ABDUL JALAL PART 2

ABDUL JALAL PART 2

“Hayateee ashe zakabar kasarnan ba labari, masoyi masoyine ai at least yakamata in sani ai, Allah yakaika lafiya, yatsaremin kai yakareka ya kare dukiyarka, Allah ya albarkaci neman ka, ya doraka akan makiyanka, dukda ni baka damu daniba amma ni kullum soyayyarka ninkuwa take a zuciyata, gangar jikina tana Nigeria, zaka tafi da rayuwata Dubai, kaine rayuwata habib ka kulamin da rayuwata, zanyi kewarka rayuwata, Ina sonka Hayateee” Habib yana harabar hotel din dasuka sauka yaji message din yashigo koba a gayamasa ba yasan na wannan mayyar ne, yana budewa yakaranta sakon yana kuma karantawa, to ya akayi tasan zebar kasar, kiranta yayi seda taja aji sannan ta dauka
“barka da wannan lokaci Rayuwata”
“ke wai aina kika samu lambata kike takuramin haka, sannan wayagaya miki zan bar garine yau”
“haba hayatee, kaifa rayuwata ne, yaya za’ayi inkasa sani, dukda nibani da mahimmanci a gurinka, kai kanada mahimmanci a gurina, Habib yakamata ka girmama kalmar so” tayi ajiyar zuciya, cikin kissa kaman zatayi kuka tacigaba da cewa “Habib bansan da wani kalman za gwada maka yadda nakeji a zuciyata ba”
“kinga dakata, wai bakisan inada aure ba kwata 2 wata biyu kenan da yin aurena, yazaki dinga turomin messages na soyayya in matata tagani fa?” “shiyasa bana kiranka nakemaka message, kuma mata hudu Allah ya halatta maka, karkayi garkuwa da aurenka ka wulakanta bukatata”
“Ke inkece a matsayin matata yazakiji idan akayi miki haka, inason matata kuma ni bazan kara aure ba mace daya Salmana ta isheni”
“Habib da kaine a halin danakeciki nake maka abunda kakemin yazakaji, nafara sonka tun kafin infara ganinka” tayi ajiyar zuciya sannan tace, “shikenan Habib ka dawo lafiya Allah ya dawwamar da farinciki a rayuwar aurenka, nikuma zan dawwama cikin bakinciki har karshen rayuwa ta, zancigaba da rayuwa da soyayyar ka” takarasa maganar tana hawaye “kakula da kanka rayuwata ina sonka rayuwata Habib, i will miss you, zanshiga yanayi mara dadi habibina” kafin yayi magana ta kashe wayarta, habib yacigaba da jujjuya kalaman yarinyar, dan tabe baki yayi yakoma masaukinsu.
Seda habib ya shafe wata shida bezo Nigeria ba shida Salma, suna dubai yana business dinsa suna cin aamarcinsu, sam khadija bata samun habib a waya saboda bata da lambarsa ta Nigeria, ta turamasa message harta gaji, ta bibiyi har gidansa taje tabawa megadinsa makudan kudi da zimmar duk randa habib ya dawo zekirata a waya ya sanar da ita, sannan tace masa idan har Saudat takuma zuwa gidan ya hadata da ‘yan sanda, yace musu su tuhimeta, sannan ayi mata iyaka da zuwa gidan habib, ganin kudi yasashi amsawa yace yadda takeso haka za’ ayi. Wannan kudin databawa megadin gidan Habib Adashin da kabir yayi ne a gurin aiki yakawo mata fiye da rabin kudin yace ta sai kayan kwalliya, shine ta dauki kusan dubu tamanin tabawa megadi dan yayi mata aiki.
tsawon watanni shidan nan haka tayisu kaman mara lafiya, zazzafar soyayya da takewa habib ta wuce misali, har rashin lafiya tayi, gaba daya yan gidansu sun kasa gane kanta, juyin duniya taki gayawa kowa abunda yake damunta, ta rame sosai. Haka bangaren Saudat tayi zarya gidan habib harta gaji, kamar yadda khadija tagayawa megadi haka ya hada Saudat da yansanda, yace musu be yadda da itaba da alama, irinsune wanda yanfashi ke hada kai dasu, haka yan sanda suka kama Saudat, ranar wuni tayi a cell, yayyensu maza sukace ba ruwansu bazasu belinta ba, dama bata da kunya gara a koyamata hankali. Maman Saudat ta dinga hadasu da Allah suje sufito da Saudat sukaki, sukace “aibasu suka aiketa yawon gidan masu kudiba” Khadija da kanta takira kabir a waya tace yazo yanata rakiya, tasa Kabir agaba sukaje police station sukayi belin Saudat, yadda khadija tasaki jiki da yansanda suka dinga hira hada exchange na number ba karamin batawa Kabir rai yayi ba, tunda suka fito yake mita “haba khadija kinsan bana sonki da irin wanan abun, danmene zaki saki jiki da wasu mazan a gabana hada basu lambar wayarki”
“kai dakata malam, aurena kake dazaka dinga takuramin, inbahaka nayiba kana ganin zasu sakarmin kanwata ne? Nifa banason wanan shirmen naka wallahi, inka gama mitar ka iya tafiya” tai shigewarta gida tabarshi a nan a tsaye. Tunda suka koma gida Saudat tayi wanka takasa ko cin Abinci, khadija taje kusada ita ta zauna “Saudat wai meye na damun kanki, bagashi naje nafito dake ba?”
“mtsee khadija ba wanan ya dameniba, ni yanzu tashin hankali na rasa habib, wallahi khadija inason habib, zanyi duk meyuwuwa nima inshiga wannan daular in dama, kome zafaru dani a gaba sedai ya faru amma sena auri habib”
“Saudat kibi komai a sannu, karkiyi gaggawa, se komai yazo miki da sauki, inkikace zakiyi garaje to zaki lalata komai ne”
“hakane amma ni yazanyi zuciyata kaman ta fashene khadija, ni kawai burina inganni a wannan daular” khadija aranta tace “yarinya man kaza, niba dukiyarsa kawai nakeso ba, har shi kanshi habib din nakeso, dan haka zan cigaba da wasa da hankalinki yarinya” ta riko hannun Saudat
“yar uwa, duk macen dataga habib taga dukiyar daya tara dole tasoshi amma kibi komai a sannu, in baki iya takunki ba garin wannan rawar jikin naki wataran prison za’a kaiki, yanzu abunda ze faru kidanyi hakuri kibari su dawo kasar nan semuga ya zamuyi tunda ba abunda zamu iya a yanzu tunda baya kasa”
“shiyasa nake sonki khadija, kin damu da damuwata, zan bari se ya dawo kasar nan”
“idan ya dawo dinma karki sake kikuma zuwa layin gidansu, kibari zansa aje a dan dinga survey din anguwar tasu da anga ya dawo za’asanar damu, Nikaina zanyi alfahari inganki a cikin wannan daular, inkika samu aina samu” rungume khadija tayi da sauri “nagode sosai, inaji dake yar uwa”

“zakigane baki da wayo, bazan taba bari kikuma rabar inda habib yakeba”

Share please
I want comments not stickers or just thanks
Daga alkalamin Aysher cool
????️????️????️????️????️????️????️????️????️????️
What’s app only 07063065680

????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????

          _ABDUL JALAL (2020)_

   _Story and written by_
  AISHA HUMAIRA (daddy's girl) 

PART 2
_PAGE 1️⃣8️⃣71

Bismillahirrahmanirrahim, da sunan Allah me rahama me jinkai, Allah yakara tsira da aminci ga shugabanmu Annabi muhammadu salallahu alaihi wassalam.
Bayan haka bazan gajiba da mika gaisuwata da godiya ga yan uwa da abokan arziki ba, bayan haka
Banyarda a juyamin littafi ba ko amfani da wani bangare ba tareda izinina ba.
Domin gyara, shawara ko sharhi, za a iya tuntubata akan what’s app number dina
07063065680
Or email address @ www.humaira17@gmail.com

    _MY FIRST NOVEL_

Haka khadija tacigaba da wasa da hankalin Saudat ba tareda ita Saudat din tasan me khadija take shiryawa ba.
Khadija ta karbi kudade dayawa agurin Kabir da sauran kudaden data damfara a gurin samarinta tafara business na atamfofi da kayan sawa, gurin manyan masu kudi, saboda tace in Allah yasa lokacin bikinta kece raini zatayi bazata barima azo ayi wani abu a wannan gidan nasuba, biki za’ayi kaman na diyar sarakuna, dan jikinta yana bata zatayi galaba akan Habib saboda alamun sun nuna yanada saukin kai da tausayi.

Ranar da habib yadawo Nigeria me gadinsa yakira khadija a waya yasanar mata, taimasa godiya take ta turamasa katin 5k saboda albishir din dayayi mata, shi habib har yamanta da batun me turomasa messages, se bayan kwana biyu yamaida layinsa na Nigeria messages din khadija yafara cin karodasu ba adadi, tsaki yayi ya aje wayar yashiga sabgoginsa, kwanan sa uku da dawowa yakoma gurin aikinsa, yana zaune a office aka kirashi a waya, bakuwar lamba ne dan haka beyi tunanin komai ba ya daga wayar, tana sallama ya gane wacece, amma yarasa meyasa duk lokacin dazata kirashi baya iyayimata rashin mutunci. Yana cikin wannan tunanin yaji muryarta tana cewa “Rayuwata, barka da dawowa kasa Nigeria, ina maka barka da zuwa nayi kewarka matuka, nayi rashin lafiya sosai bayan tafiyarka, ina fatan kundawo lafiya” Abun mamaki taji yace “ya jikin naki?” seda tayi murmushi ta wani lumshe ido “Jiki ina samun sauki Alhamdilillah”
“me yake damunki?” takuma kashe murya “hayatee komaima yana damuna, nikaina narasa meke damuna, amma jigon rashin lafiyata soyayya ce, at least zansamu relief tunda ka dawo, bari in barka ka huta, I love you hayatee” ta kashe wayarta, tunda habib ya dawo Nigeria tafara shawo kansa saboda koyace katta kara kiransa bata fushi, kullum cikin nuna masa soyayya take, ta lura ya dan damu akan maganar rashin lafiyarta, hakan yasa tafara ji ajikinta burinta yana daf da cika. Tacigaba da kokari tana dauke hankalin Saudat daga kokarin zuwa gidan habib.
Seda khadija ta lura habib yafara bata kulawa, seta dena tura masa message ta kashe wayar da take kiransa da ita domin ta tabattar da ko yafara sonta, haka ta danne zuciyarta tsawon sati biyu bata kirashi ba kuma bata turamasa message ba.
Ranar da sati biyu ta cika khadija ta kunna wayarta, messages ne suka shigo wayarta, data bude duk na habib ne sekuma kamfanin layi, dayake shikadai take kira da layin, duk messages din yana tambayarta ina tashigane layinta baya shiga Allah yasa lafiya, bata san lokacin datayi wani tsalle ba tayi ihu a daki, mamanta ta shigo dakin da sauri “ke lafiya meyasameki?”
“bakomai mama bansan nayibane”
“to Allah ya shiryeki auta” mama ta fice khadija ta mike tsaye hada rawa a cikin daki. Bayan sallar magariba kabir ya tura yaro yace yayi masa sallama da khadija, tace yaron yace tana zuwa, ta shirya zata fita gurin kabir sega kiran Habib. Nan da nan ta tashi ta kulle kofa tazo tanemi guri ta zauna akan gado ta daga wayar cikin sanyin murya tai masa sallama, kafin ya amsa sallamar yace “ina kikashiga haka tsayin wannan lokacin?”
“hayatee bani da lafiya ne fa”
Cikin sauri yace “subhanallah jikinne har yanzu? Yanzu kina inane?”
“ina gida naji sauki”
“dagaske kinji sauki kokuma wasa kike?”
“Am serious, yau naci Abinci sosai nayi wanka nayi kwalliya, i wish kaga kwalliya nan hayatee” murmushi yayi yace “dagaske?” “Eh mana nayi kyau sosai, sedai ciwon so duk ya ramar dani”
“yaushe zan ganki?”
“Duk sanda kakeso, a shiryenake”
“kiyi fixing time, seki gayamin zanzo mugaisa”
“masha Allah, hayateee harnaji na warke gaba daya”
“to Allah yakara afuwa, bari zan shiga gida” cikin sauri cikin shagwaba khadija tace “haba hayatee ni wallahi bangaji dajin muryarka ba, kalli tsayin lokacin daka dauka bana jin muryarka fa” haka khadija ta dinga hilartasa suka shantake suna waya, tana masa hira me dadi har gurin goma da rabi na dare sannan sukayi sallama, Kabir yagaji da jira gashi lokacin sanyi amma khadija taki fitowa maganar duniya tayi banza taki bude kofa tacigaba da wayarta, daga baya tace ace masa yacigaba da jira inyaga ze iya tana da abunyi me mahimmanci datakeyi.
Seda ta gama wayarta tace ace masa ya tafi bazatazoba. Saudat ta shigo dakinta tace “khadija wai dan Allah wani zazzafan kika samune haka kusan awa uku kina waya, naga duk saurayin dakikayi bakya yiwa Kabir wulakanci amma yau kin shuka masa dayawa fa” khadija tayi wani shu’umin murmushi tace “ai ke bar gara kawai, najefa fatsata a ruwa kuma da alamu nakamo kifi me nauyin gaske, ba kama kifinne matsalar ba, sedai zanyi gwagwarmaya kafin kifin yazama mallakina saboda akwai masu farautar wannna kifin dayawa abakin ruwan” ta kuma kallon Saudat tace “kodayake kince ranar biyan bukata rai ba abakin komai yakeba yar uwa, dan haka zan jure gwagwarmaya da kubale in mallaki kifin nan”
Saudat tace “kinga ni kiyimin hausar dazan gane, se wani kwana2 kikemin, nibangane mekike nufi ba”
“karki damu zaki gane very soon yar uwa”
Bangaren habib kuwa, Salma ta damu matuka baya kaiwa tsawon wannan lokacin a waje, amma yau ya kai, tayi2 yagayamata dalili yace bakomai wani abune ya rikeshi haka ta hakura.
Wasa2 taga ya maida hakan dabi’arsa baya shigowa gida se bayan goma, dataga bashida niyyar denawa itama ta watsar dashi tacigaba da sha’aninta, seta ajiye masa abincin sa akan dining tayi kwanciyar ta, hakan yakara bashi damar sakewa suyi waya da khadija.
Ranar juma’a da yamma suka shirya zasu hadu a wani gurin shakatawa, saboda khadija bataso yazo da rana gidansu Saudat ta ganshi, yarigata zuwa gurin yana zaune yanata duba agogo har yafara fidda ran kozatazo, yana kokarin kiran layinta ne, yaji kamshi me dadi yacika masa hanci, dukda yajuya baya, amma tana kallonsa tabaya tasan shine, a hankali ta tako tazo bayan kujerar dayake ta tsaya, ta durkuso da kanta a hankali tace “Hayateee barka da zuwa” ya dago kai ya kalleta daga sama har kasa, doguwar mace ce, sannan tana da dan kiba kadan, baza akirata da fara tas ba amma tanada hasken fata sosai, tabbas khadija tana da kyau dai dai2 gwargwado, murmushi yayi mata “sannu da zuwa masoyiyar boye” murmushi tayi ta zagaya ta zauna akan kujerar datake facing dinsa, suka gaisa sun sha hira sosai sannan ya dauketa ya kaita har bakin layinsu shikuma ya tafi.
Khadija tayi nasara samun zuciyar habib tana nunamasa soyayya iyayinta, haka habib yasake da khadija suke soyayya ba tareda Salma tasani ba, yakanzo gurin khadija tadi, Saudat ta fusakanci yan kwanakin nan khadija tana cikin farinciki. Bayan sun gama cin Abinci khadija ta tafi daki ta shafe kusan awa uku tana waya, a iya sanin Saudat datayiwa khadija tasan bata son doguwar waya, amma ya akayi kwanan nan take waya haka, mikewa tayi tabi khadija daki, taje ta tarar da ita tanata zuba shagwaba a waya, tana ganin Saudat ta shigo dakin tai maza tayiwa habib sallama ta mike zaune
“Saudat lafiya kuwa na ganki haka ba zato babu tsammani”
“hmm dole kice haka mana almost 3hrs kina waya, ba’a kojin mekike fada, shikam wani me nasarar ne haka? Kodai kin hadu da dream hubbyn nakine” wani kasaitaccen murmushi khadija tayi “kwarai kuwa kedai kiyitamin Addu’a”
“shine babu ko Labari balle a gabatarmin dashi”
‘mekikeci na baka na zuba, shida zezama sirinkinku sekin gaji da ganinsa “Saudat tace” Allah sarki Kabir yanata tsuma ze aureki “
Tsaki khadija tayi
” ke dalla kidenamin zancen wannan wawan, nifa badan ina tausayinsa ba da tuni na dade masa wulakanci, kodayake wulakanci na nawa, bashida zuciya ne”
“Mhmmm nikam nace khadija waime ake ciki game danawa damuwar ne, wallahi khadija ko baccin kirki bana iyayi” Ajiyar zuciya khadija tayi tace
“gaskiya Saudat ina tausaya miki, abun nada matukar tausayi, nikaina na kagu inga kinshiga wannan daula amma semunbi komai a sannu, bakisan iya kokarin danakeyi miki ba, yanzu haka nabada cigiyar in yadawo a sanar dani, naje har layin gidansa dakaina, amma ance an hana shiga layin ba tareda wanda zakaje gurinsa yasaniba, amma inata miki kokari “
” to khadija Allah yasa adace”
“zama adace kakri damu Saudat”.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122 123 124 125 126 127 128 129Next page

Leave a Reply

Back to top button