ABDUL JALAL PART 2

Tirkashi
Share please
I want comments not stickers or just thanks
Daga alkalamin Aysher cool
????️????️????️????️????️????️????️????️????️????️
What’s app only 07063065680
????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????
_ABDUL JALAL (2020)_
_Story and written by_
AISHA HUMAIRA (daddy's girl)
PART 2
_PAGE 1️⃣9️⃣72
Bismillahirrahmanirrahim, da sunan Allah me rahama me jinkai, Allah yakara tsira da aminci ga shugabanmu Annabi muhammadu salallahu alaihi wassalam.
Bayan haka bazan gajiba da mika gaisuwata da godiya ga yan uwa da abokan arziki ba, bayan haka
Banyarda a juyamin littafi ba ko amfani da wani bangare ba tareda izinina ba.
Domin gyara, shawara ko sharhi, za a iya tuntubata akan what’s app number dina
07063065680
Or email address @ www.humaira17@gmail.com
_MY FIRST NOVEL_
Washegari da yamma makwabcin su khadija yatafi gidansu Kabir, dayake abokin baban kabir ne kafin ya rasu, yaje gidansu kabir yai sallama mahaifiyar kabir tayi masa iso, bakowa a gidan se ita suka gaisa da mutumin, tunda mahaifinsu kabir ya rasu jefi jefi yakanzo su gaisa shima se a shafe shekara bezo ba, suna ciki gaisawa ne kannen kabir suka shigo suka gaisheshi ya amsa yana su karimane suka girma haka masha Allah, yana nan zaune yaga suna gaganiyar fita da murhu da ice waje, seda suka gama ya kalli mahaifiyar kabir yace “suwai ba waime yaran nan suke da murhu a waje” mahaifiyar kabir tace
“kasan yanayin rayuwar ne se godiyar Allah, suna dam soye soyene a waje suna siyarwa, in sun siyar muke samun biyan bukatun yau da kullum da nauyin karatunsu, ga kuma batun aure na kokarin tasowa, ba mai yimana komai se Allah”
“Amma ina kabir, naji ance yasamu aikin kamfani kwanakin baya, ga kuma nakan ganshi wataran a kasuwa yana neman kudi, ya akayi yake barinku har se kannensa sunfita waje suna siyarda abu” Ajiyar zuciya mahaifiyar kabir tayi
“hmm lamarin kabir se addu’a inzaka yankani bansan inda yake kai kudi ba, kullum na tambayeshi se yace bashida kudi, semu shafe wata uku ko gawayin girki be saimin ba balle Insaran kayan Abinci, ficika kabir baya moramin a kudin dayake samu, haka kannensa zasu shafe tsawon likaci a gida ba makaranta saboda ba abiya kudin makaranta ba amma baze iya biyaba, tun ina magana harna hakura na zuba masa ido”
“Tirkashi anya kabir nason yagama da duniya lafiya kuwa?”
“to yazanyi, na hakura na kyale shi yaje in abunda yakemin ya kyauta yaje shima ze gani”
“to bari in gayamiki wani abu, kimanin shekaru shida kenan kabir yake zuwa gurin wata yarinya a kusa da gidana, ita yake kashewa kudadensa, yarana suna shiga gidan suna gayawa mahaifiyarsu irin hidimar dayake mata, yanzu haka yarinyar bikinta saura sati shida, shi kabir ne saniba kuma ko jiya akan idona yabata katuwar leda cike da kaya”
Zaro ido mahaifiyar kabir tayi “kana nufin dama dagaske ne kabir yana neman yarinya, a gayamin amma ban yadda ba”
“Aiko yakamata ki yadda, dan yarinyar ba karamar hatsabibiyabacce ba, ya dade yanamata wahala duk abunda yasamu ita yake bawa, yanzu kuma zatayi aurenta ta barashi, gara tun wuri kisan halinda kike ciki, ni zan tafi Allah ya kyauta gaba” haka mutumin nan yatashi yabar maman kabir da bacin rai batasan lokacin data fashe da kuka ba “yanzu duk wahalar danayi daku amma sakamakona kenan agurinka kabir, ka fifita budirwa sama dani” haka ta cigaba da kuka, da magariba kannen Kabir suka dawo daga gurin sana’arsu amma suka tarar da mahaifiyarsu ranta a bace, na suka shiga jero mata tambayoyi, bata boye musu komai ba tagaya musu, karima tace “aini na dade da sanin zancen nan, banason ranki yabacine, amma yaya kabir har adashi yake yaje ya kaimata, komai yasamu ita yake kaiwa”
“Amma karima shine baki taba gayamin ba” karima tace “to mama meye amfanin fadar, yanzu da kika sani meyakara inba bacin rai ba, ai ga sakayya nan, zatayi aure tabarshi kuma itama zata gani, dan Allah kidena kuka” haka suka cigaba da rarrashin mahaifiyarsu daren ranar mahaifiyar kabir kasa bacci tayi, mussaman inta tuna matsin rayuwar dasuke shiga amma Kabir baya musu komai yana can yanayiwa budurwa bauta.
Yau khadija ta shirya ta tafi kasuwa bata nan, mahaifiyar kabir kasa jurewa tayi ta shirya ta tafi gidansu khadija, da taje khadija bata nan se mahaifiyar khadija ta tarar suka gaisa sannan maman Kabir tace “dama nice mahaifiyar Kabir” umman khadija tace “Allah sarki sannu dazuwa, kabir yaron kirki ya kuke ya yan uwansa”
“muna lafiya kece mahaifiyar khadija?”
“eh nice ya akayi ne?”
“yanzu dama bazaku bashi auren yarinyar ba amma kuka dinga sawa yana kashemata kudi har tsawon shekara shida, ni ina can ina fama da maratun kannensa, kukuma ya tare a gurinku, ga wahala gashi yarinyar zatayi aurenta kunyi mana adalci kenan” takarasa maganara idon taf kwalla, umman khadija tace “to baiwar Allah ai se hakuri dama indai ka haifi namiji ai wata ka haifawa, kuma ita mace allura ce a cikin ruwa me rabo ka dauka, kuma kinsan halin yarn zamani ba’a iya musu dan haka se hakuri”
“Yanzu hakan yayai daidai kenan”?
“to inma beyi daidai ba aisedai kiyi hakuri” ana haka sega khadija ta dawo, batabi takan mamanta da bakuwar dasuke tareba ta shige daki abunta, mamanta ta kirata ta nunamata maman kabir tace “ke ga babar kabir nan tabiyo jin kadin ya akayi kinsan bazaki auri danta ba kika dinga ci masa kudi, itakuma baya kulada ita” kallon mahaifiyar kabir tayi tace “banda abunki aiba nina rikeshi nahanashi tafiya ba, kuma ni bance karya kulaldake ba, abunda nasani niba sa’ar aurensa bace dannafi karfin auren matsiyaci irin danki m, kidubeni da kyau banyi kalarsa ba dan haka yaje yanemi daidai da shi baniba, sannam ze iya lissafa abunda ya kashe a biyashi konawane, zan auri miji daidaidani danki shine matsiyaci se abiyashi kudinsa sekuma me? “
Bude baki mahaifiyar kabir tayi cikin mamaki “Au hakama zakice” ta juya ta kalli mahaifiyar khadija “yanzu kun kyautamin, kina kallon yarki abunda kukayi adalci ne? Shikenan kuda Allah kuma wallahi ke sekinga sakayya a rayuwarki, se Allah yabaki dan dazemiki fiye da abunda kikasa dana yaimin, kirikiri insha wahala da yayana, tun suna kanana har suka girma, amma kika kanainayemin yaro, kin hanashi ya amfanamin komai, alhalin kinsan ba aurenshi zakiyi ba, wallahi na barki da Allah” kuka sosai mahaifiyar kabir takeyi, wanda hakan ya janyo hankalin mutan gidan suka fifito tsakar gida, ita kuwa khadija tace “ai kokinki ko kinso dole kibarni da Allah dama, kabir ne naci rabona dama rayuwa ta gaji haka, kinzo se hayagaga kike mana kin taramin mutane sekace namiki sata aikin banza kawai” khadija tai tafiyarta ta shige daki haka mahaifiyar kabir ta baro gidan gwiwa a sabule tanata kuka, tana zagin khadija.
Koda mahaifiyar kabir takoma gida inta tuno abunda yafaru se tayi ta kuka, da magariba kabir ya shigo gidan, yazo ya gaisheta a fusace tace “ka tashi bana bukatar gaisuwarka kabir, kaje na yafewa diniya kai na sallamaka ga yarinyar daka fifita fiye da uwarka, kabir ashe tsawon shekaru shida kanayiwa yarinya bauta itada iyayenta, amma ni wani lokacin abunda zamuci da kannenka gagararmu yakeyi kana kallo ko a jikinka, kaje idan abunda kayimin ka kyauta kaje ga duniya nan”
“haba mama wacee irin maganace wanan wane munafikin ne yagaya miki haka?”
“dalla rufemin baki nice munafukar, har gidansu yarinyar naje yau, suncimin mutunci ita da uwatta, kuma suka tabattar min da wani zata aura, kayi asara kabir, bazanma bakiba amma hakkina ya isheka wallahi” a sukwane kabir ya mike tsaye “bangane khadija zatayi aure ba wayagaya miki?” wani takaici ne ya tokare mata a kirji wato shi ta batun auren ne ya daga masa hankali, shiru tayi ta sunkuyar da kai tanata sharbar kuka, a sukwane ya fice yabar gidan. Be tsaya ko ina ba se gidansu khadija akayi masa sallama da ita, yau yaci sa’a ta fito, ko gaisawa basuyi ba a gigice yace “khadija wai dagaske aure zakiyi”?
“injiwa?
” mama tacemin tazo gidan nan, an tabattar mata aure zakiyi, khadija ki gayamin gaskiya “
” nifa bana son wannan abun ds kakeyi ka nutsu mana, nibawani aure da zanyi da auren zanyi da bakasani ba, ka dinga bincike ka tabattar da abu kafin kazo kanamin surutu”
“Alhamdilillah har naji dadi, khadija inna rasaki bansan ya zanyi ba” dariyar mugunta tayi masa tace “kaga zankoma gida ina aikine, adinga hakuri dan ba kullum ake kwana a gado ba, kaga dama A’ayi bikin kawata ne zanturomaka 100k a account dinka inaso asamomin sababbin dari biyar biyar”
“100k dijena ai sunyi yawa, yazaki lika har hundred thousand”
“bacewa nayi kabani kyauta ba, zanturomaka ne kamin canjinsu kawai”
“dija samun sabon kudi yana dan wahala, amma zan duba miki insha Allah zan kawomiki karki damu”
“shikenan yayi kyau, ka gaida gida” daga nan ta shige cikin gida abunta.
Lokacin biki nata kuma karatowa, Salma ta rame sosai, duk tayi duhu saboda damuwa, mahaifiyar Habib da kanta tazo kano, taitayiwa Salma nasiha tanabata hakuri, sannaan tajawa Habib kunne akan ya kulada Salma, Ta hadasu tayi musu fada sosai sannan takoma maiduguri.
Saura sati biyu biki Habib tafiya takamashi, akai sa’a a ranar akakawo iv din biki, yaje dakin Salma ya sameta a kwance ya zauna a kusada ita yace “Habibty anjima zan tafi, ga katin biki an bugo ko da wanda zaki gayyata”
“Allah ya sanya Alkhairi” shine abunda tace masa kawai
“Habibty banajin dadin yadda kike shareni, nasan namiki laifi amma horon yayimin tsanani”
“dan Allah habib ka kyaleni, ka tafi karka makara”
“kina korata kenan?”
“niban koreka ba amma ka kyaleni”
“shikenan amma kimin Addu’a mana”
“Adawo lafiya Allah ya kiyaye hanya” haka ya juya ya tafi jiki ba kwari, bayan fitarsa ta dakko wayarta tana kallon hotunan bikinta da Habib tana kuka, hotunan Sauda data ganine yasataga bata kyauta ba yaushe rabon dasuyi ko waya, dan haka tasaka tshohon layinta ta kira Saudat. Ba karamin mamaki Saudat tayi ba dataga kiran Salma dan haka cikin sauri ta daga wayar
“salamu alaikum” Saudat tafada,
“wa’alaikum salam, Saudat yakike ya gida”
“lafiya kalau Salma, Salma naje gidanki ba adadi bana samunki, daga baya aka cemin kuntashi bansan inda kikakoma ba”
“eyya kiyi hakuri Saudat, kinga mun dade bama Nigeria ne, kuma damuka dawo ba dadewa munkoma gadon kaya”
“Allah sarki yanzu kina gari kenan, aiko insha Allah cikin satin nan zanzo dukda munata shirin biki” Salma tace
“Masha Allah, bikin waza’ayi? Amma ba gayyata”
“Khadija ce zatayi Aure saura 3 weeks”
“Kai kice na bugo waya a dai dai, da yanzu se ayi babuni ai yakamata inzo bikin khadija, dukda nima Habib ne zeyi Aure kusan lokaci dayane ma dana khadija” seda gaban Saudat ya fadi
“A…. Au… Aure kuma, wai wani Habib din kike nufine?”
“Hmm Saudat kenan, wane Habib kuwa, mijina mana, abun yabaki mamaki ko? Aure zeyi Saudat, amma Insha Allah zanzo bikin khadija ban manta dawainiyar da kukayi a bikina ba” cikin Saudat tace “to shikenan Salma se anjima, semun sake waya” ta kashw wayarta, mikewa tayi a sukwane ta tafi dakin khadija tana kwala mata kira
“lafiya kikemin wannan kiran, kaman wadda kikebi bashi meye haka?”
Saudat ta karaso cikin dakin tana haki ta zauna sanna tace “Khadija na shiga uku”
“Kamar ta kinshiga uku, meyasameki?”
“Ni narasa ta ina zanfara, Salma sun dawo Nigeria yanzu haka mukayi waya da ita tagayamin unguwar dasuka koma, wai amma Habib Aure zeyi saura 3 weeks, Khadija Aure zeyi nikam na kade, wallahi ko wacece bata isaba wallahi “
“to shine kika daga hankalinki haka, kemafa mijin watane kike kokarin sekin Aura, har gara ke baki Aureshin ba, ita matarsa ma bata daga hankalinta ba seke, Saudat abun nan naki yafara yawa, you better find another solution, kidena bawa kanki wahala, inbahakaba ki mutu bakiyi Aure ba”
Mamakine yacika Saudat ta kalli khadija “Au hakama zakice, dole ki gayamin haka tunda ke zakiyi Aure, to bari kiji ingayamiki wallahi kowa ze aura inze auri mata hudu seyasaki daya ya aureni, duk bala’in daza’ayi sedai ayi wallahi, matsalata tawace zanyi kokarin shawo kan matsalata inci ka burina, zanje gidan Salma sedai ai duk wacce za’ayi “
Murmushi khadija tayi” To Allah yabawa me rabo sa’a, fada da aljani ba wasa ba, kije Allah yabawa me rabo sa’a” tsaki Saudat tayi ta fice daga dakin, sosai khadija take dariya tace “sha3 zakigane bakida wayo, keda Habib har abada”
Duk yadda mutan gidan su khadija sukaso suga mijin dazata aura ki tayi , kome za’ayi sedai a gidan yan uwan babansu, amma taki yadda sam yazo gidan, invitation din daurin Aure ma hanawa tayi agani, saboda kar Saudat tagano, tayi mata hauka.
Yau khadija ta yanke shawarar zata gayawa kabir Aure zatayi zata sallame shi, yadena zuwa gurinta yaje shuma Allah ya hadashi da rabonsa, da magariba kabir yakawowa khadija wannan kudin, lokacin saura kwana takwas biki, ta karbi kudin tayi masa godiya suka gama hira zetafi tace “dan jirani ina zuwa” ta shiga cikin gida ta dakko iv ta fito, yana nan tsaye inda ta barshi ta miko masa kati. Yasa hannu ya karba yace “wannan fa?”
ba fargabar komai tace “duba kagani mana?”
Kafin kabir yagama karanta katin, yaji kafarsa na rawa, fitsari yacika masa mara
“khadija wannan invitation din na waye?”
“bangane ba bagashi a hannunka ba kana gani, sunan waye kuwa, katin Aurena ne, saura kwana takwas dama ita duniya haka ta gada, dan haka iname baka hakuri Kabir Allah yahada kowa da rabonsa, nasamu irin mijin danake mafarkin Aure dan haka
Cikin tsawa Kabir yace “Dalla malama dakata, kina nufin zaki Auri wani baniba wallahi khadija karya kikeyi, shekara shida ina wahala dake, amma kice bazaki Aureniba wallahi karya kikeyi”
“dalla dakata, kai namaka kalar auren matsiyaci kamarka, wanda se ya samo da kyar, nasamu hamshakin attajiri daidai dani kaima seka samo yar talakawa wadsa zata iya da talaucinka ku daidaita, inkana ganin bazaka hakura ba, ka lissafa nawa ka kashemin kobo bayan kobo za’a biyaka hada Riba “
” Wallahi baki isaba, kece babbar matsiyaciya kwadayayyiya, kije k Auri wani khadija, kin kyauta amma wallahi yadda nasa uwata kuka saboda ke, kema se kinyi wanda yafi na uwata, zan nuna miki ni dan halak ne, amma ki saurari matakin dazan dauka akanki, anta gayamin zakiyi Aure amma ban yadda ba yau kin gayamin da bakinki, wallahi sena wulakantaki a idon duniya, sena turamiki bakinciki mafi muni da zeyi ajalinki”
Kare masa kallo tayi tsaff sannan tace “kai kana ganin har akwai wani bakinciki, zanyi Aure a gidan Naira, zan rayu da wanda nakeso, jeka kayi abunda kaga zaka iya, khadija ce kafi kowa sanina sha3 kawai, idan nayi Aure bazaka kara ganina bama dan wahala” ta shige ta barshi a kofar gidan
Zubewa kabir yayi a gurin, yanajin kaman zuciyarsa zatayi bindiga wai yaushi khadija tabawa katin Aurenta.