ABDUL JALAL PART 2

ABDUL JALAL PART 2

Duk ranar da Habib zezo gurin khadija tadi sedai su hadu a gidan kanin mahaifiyarta acan suke zancen, soyayya ce me karfi tashiga tsakanunsu, duk kasar dayatafi A gaggauce yake ya dawo domin ya hadu da ita, baya jure dogon lokaci basu hadu ba.
Habib da kansa yacewa khadija ze turo iyayensa ayi maganar aure, amma zeje maiduguri tukuna in yadawo seya turo, tayi murna ranar kamar ta zauce bata taba zaton a abubuwa zasu mata da sauki haka ba.
Gefe guda habib yanata tunanin, yadsa ze sanarwa da Salma batun auren dayakeso yayi, dan yasanta da matukar kishi, dan haka ya yanke shawarar zefara zuwa maiduguri in magana tayi nisa yagayawa Salma.
Koda Habib yajewa mahifiyarsa da zancem Aure bata bashi goyon bayaba hasalima faada takama yimasa “haba habib, yaushe kayi auren fari da har zakace zaka kara aure, yarinyar nan yar uwarkace fa, mahifinka da mahifiyarta uwa daya uba daya, hakan ze iya shafar zumuncinku, gaskiya ka hakura kozakayi aure ba yanzu ba” yakada yaraya amma mahaifiyarsa taki yarda, Habib tunda yake betaba yiwa mahaifiyarsa musuba se wannan karon, yaita mata magiya, karshe seda yaje yagayawa yayanta yazo yasa baki, badan tasoba haka ta amince, amma tace kafin aje neman auren se anyi bincike, akayi bincike amma bincike ya nuna khadija ba mutuniyar kirki bace, batada aibu, sedai rashin kunyarta da iya fitsara, yan uwan mahifin habib suka gayawa mahaifiyarsa nan ma ta dage tace baze yuwi ayi auren nan ba.
Khadija yagayawa khadija halin da akeciki ta damu sosai nan ta shiga addu’a ba dare ba rana, ta sanarda mahifiyarta komai sukacigaba da addu’a habib yanakin baze iya rabuwa da itaba dan haka yacigaba da lallaba mahaifiyarsa.
Habib ya canza gida, yakoma wani dankareren gida daya Gina a gadon kaya, gidane na alfarma matuka, anan ya tsara inya auri khadija ze hadasu da Salma. Bayan khadija ta tabattar da Habib ya tashi daga gidansa, taje ta samu dansandan dayake gadin rukunin quaters din dasu Habib suka tashi, tabashi kudi, ta shiryamasa abunda takeso yayi mata, sannan ta dauki Saudat sukaje tsohuwar unguwarsu Habib da nufin suje sugani yadda zasuyi kozasu samu Habib, suna zuwa dansanda dayake gadin rukunin quaters din yace musu “wakuke nemane?” khadija tace “gidan Habib kamal mukazo”
Nan yagaya musu “Ai yabar quaters din nan, tunda yadawo daga Dubai bezoba”
Da sauri Saudat tace “ina suka koma?”
“kamarya ina sukakoma dokace, da sun yadda daku dakunsan inda suka koma dan haka kubar nan gurin” khadija tai kokarin yagaya musu amma yai musu korar kare tare da barazanar ze kullesu, khadija ta kashe masa ido alamar aikinsa yayi kyau.
Habib yasha wahala sosai sannan mahaifiyarsa ta amince da maganar Aurensa da khadija, dangin mahifinsa ciki harda mahifin Salma, sukazo nema masa auren khadija gurin wan mahaifinta, sannan mahifin Salma yajawa mahifiyarta kunne kan be yadda wani yagayawa Salma Habib zekara Aure ba shida kansa ze gaya mata, dangin mahifin Habib suka kai kudin Auren Habib akasaka wata shida.
Khadija jitake kaman ba itaba, habib yagaya mata ansaka wata shida ji take yamata nisa wata shidan nan, se murna take ta tafi dakinsu Saudat cikin zumudi tana kiran sunan Saudat, tana zuwa ta tarar da Saudat tana kuka, da sauri ta karasa inda take tadafata “Saudat meyasameki haka?” Saudat ta share hawayenta ta girgigiza kai tace “bakomai khadija”
“A’a da komai gayamin menene?” Saudat ta dan gyara zama tace “khadija har yanzu burina becikaba, gashi ke zakiyi aurenki amma ni se gararamba nake, ba wani tsayayye wanda nake hangen yakasa samuwa, yanzu zakiyi aurenki ki barni” khadija ta riko hanun Saudat sannaan tace “Saudat dan adam be isa yasamu abunda ba rabonsa ba, indai habib rabonkime sekin aureshi, inba rabonkibane ba ba yadda zakiyi, shawarata agareki shine karki tsaya jiran Habib, ki bata lokacin ki, tun wuri kinemawa kanki mafita”
“khadija kina nufin in hakura gaskiya bazan iyaba kome zefaru, kedai kiyi aurenki ni zancigaba da fafatukata, sena auri Habib wallahi” murmushi khadija tayi “to shikenan Allah yabawa me rabo sa’a” daga nan ta tashi ta fice.
Habib da kansa ya shirya ya dauki Salma suka je maiduguri, yakaita gidansu da nufin tayi musu yan kwanaki, mahaifin salma yasa aka kiramasa ita dakinsa, ya zaunar da ita yayi mata nasiha sosai sannan ya sanarmata Habib ze kara Aure, ji tayi kaman mahifinnata ya watsa mata wuta, take idonta yayi jawur ta kalleshi “Aabba kan nufin Habib dinane zeyimin kishiya, kuma kake gayamin innalillahi wa inna ilaihi raji un, dan Allah Abba kacemin da wasa kake, wallahi bazan iyazamabda wata a matsayin kishiyata ba”
“Ke meye hakane? Akanki aka fara, to ki nutsu, akanme mijinki yanada halin daze auri mata hudu ya kuma iya rike su danme zakice baze aure ba, karki kuskura inji kin daga masa hankali shiyasa nace nizan gaya miki da kaina, dan haka kiyi hakuri, daba a aure dakema baze aureki ba, yakamata kija girmanki tunda kece uwargida, dan haka kiyi hakuri tashi kije Allah yayi miki Albarka ” da kyar ta mike tsaye tana tafe tana hada hanya ta tafi dakin mahaifiyarsu, tana zuwa ta zube a jikin mamansu takama kuka
” mama dama habib ze iya yimin kishiya, ko shekara biyu bamuyi da aure ba shine ze auri wata, mama anyimin adalci kenan” ajiyar zuciya mama tayi tana dan dukan bayan Salma alamun rarrashi
“kiyi hakuri Salma kinji, kuma bazamu kira abunda habib yayi da rashin kyautatawa ba tunda shima danmune, ni macece salma masan meye kishi abune me ciwo amma kiyi hakuri zakiga ribar hakurin, kiyi masa fatan alkhairi sannan karki nuna masa kin damu”
“A’a Mama bazan iyaba, wallahi zuciyata zata fashe, mama bakisan menakeji ba, bantaba mafarkin Habib zemun kishiya ba, in hakanema yabari sena kwana biyu a gidansa mana, amma yaushe mukayi auren zemun haka, toni na hakura da aurennasa yaje ya zauna da wadda yakeso” nan mama taita rarrashinta tana nunamata illar cewa zata kashe aurenta. Kwanan salma biyu a gida sannan habib yazo daukar ta, iyayen salma sam basu canza masa ba, sedai Salma fuskarta sam babu walwala zakayi zaton jinya takeyi, harsukazo kano batace masa uffan ba.
Bayan sunkoma gidama ta tattara tayi watsi dashi, bata cin Abinci sosai kullum cikin kuka take abun yafara damun habib sosai dan haka yaje ya sameta a dakinta yanzuma idonta jawur da alama tasha kuka sosai. A hankali ya karasa ya zauna kusa da ita yayi kokarin janyo ta jikinsa amma ta kwace, ya kalleta “habibty dan Allah kiyi hakuri, bazanyi Auren nan dan in wulakanta kiba, matsayinki yana nan a zuciyata kaman yadda kika sani, dan Allah badanniba kidena azabtarmin da kanki, kidinga cin Abinci kin rame sosai kindena bani kulawar da duk kike bani, please my Salma calm down” kuka takuma saki me ban tausayi, ya rungumeta ya dinga mata nasiha yana rarrashinta a irin kishi na salma be taba tunanin ze iya rarrashinta ta hakura ba, kusan kullum se iyayenta sun kirata a waya anmata nasiha da addu’oi hakan yasa tasamu raguwar radadin da take ji a zuciyarta.
Biki nata karatowa anata shirye2 amma har yanzu yan gidansu khadija basu taba ganin Habib ba, sunyi mitar sunyi harsun gaji amma taki yadda aganshi, yayyenta sunyi fada sosai dasukaji cewar ba Kabir ne yakawo kudin auren khadija ba, amma aka barshi yana wahala, amma mahaifiyarta ta goyamata baya, hatta yan anguwa bakowa yasan khadija zatayi aure ba saboda tace ba kowane garane zezo mata gurin biki ba, mussaman ma yan unguwarsu yan bakin ciki, Habib yana sakarwa khadija kudi yadda yakamata anata shirin biki. Babban abun mamakin yadda haryanzu kabir besan khadija zatayi Aure ba yana zuwa gurinta tadi, kuma yanabata abu takarba, yauma suna tsaye tagama hira da Kabir wani makocinsu yagansu, sungama tadi ya dakko uwar leda cike da kaya yabata, nan ya jinjina kai lallai wannan yarinyar tacika yar banza, aikuwa sena gayawa yaron nan, kokuma inje har gida ina sanarwa da uwarsa dan watakila idan nagaya masa wannan makirar yarinyar tace karya nake babarsa zanje ingayawa

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122 123 124 125 126 127 128 129Next page

Leave a Reply

Back to top button