ABDUL JALAL PART 2

ABDUL JALAL PART 2

Antin Jalal ta kamo Hannun Jalila da fuskarta ta jikebda hawaye tace “Jalila nagaymiki iya abunda nasani gameda rayuwar Jalal, wani abun nima har yanzu ban saniba, nasan zanbarki cikin dunbin tunani, amma Jalila bantaba zaton Akwai wanda ze iya karkata hankalin Jalal ba, duk lokacin daka dakko yimasa Nasiha ko ransa yabaci sekaga yafita hayyacinsa idonsa ya canza kala yafara jifa da abubuwa, kin dakko hanyar daidaita Rayuwar Jalal amma bata sigar dakika fara ba, duk lokacin dakika batawa Jalal rai seya gayamin, Jalila akwai abubuwa da bangayamiki ba saboda ba’a bakina yakamata kijiba, wannan tarihin danabaki nagaya mikine bisa Amincewar Jalal, yanzu mu tashi kinga azahar tayi wanka zanyi inyi Salla zamu juya.
Jiki a sanyaye Jalila ta mike suka nufi cikin gidan, Jalila kam waje tayi, ta tafi gida, tana zuwa gida ta tarar da Nana a harabar Gidan, Nana tana ganinta tace “Jalila ina kika shiga ne? Tun dazu nake nemanki nakira layinki amma wayar na daki”
Jalila batace uffan ba ta wuce daki, tana zuwa ta zube akan Gado, ta fashe da kuka
“ban kyautaba, Mummy meyasa? Meyasa kikayi haka, Ashe shiyasa Jalal yake cewa Kinfiye sonkanki, Saboda kudi da son zuciya kin bata farincikin mutane da dama, kinyi sanadin Rayuwar danki, Jalal ka yafemin bansaniba” takara fashewa da kuka

A ko yaushe ina alfahari daku masoya wannan Novel ina godiya da addu ‘oinku
Sannaan masu rokon adinga posting a Facebook insha Allah za’ a fara posting din Littafin ABDUL JALAL Facebook tundaga farko
Insha Allah, za’afara posting a group din
AISHA HUMAIRA NOVEL FANS (Daddy’s girl) dakuma sauran groups nagode sosai ❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️

Share please
I want comments not stickers or just thanks
Daga alkalamin Aysher cool
????️????️????️????️????️????️????️????️????️????️
What’s app only 07063065680.
???????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????? ???? ????

          _ABDUL JALAL (2020)_

   _Story and written by_
  AISHA HUMAIRA (daddy's girl) 

PART 2
_PAGE 2️⃣4️⃣77

Bismillahirrahmanirrahim, da sunan Allah me rahama me jinkai, Allah yakara tsira da aminci ga shugabanmu Annabi muhammadu salallahu alaihi wassalam.
Bayan haka bazan gajiba da mika gaisuwata da godiya ga yan uwa da abokan arziki ba, bayan haka
Banyarda a juyamin littafi ba ko amfani da wani bangare ba tareda izinina ba.
Domin gyara, shawara ko sharhi, za a iya tuntubata akan what’s app number dina
07063065680
Or email address @ www.humaira17@gmail.com

          _MY FIRST NOVEL_

Sosai Jalila take Hawaye, tareda surutai a hankali, Nana ce ta shigo dakin, da sauri Jalila ta goge hawayenta, zuwa tayi ta zauna ta kalli Jalila
“Jalila lafiya kuwa, meyasameki? Meyasaki kuka kuma ina kika shiga tun dazu nake nemanki” Jalila bata san wace tambayar yakamata ta fara amsawa Nana ba, Jalila ta dan girgigiza kai tace “Bakomai karki damu”
“Yazakicemin ba komai, kuka fa kikeyi”
“Nana bakomai”
“Shikenan tashi muje, Bakin su Jalal zasu tafi, taso Anty Amina tace inkiramata ke” se yanzu Jalila tasan sunan Antin Jalal dinma, ba musu ta mike suka fito tare, suna shiga gidan suka tarar dasu sunfito zasu tafi, Mahmud ya kalli Nana yace “Nana gashi zan tafi bangama ganinki ba” murmushi Nana tayi “Nima bangama ganinka ba, kaje kayi zamanka a England, memakon kadawo Nigeria muma mu amfana da iliminnaka, kaje se wani uban kumatu kakeyi”
“Allah hajiya Nana, ke bakiga yadda kikakoma bane, kinzama wata madam, yanzuma Anti Amina mukayi waya, zasu zo nan kano, shiyasa nadawo nace nima suzo dani zan dade a Maiduguri kafin inkoma England” ya kalli Nana yayi kasa da muryarsa yace “Nana wannan ce Jalila ne?”
“itace kasanta ne?”
“A’a na tambayekine kawai, naga tana kama da wata ne, just forget, bani lambarki”
“Seka biya tukuna” murmushi Mahmud yayi, “Yimata kudi ko nawane imbiya” Nana tai dariya ta karbi wayarsa tasamasa lambarta, Suna tsaye suna jira Jalal yafito suyi Sallama amma tunda Jalila taimasa abun nan da safe, ya shige daki yaki fitowa ko sallama suyi, Jawwad yanata masa magiya amma yaki bude kofar nan.
Anti Amina takamo hannun Jalila tayi gefe da ita, ta kalleta tace “Jalila kuka kuma? Meyasa? Munasa ran samun nasarar daidaita rayuwar Jalal ta hanyarki amma muga karaya a taredake, karkimana haka Jalila, banbaki labarin Jalal dan isaki damuwa ba” kaman ta ziga Jalila takuma fashewa da kuka, Rungumeta Anti Amina tayi tana sharemata Hawaye cikin kuka Jalila tace
“Anty dana san haka Rayuwar Jalal take daban zama daya daga cikin masu kara rusa farincikinsa ba nasan na dade ina bata masa Rai amma…….
” Jalila kina yimasa hakane dan inyaji haushi ya dena abunda yake nasani karki damu kinji kidena kuka”
Jalila ta jinjina kai, suka musu rakiya har mota suka daga suka tafi.
Jalila jikinta a sanyaye takoma gida, daki takuma komawa ta kule akan gado tayi shiru nan ta shiga tunani daban2,
“Kenan Kabir shine Oga Kb? , Jeje yataka Rawa gurin lalacewar Jalal, menen alakar Kabir da Jeje?” dafe kanta tayi tai tagumi hannu bibiyu tai shiru sekuma wani abu yakuma fadomata a rai
“Saudat tabawa Jalal turare, aranar yadinga karkarwa cikin dare yana firgita, kenan Saudat ma wani abun tayi masa kokuma mene? To wa zangayawa? Mema yakamata inyi ne? “
“Yasalam” Jalila ta furta da karfi tareda dafe kanta, da Hanzari Nana ta shigo dakin ta tarar Jalila ta dafe kai tana kuka
“Jalila lafiyarki kuwa? Tun dazu nake tambayarki meyasameki amma kinki gayamin se kuka kike kinga yadda idonki yayi Ja kuwa?”
Murmushin dole Jalila ta kakalo, “Karki damu kaina namin ciwo sosai, allow me to rest” ta ture Nana ta kwanta, Nana ta dade tana mamakin meyake damun Jalila haka?
Yadda Jalila taga Rana haka taga dare, banda zunzurutun tunani da tambayoyi ba abunda ke kai komo a zuciyarta, ga wani irin tausayin Jalal dake ratsa zuciyarta, antarwatsa Rayuwarsa akan abunda lokacin da ake laifin baya duniyar, gaskiya Mummy bata cancanci zama uwa ba, ta fifita duniya akan Rayuwar danta. Har gari ya waye Jalila idonta biyu,
Halima da Nana ne suka hada breakfast, nanma sukayi sukayi taci Abinci takici, Abun yafara bawa Nana tsoro, dan haka taje tagayawa Maama halin da’ake ciki
“Nono kikeso inkamota in bata ko goyata zanyi inta jijjigata?”
“Maama bahakaba, at least yakamata musan meyake damunta, kartayiwa kanta illa, tun jiyafa bataci Abinci ba tanata kuka, kinsan batada cikakkiyar lafiya fa?”
A fusace Maama tace “fita kibarmin daki, kar Allah yasa taci, inta kashe kanta aita huta”
“Amma Maama….
” Bazaki fita ba sena makeki” ba shiri Nana ta fito, ta nufi part din Jawwad amma bayanan, takira wayarsa harta katse be dauka ba, daki takoma tazubawa Jalila ido data kwanta ta rufe ido, amma hawaye nabin gefen idonta
“Jalila dan Allah kitashi kici Abinci, wallahi gaba daya zuciya ta babu dadi, na damu matuka, dan Allah kici wallahi inbaki ciba nima bazanci ba” A hankali Jalila ta bude ido, ta mike zaune ta kalli Nana tace “zubo muci, banason kizauna da yunwa”
Nana ta zuba Abinci amma Jalila ta dan cakala ta barshi.
Wunin Ranar Haka Jalila tayi duk surutun nan amma yau tsit kakeji, Nana tayi tambayar harta gaji ta samata ido.

Da daddare Jawwad ya shigo yasamu Maama a palour yake gaya mata Ankai Jalal Asibiti. Da sauri Jalila ta mike ta fito palour ta labe
Maama tace “meysameshi haka?”
“kinsam jiya yan maiduguri sunzo, kuma dai kinsam babu jituwa tsakaninsu da Mummy, andai bata masa rai yaje ya kulle kansa a daki, yafasa abubuwa sosai sannan cikinsa da yunwa ya sha wani abun bansan meyasha ba, da kyar na bude dakin dazu, naganshi a sume shine muka kaishi Asibiti, yanzu can zantafi zan kwana dashi”
Maama ta kalleshi “ohhh Jawwad Allah yayemaka wannna Jaraba, wannan yaron Jalal kullum seyajanyo abun daze hanaka hutawa, sekayi tayi ai wahalalle”
Murmushi Jawwad yayi yace “Maama kenan, ai duk dan halak baya manta alkhairi, bari in tafi seda safe” ko kallonsa bata kumayiba, har ya juya ze fita Nana tace “Yaya Jawwad amasa sannu dan Allah, kuma wallahi Baby ma inaga wani abu na damunta tunjiya kuka takeyi, taki cin Abinci da kyar nasata taci kadan”
“Haba dai? Kuma kin tambayeta meyake damunta?”
A fusace Maama tace “fita katafi inda zaka, bazasu hadu sukasheka ba kowa ya kwaso iskancinka akanka ze sauke, kaidabaka san ciwon kanka ba”
Jiki a sanyaye Jawwad ya juaya yafita, Jalila takoma daki ta kwanta tai shiru tamarasa tausayin wa yakamata taji.
Jin batun Jalal na gadon Asibiti abun yadameta.
Har gari yawaye Jalila nata kasa kunne taji wanda zeyi zancen halin da Jalal yake ciki, har wajen azahar shiru, Jalila tace “Nana naji kaman yaya Jawwad yace an kai Abokinsa Asibiti?”
“Eh acanma ya kwana, har yanzu kowaya beyoba, dazu Maama takirashi a waya amma bata shiga”
“to ya jikinnasa?”
“Nima bansaniba wallahi, amma bari mujira zuwa anjima”
Jalila ta gyada kai, ta dakko wayarta tana dubawa taga missed calls rututu
Call logs dinta tashiga tatarar da missed calls na Zahrah, Jalila ta kirata a waya bugu biyu ta dauka
“Salam alaikum, Jalila ina kika shiga tun jiya nake kiran wayarki amma ba kya dagawa”
“Am sorry ina wani mahimmin abune, se yau na dakko wayar, ya akayine?”
“Hmm Jalila sarkin Sabga, dama gayamiki zanyi anbada belin Baban Samir Fa shida duk wanda aka kamasu, shine nace kina ganin ba abunda ze faru kuwa insuka ganomu”
“Zahrah karki damu babu abunda ze faru, koda anganomu muka shirya wannan abun, to ki zame kibanni ba ruwanki balle baza’a gane ba, Burina ya cika na tonawa duniya asirin ya da Uba, duk wani cin zarafi da wulakanci dasu Saleema sukeyi dole sudena, saboda wannan mummunan abu. Kunya dasuka aikata, Amma tabbas zankuma gauraya dasu, Alhaji Kabir da Jeje, Nagode kigaida Umma” Jalila ta kashe wayarta, tacigaba da duba kiran da akayi mata takuma cin karo dana Hanan, da sauri ta kira Hanan, seda takusa tsinkewa sannan Hanan ta dauka, tace “Se yanzu zaki kirnaiko? Tun jiya nake kiranki amma kinki dagawa yar wulakanci kawai”
“Yi hakuri Hanan, lokacin bana tareda wayar se yanzu na duba nagani”
“To na hakura Allah ya temakeki, dama zamuje Bauchi nan da 2 weeks, Daddy yace zamuzo mu tambayi Abba inya yadda mutafi dake Inna taganki”
Jalila tace “Hanan zanyi murna da zuwanki, ina cikin matsala inason inganki”
“Matsala kuma Jalila? Meyafaru?”
“Hanan na dade ina tafka kuskure, yanzu ina nadamar abunda nayi, abun baze yuwu ta waya ba, nafison mu hadu”
“Subhanallah Jalila nadamar mekuma? Zaki banni cikin damuwa da tunani, ki gayamin menene?”
Jalila ta dan share Hawaye tace “Hanan for all this time i have hurting Jalal, calling him with different bad names, he is innocent, Hanan an gayamin tarihinsa, Jalal abun a tausaya masane, inajin kunyar hada ido dashi, Hanan ban kyauta ba”
“Is ok kidena kuka, ai duk dan adam baya wuce aikata kuskure, Calm down, abunda na dinga nunamiki kenan a baya amma baki ganeba, baka yankewa mutum hukunci kai tsaye akan abunda kaga yana aikatawa, idan nazo zamuyi maganar, amma ya akayi kikasan ba laifinsa bane?”
” Ai baze yuwu a waya ba, se mun hadu”
“Amma yakamata ki wanke lefinki”
“Hanan tayaya, tunda na riga nayi”
“Hakuri zaki bashi mana”
“Hakuri kuma?”
“Eh mana, yakamata kinemi ya yafe miki”
“mhmm Inasu Yaya Abdallah? Inason ganinsa ma ina neman yamin wata Alfarma inze iya”
“Wace Alfarma kenan?”
“Ina ruwanki semun hadu nida shi, ki gaida Baba”
“Hmm shikenan zeji Insha Allah” sukayi Sallama
Jalila kasa jurewa tayi ta dau waya takira Jawwad amma baya dauka, haka ta hakura.
Washegari shiru2 Jawwad be dawo ba. Har bayan Azahar gashi baya daga waya, hakan yasa Jalila ta kara shiga damuwa, ta fito harabar gidan, dan tasamu ta kadaice tayi tunani, tana nan Zaune tayi nisa sosai a tunanin tarasa ta ina yakamata ta fara, gaba daya abubuwa sun hargitse mata.
Motsi taji abayanta yasatayi saurin waigawa, Jawwad ta gani a tsaye tai sauri ta mike tsaye.
“Baby meke damunki hakane? Tun dazu nake magana amma kinyi shiru, gayamin meke faruwa?”
Murmushi Jalila ta kakalo, “Yaya Jawwad bakomai kawai dai banji bane, ina ka shiga bana ganinka nakiraka a waye baka dagawa”
“Jalal ne ba lafiya, na kaishi Asibiti na manta wayata a gida”
“Meyasameshi?”
Ajiyar Zuciya Jawwad yayi sannnan yace “jininsa ya hau, yana damun kansa dayawa, Jalal baya iya controlling bacin Ransa, yanada saka abu a ransa, ga kinsan shan taba yana kara saka hawan jini, amma Alhamdilillah jikinsa da sauki an sallameshi tare muka dawo gida” jinjina kai Jalila tayi “Allah yabashi lafiya”
“Ameen Baby, meyasamin ke kuka kika kasa cin Abinci Nana ta gayamin”
“Nikuma ai kaina ke ciwo kawai itakuma tabi ta damu, amma na warke ai”
“Anya kuwa, karya ba halinki bane, fuskarki ta nunamin kina cikin damuwa”
“bana cikin wani damuwa ni, kako ci Abinci naga kaman a gajiye kake”
“Hmm wato ba kyason incigaba da tambayarki ko?”
“bahaka bane, banaso ka zauna da yunwa ne”
Murmushi Jawwad yayi, “Ina jin yunwa kam, samomana wani abun, Jalal ma beci Abinci ba, yaki cin Abinci wallahi, nayi2 amma yaki, Yana cikin damuwa sosai, anyway samo mana abunda yasamu in lallabashi koze ci” gyada kai Jalila tayi ta juya da sauri ta tafi cikin gida.
Tana shiga palour ta tarar da Maama tana mata wani irin mugun kallon banza, Jalila ta dauke kai kaman bata san meke faruwa ba tai kitchen abunta. Ta dafa masa jallof spaghetti, ta hada da juice bayan tagaama take tunani yanda Maama ta zauna a palou tana mata kallon banza, yanzu in tace zata kaimasa Abinci wani bacin ran zata jawa kanta dan haka ta kirashi a waya tace yazo ya dauka, befi minyi bakwai ba sega Jawwad yaje kitchen ya dauki Abincin. Har yazo ze fita Maama takirashi, yadawo ya zauna a gabanta yace “Maama gani, Allah yasa ba laifi nayi miki ba”
“laifi kuma tun yaushe kake sabawa umarnina, minyi magana akan muna son hada Aurenka Naja amma har yanzu baka kumabi takan zancen ba, sekara shigewa wannan algungumar yarinyar kakeyi, ban isa ingayamaka magana kajiba ko?”
“Maama dan Allah kiyi hakuri, na yadda in Auri duk wadda kikeso, amma bazan iya Auren Naja ba”
“Jawwad kake kallon tsabar idona kake cemin bazaka iya Auren Naja ba”
“Maaama Naja yar uwata ce bazankita haka kurum ba amma…
” Yimin shiru badai akan waccan hatsabibiyar kake rawar kaiba, idan ina raye ayi ingani, tashi kabani guri”
Jiki a sanyaye cike da damuwa Jawwad ya mike yabar palourn.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122 123 124 125 126 127 128 129Next page

Leave a Reply

Back to top button