa yayi ya amsa mata, bata jira izininsa ba ta haye kujerar dake fuskantarsa ta maze hada jujjuyawa, aransa yace “Ikon Allah wanna yarinyar ba dai mulkiba” seda yagama abunda yake yayinda still yanzuma tunani take tanayi tana kokarin maida kwallar data taru a idonta, ya dan dubeta yai nazarinta nawasu seconds sannaan yace “Wayabaki damar ki zauna?” bata kalleshiba tace “bana son tsaiwa dazu ma daka tsayar dani a aji kafata ciwo take” “Kodayake bakiyi kakar wahala ba, amma Meyasa kike kokarin boye baiwar da Allah yayi miki, meyasa kika zabi kidinga dizga kanki agaban yan ajinku? Kika fi maida kai akan tunani kullum?” shiru ta danyi idonta taf hawaye tace “ai kai ka janyomin, nagaya maka kadena tambayata agaban yan aji amma kullum seka tambayeni danka wulakantani, ni bazan bada amsa agaban yan ajiba, bana son sa ido”
“Wayece miki dan in wulakantaki nake tambayarki?” “Zuciyatace tagayamin” murmushi yayi “tagayamiki ba dai dai ba, amma meyasa kike boye baiwar da Allah yayi miki, ga yawan tunani a class, you are too young ace kina tunani dayawa?”
“Akan me zan nuna ni watace? A hakanma wasu sun tsaneni a ajinmu nibansan menayi musu ba,”
“Suwaye suka tsaneki?”
“Samira da gangs dinta mana, kuma wallahi in basu fita sabgata ba senayu maganin yarinya “
Kallonta yayi “I like your confidence, amma kidena wannaan maganar, yarinyar nan tanada manya karki sa kanki a matsala kinada kwakwalwa me ban mamaki, ba ruwanki dasu kiyi karatunki kawai” Jalila a zuciyarta tai murmushi “tab aikuwa bazan bar gurin nan ba senaji Labari sosai akansu, bari inbi da mutumin nan a sannu”
Dan zumbura baki tayi “ni ina ruwana da wasu manyanta akan me zata takuramin, nima inada Allah kuma babana yana sona dan haka ba wanda zemin komai”
“No bahaka bane, yarinyar tasan manyan yan siyasa, gata fitinaniya har yan daba ne da ita karkije tasa a miki Illa” Zare ido Jalila tayi ta lura yanajin dadin hirar dasuke dan haka tace “to sir amma aka kyaleta a cikin school din nan haka kawar nan tata tafi tsanata taana cemin dakikiya fa,
They are terrorist in har mace za’ace tanada yan daba tazama hatsari a society” “Hakane amma ya zamuyi, hukumar makaranta bata dau mataki ba ance babu kwakwkwarar hujjar data tabattar dahakan kinga se hakuri, dan haka ba ruwanki dasu kiyi karatunki kawai kidena wannan tunanin”
“To nagode sosai Insha Allah zan kiyaye, amma tunani yazamemin dole, anyway am very grateful with your advice nagode, Allah ya jikan mahaifa” murmushi yayi yace “Nima nagode Allah ya wuce mana gaba” ta dakko Jakarta ta fito.
Jalal jiyake kaman inyayi kykyawan yunkuri zuciyarsa zata fasa kirjinsa dan bakinciki da bacin rai, daren ranar kasa bacci yayi, yasha giyar amma batayi masa komai ba, haka Jawwad yazo yasameshi da safe, juyin duniya yaki kula Jawwad balle yagaya masa meyake damunsa, haka Jawwad ya hakura ya kyaleshi ya tafi makaranta, yana nan zaune a palour yaji bacci ya sace shi, kira’ar Karatun Jalila ya dingaji a mafarki, wadda yagani a gidan telabijin shekarun baya koda ya farka daga baccin se yaji babu damuwar a taredashi, yai ajiyar zuciya yai shiru yana tunani wayarsa ce take ringing, kallon wayar yayi, sunan Hannah yagani, tsaki yayi yaki daukar wayar.
Ilham hankalinta yagama tashi jin abunda Jalal yace jiya, kwana tayi batayi bacci ba, aiko sama da kasa zata hade bazata bar gidan nanba ba tareda ta samu abunda take soba, dan haka da sassafe ta tafi dakin Mummy,
Kuka sosai tasakawa Mummy, “Mummy kingani ko, baya sona kinga wulakancin dayayumin, betabamin goriba se jiya dan kawai ance asa ranar aurenmu nikam nashiga uku Mummy, wallahi inban aureshi ba mutuwa zanyi”
“Ilham meye hakane, kibi komai a sannu mana, kiyi hakuri bazaki bar gidan nan ba shima bacin raine yasashi fadin abunda yafada amma kiyi hakuri zan shawo kan matsalar”
“Mummy nan da yaushe to? Nifa gaskiya na damu, bantaba tunanin Yaya Jalal zemin haka ba, anya kuwa ze yadda da aurena”?
“Nace kiyi hakuri nasan abunda zanyi, aure keda Jalal ba fashi, kigoge hawayenki kidena kukan haka ya isa, tashi muje palour”
Ilham ta goge hawayenta suka fito itada Mummy.
Hannah tarasa meyakemata dadi, dagaske Jalal za’asamasa ranar aure da Ilham, aikuwa da Ilham ta tafka mafi girman kuskure a ratuwarta, to amma Jalila fa meye nata manufar, amma yakamata in gayawa Jeje wadda ta rusa masa shiri, amma yakamata inyi magana da Wannan yarinyar yana da kyau insan meye manufarta, wayarta ta dauka tayiwa Jalal message
Jalal ya shiga yai wanka, message ne ya shigo wayarsa, ya dauka ya duba
“Wallahi Jalal inbaka amince da aurena ba, narantse maka sena nuna maka ni cikakkiyar yar bariki ce, wallahi sena maka sharrin da harka mutu ba wanda ze yadda bakai kayi ba, ka rubuta ka ajiye gara tun wuri kanemamana mafita karka kuskura kayi ganganci auren wata, dan wallahi bakai ba kwanciyar hankali
“Hmm bakida hankali” Jalal ya furta a hankali, yafito ya tafi cikin gida dan yunwa yakeji, a palour yaga Mummy da Ilham, be kulasu ba yaje ya dakko abunda ze dakko ya nufi part din daddy, Ilham ta zata yanzuma zemata masifar yace tabar gidan amma taga be kulata ba, yaje part din daddy ya zauna yaci Abincinsa suka sha hira, a haka daddy yaita masa nasiha akan hakuri dakuma yadena kyamar Ilham, se Jalal yaji kaman yai masifa danshi baya son adinga dangantashi da Ilham wai ya aureta, se ya tuno abunda Jalila tagaya masa akan baya yiwa mahaifinsa biyayya, haka yayi shiru daddy yaitai masa nasiha, Jalal yana gama cin Abincin sa ya kalli daddy “daddy kaga naji nadena, yanzu inason in dan fita ne”
Daddy yace “ba dai kasaon fadan danake maka Seka dawo Allah ya kiyaye” “Ameen” ya tashi yabarwa daddy kwanukan Abincin a palour, Ilham tanata fargaba da Jalal yafito amma taga still be kulata ba ya fice daga palour, dakinta ta koma ta dauki wayarta takira yaseera, bugu biyu ta dauka
“Hello yaseera kinajina?”
“ina jinki Ilham lafiya naji muryarki a haka”
“Yaseera ina cikin matsala” “matsalar me kuma?”
Nana Ilham ta gayamata dukkan abunda yafaru jiya akan ance za’ayi maganr aurensu da Jalal.
“tabdijan lallai Ilham akwai katuwar matsala, gaskiya yayan nannaki akwai taurin kai, dole musake shiri amma kunyi waya da ummane?”
“A’a yaseera amma zanje anjima, wallahi banaso ingaya mata ne hankalinta ya tashi banaso ta karaya akan bazan iya cika mata burinta ba, gani nake bazam gayamata ba, gara mubari ranar Sunday muje gurin malam”
“to shikenan yadda kika gani, amma abun da damuwa wallahi, ace duk wani kissa taki tasiri akansa sekace ba namiji ba, anya ba mata maza bane ba
Ace mutum zuciya kaman karfe”
“Hmm kema dai kyafada yaseera, bari ranar ki shirya da wuri muje”
“to shikenan Allah ya kaimu” “Ameen yaseera nagode sosai”.
Y’an kwanakin nan, Jalila ta dan sakewa Sulaiman suna gaisawa saboda tasamu damar daze temakamata, amma sam taki yadda yazo gidansu ko susake haduwa, dama ba koyaushe yake zama a kano ba se lokaci2 yake zuwa, aikinsa yafi a Lagos, anan yake gayamata shi kakakin rundanar yansanda ne na jihar Lagos, amma iyalalinsa suna kano, suna hira sosai da Jalila yana bata labarin nasarori da hatsarin ayyukansu, amma daya dakko batun daya shafi soyayya seta kashe wayarta, hakama Alhaji Kabiru Jalila ta sakar masa sosai gani yake kaman sonshi takeyi, a nan takara tabattar da Saleema yarsace ta cikinsa itada faruk.
Yanzuma waya suke da Alhaji Kabiru
“sweet heart wai yaushe zaki farantawa masoyin kine, kinki yadda mu hadu”
“tab waikai bakajin kunyane yarka fa daka nunamin hotonta zata girmeni kawai sesuga ka auri yar yarinya?”
“to meye a ciki gidanki daban zan ware miki, ita Saleema tanacan karatunta tanagama karatu zan aurar da ita, Faruk yana ABU, sukenan yarannawa fa, kuma basuda damuwa da aurena, please my sweet kibari mu hadu mana, yakamata kinunamin soyayya ina Sonki fa” shi sam besan Jalila tasan Saleema department dinsu dayaba, Jalila aranta tace me mutumin nan yake nufine? Amma ta maze tace
“yaushe zakazo ku gaisa da Abba na?”
“Ai wannan ba wani abun damuwa bane, kibari mugama fahimtar juna mana kinki bari inzo gidanku balle mudan dinga fita chilling din nan, bakya wani nunamin soyayya”
“Banda wannan danake maka wacce kakeso kuma?”
“yakamata ace kinkawomin ziyara gidana mu gaisa mana” “haka kurum matarka ta zaneni” “wayace miki nan zakije, gidana danake ganin special guest dina zakizo” murmushi Jalila tayi “hmmm special guest, ashe nima special ce” “sosai makuwa please my sweet yaushe zakizo?”
“karka damu kabari in mungama exams zanzo, ba dai zuwa kawai zanyi shize tabattar maka da inasonkaba karka damu”
“Kai amma naji dadi sweet, Allah ya kaimu kugama”
“Ameen se anjima” koda sukayi sallama Jalila ta kalli wayar ta takunna recording gaba daya wayar datakeyi tana recording dinta, tana saving a Gmail dinta “Azzalumi kawai, shiyasa abunda kakeyine yasa yarka take can take watsewa a makaranta bakasaniba Jaki kawai, zakuga abunda zan muku kaida yartaka sena kunyataka agabanta in nuna mata nafita iya rashin mutunci”.
Sosai Zahra ke gudun cigaba da mu’amala da Jalila sedai ta waya saboda kashedin dasu sameera sukayimata, gashi suncigaba da uzzuramata akan lallai ta amince da bukatar sameera, tarasa inda zatasa kanta abun ya isheta, dan haka ta samu Jalila tagayamata halin da take ciki, “Zahra yazama dole ki amince da batun su Sameera”
“haba Jalila so kike rayuwata ta tarwatse ne yazakice haka?”
“basonake rayuwarki ta tarwatse bane, taimakonki zanyi”
“to tayaya Jalila, kinsani nasani dukkansu ba mutanen arziki bane da sharri suke nufina”
“Nasani ai tarko zamuyi musu nasan yadda zanyi dasu” Saleema ce tazo har inda su Jalila ke zaune ta kalli zahra “wato zahra bakiji kashedin da Sameera ta miki bako? Har yanzu kina biyewa wannan yarinyar ko”
“Ke wai dakata, suwaye dinta ku, ana dolene ko angaya muku kowa sakaraine dabba irinku” “Ke shiga hankalinki, bana son shishshigi muna daf dasawa amana maganinki yadda ko hanya muka hada sekin kauce”
“Allah ko? Dama waze hada hanya da kazamai jakuna marasa tsoron Allah, aini base kunsa anyi maganina ba, nizanyi maganinku daga ke har kawartaki ba sameera ba ko langa ce kukiyayeni musamman ke” ta nuna Saleema,
“Asararu ko kunya bakwaji kaf school din nan kowa yasan mekukeyi” kafin Saleema tayi magana Jalila ta dau jakarta tayi gaba tabarsu Zahra a gurin.
Kwanci tashi ba wuya a gurin Allah su Jalila suka fara exams din first semester, kowa yana abunda yaga ze fisheshi, wasu sun dukufa karatu, wasu ko sharholiyarsu kawai sukeyi, itakam Jalila ta maida kaine akan lissafin yadda zata bullowa al’amuran ta dasuka dameta,
Yau karfe tara zasu shiga exams, ita Nana sun gama tasu Jarrabawar dan hutu ma sukeyi, gashi Manu direba baya nan Maama ta aikeshi, da karambani Jalila tasaka Manu yakoya mata mota, da mukulli na nan da dakanta zata tafi yau, dan haka ta yanke shawarar tafiya ta hau napep,
Tana fitowa daga gidataga Daddy da dansa Jalal a jikin motar Jalal, durkusawa Jalila tayi “daddy ina kwana?” “Lafiya kalau Jalila makaranta za’atafi ina direban naku?”
“daddy baya nan, napep zanje in hau karfe tara zamu shiga exams”
“kai Masha Allah, Allah yabada sa’a, takwarar Jalal, Allah ya temaka” Jalal ya tsani yaji ance takwarar nan tasa, yawani hade rai, “Ameen daddy nagode sosai Allah yasaka da alkhairi bari in tafi kar in makara” “A’a tsaya, dama Jalal fita zeyi, Jalal kuje seka ajiyeta a makarantar tunda duk hanyace” kallon daddy yayi, ya kalli Jalila ya dauke kansa

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122 123 124 125 126 127 128 129Next page

Leave a Reply

Back to top button