ABDUL JALAL PART 2

❤️❤️❤️❤️ ABDUL JALAL NOVEL FANS GROUP ???? ???? ???? ???? ???? ???? inayinku irin sosai din nan comments dinku nasani nishadi da bani karfin gwiwa inayinku ina kaunarku nima Allah ya barmin ku ????????????????
Share please
I want comments not stickers or just thanks
Daga alkalamin Aysher cool
????️????️????️????️????️????️????️????️????️????️
What’s app only 07063065680.
???????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????? ???? ????
_ABDUL JALAL (2020)_
_Story and written by_
AISHA HUMAIRA (daddy's girl)
PART 2
_PAGE 2️⃣8⃣81
Bismillahirrahmanirrahim, da sunan Allah me rahama me jinkai, Allah yakara tsira da aminci ga shugabanmu Annabi muhammadu salallahu alaihi wassalam.
Bayan haka bazan gajiba da mika gaisuwata da godiya ga yan uwa da abokan arziki ba, bayan haka
Banyarda a juyamin littafi ba ko amfani da wani bangare ba tareda izinina ba.
Domin gyara, shawara ko sharhi, za a iya tuntubata akan what’s app number dina
07063065680
Or email address @ www.humaira17@gmail.com
_MY FIRST NOVEL _
Gaba daya sukayi shiru suna sauraranta, tareda kallon mamaki, tacigaba da cewa “Sannan kuma zan tabattar maka da zarginka Nice kuma nasaka aka dauke Jalal ranar birthday dinsa” ta juya ta kalli Suleiman tace “Yallabai gashi nan, ku tambayeshi”
Suleiman ya janyo kujera gaban gadon Jeje ya zauna, ya kalli Jeje yace “Ya jikin naka dan uwa” da kyar Jeje ya motsa baki yace
“Da sauki”
suleiman ya gyra zama yace “Inbazaka damu ba, zamuyi maka tambayoyine gaskiya muke bukatar ka gayamana in kayi karya, zamu daukeka a haka mutafi da kai office ka warke a can, mecece Alakarka da mutumin daya yi maka wannan raunukan?”
Jeje yace “Ubangida nane, ni yaronsa ne”
“Ubangidanka kamar yaya? Aikin me kake masa, A ina kuka hadu? Yaushe kafara masa Aiki?” Jeje ya juya ya kalli Jalal ya sunkuyar da kai kasa, a fusace Suleiman yace “magana fa nakeyi maka, kabani Amsa kuma in kayimin karya seka gane kuskuren ka” Jeje ya juya ya kalli Jalal yace
“Jalal ina fatan zakamin Afuwa jin abunda ze fito daga bakina, Asalina nidan garin Azare ne, a cikin wani kauye, mahifina ya dakkoni yakawoni Almajiranci lokacin inada kananun shekaru dabasu fi takwas ba, tunda aka kawoni bawanda yakuma zuwa inda nake, balle susan halin danake ciki, sedana shekara goma shahudu sannan naje gida, kodanaje gida mahaifiyata ta rasu, nayi bakin ciki me tarin yawa nadawo kano, Rayuwar Almajiranci Rayuwace me matukar matsi da wahala, ba kula ba Abinci sabulun wanka wanki, balle magani komai kai zakayiwa kanka Rayuwa tayimin Zafi nafara shiga kasuwa domin neman na kaina, na gudu daga makaranta a haka na shiga makarantar boko, a kasuwar nan nasamu aiki a gidan karuwai nake musu aiki, a haka nakoyi shaye2, neman mata tunda kananun shekaruna, Jagaliya da bangar siyasa ba wadda ba’adamawa dani, mun hadu da Alhaji Kabiru a gurin campaign din wani ubangidansa, ninake jagorantar group din jagaliya da ‘yan daba, Alhaji Kabiru ya gayyaceni gidansa da zummar yanaso inmasa wani Aiki zena biyana, na yadda na Amince, ya nunamin hoton Jalal yace akansa yakeso inmasa Aiki, nace kamar yaya, yace soyake Jalal yazama mugun dan shaye2 dan Jagaliya kamar ni, nace masa amma tayaya hakan ze faru yacemin inyi duk yadda zanyi zena biyana duk wata dubu Ashirin, idan har burinsa yacika Jalal ya lalace ze bani wasu kudi masu yawa, Na amince na karbi Adress din Jalal nafara zuwa unguwar su, na lura yanada saukin Kai dayawan kyauta, dukda na girmeshi haka na dinga kokari ina shiga jikinsa, ina turamasa Akidar shaye2, dabe amince ba har sabani muka samu, amma daga baya bansan ya akayi ba ya Amince da kansa, Abokinsa Jawwad yayi kokari yaga ya rabamu amma abu yaki, haka nakoya masa zuwa clubs daban2 kasancewar yanada kudi kayan maye se wanda mukeso zamu sha, Nayi kokarin in koyamasa bin mata amma yaki, sam hankalinsa baya kan wannan shidai kawai yayi shaye2 Alhaji Kabiru yacigaba da biyana makudan kudade kafin daga baya ya nunamin sana’ar dayakeyi ta saida miyagun kwayoyi da makamai ta barauniyar Hanya, idan Jarinsa yai kasa senazo nasan yadda nayi na karbo masa kudi masu yawa a gurin Jalal seyaraba yabani kasona, nazama babban Aminin Jalal, Alhaji Kabiru yasa nadinga Jan ra’ayin Jalal akan mutafi Dubai semunfi holewa acan bame samana ido, mussaman shi da mahaifiyarsa take takuramasa aikuwa ya yadda, shikuma Alhaji Kabiru yahada baki da wasu ma’aikata za’asaka kwayoyi a kayan Jalal, yadda semunje dubai za’a kamashi, idan mukaje dubai aka kamashi da wannan kayan hukuncin kisa ne, Amma abun mamaki se a Airport Jalal yace yafasa tafiyar nan, Saboda Jawwad. Ba karamin fushi Alhaji Kabiru yayi dani ba, yana ganin sakacina ne, da wannnan ya wuce se muka shigo da Hanna wata karuwa cikin tafiyar tamu, Saboda tasirin mace ga da namiji, Amma duk yadda taso ta janyo hankalinsa kanta yaki, Idan yayi shaye2nsa yayi bacci A gurin wataran Jawwad ne yake zuwa ya dauke shi, muka hada baki aka shirya masa birthday party, da nufin cewa za’ayi party ne imu imu abokan shaye2nsa, Amma abun mamaki muka ganshi shida yan uwansa dasu Jawwad, muka shirya idan aka bashi kayan maye a gurin zamu faki idon mutane mu daukeshi, za’a kaishi wani gida da aka kama Hayarsa na wasu yan awanni, Zamu kai Jalal can, a gidan Akwai manyan makamai, Akwai yara kanana da aka hayo aka saka a gidan, Alhaji Kabiru ya saye wasu manyan “yan sanda da kudi, cewar za’azo akama Jalal a wannan gidan, da wannan kayan za’ace an kamashi da miyagun kwayoyi, da Makamai sannam yana safarar yara mata, Amma shima se akasa aka Sace Jalal a gurin party muka nemeshi muka rasa, shima Alhaji Kabiru yai fushi dani da kyar ya hakura, Sekuma karon karshe da Alhaji Kabiru yakamani da ‘yarsa a gidan Karuwai, da muka dau tsawon lokaci tareda ita, Yallabai wannan shine Abunda ke tsakanina Da Alhaji Kabiru ” gaba daya dakin yayi shiru, Jalal cikin Rawar murya da sanyin jiki yace
” Jeje waye Alhaji Kabiru, Menayi masa haka A rayuwa? Laifin menayi masa yazabi ganina a wannan Kazamar Rayuwar?” Jeje yace” Alhaji Kabiru shine mahaifin wannan Abokin naka Faruk, da mahaifinsa ke yawan yimasa kashedi akanka, sannan kuma shine tsohon Saurayin mahaifiyarka data Yaudara, Yasha alwashin daukar fansa”
“Shine ya zabi Ramawa akaina? Ina ina lokacin dahaka tafaru tsakaninsu? Meye Nawa a ciki? Meyasa kowa akaina yakeson daukar fansa? Meyasa? Jeje nikayiwa haka ko? Kashiga Rayuwata ka lalatamin komai, harda kokarin Rabani da Aminina Jawwad na yadda da kai amma aka hada kai da kai ana hadamin wannan miyagun tarkunan, Yanzu badan Allah ya kiyayeni ba…. Kasa karasa maganar yayi, Hawaye yafara fita a idonsa ya mike yanufi hanyar fita da Sauri, bayansa Jalila itama tabi da Sauri, tana kiran Sunansa amma kafin ta cinmmasa tuni ya hau motarsa ya kunna, ya tasheta da gudu yabar Asibitin.
Haka ta dawo dakin data bar Suleiman, suleiman ya kammala tambayoyinsa.
Jeje ya kalli Jalila yace “Kin shammaceni fiye da tunanninki, ban taba zaton karamar yarinya kamarki zata iya aikata wannan abunba, kin kassaramin Rayuwa, kisani Babu wanda ze iya daukar mataki akan Oga KB, saboda za’a sakeshi ki Saurari abunda ze biyo baya idan aka sake shi” wani mugun kallo tayiwa Jeje “Duk wani zalunci da kassara Rayuwa yabiyo bayan wanda kukayiwa Jalal, Azzalumi daga kai har uban gidan naka, Kaike min kallon karamar yarinya, duk abunda nasa gaba sena ga bayansa, zamu gani nagama da babinku har gaban Abada, kuma ka saurara kagani ko ansakeku zalincin dakukayi baze barku ba” Ganin Jalila ta dau zafi sosai yasa suleiman yace “Kwantar da hankalinki, ki share hawayenki wanda zan dankawa case din shima wanine, za’adau matakin daya dace, kaikuma ina gurin kake wannan maganganun ko? Ka kara daure kanka zaka gane bakada wayo” sannan ya kalli Jalila yace “Shi waye wannan din? (JALAL) Jalila tace” Yaya nane”
“Gaskiya an cutar dashi Sosai, and he needs counseling, kusa ido sosai akansa sannan ku kuladashi, ajashi a Jiki a dage da Addu’a har Allah yasa a raba shi da shaye shayen nan”
“Hakane Insha Allah za’ayi kokarin hakan,
” Yawwa yanzu dai muje in ajiyeki a gida ko? “
” A’a ka ajiyeni a hanya dai” Yai murmushi yace to muje.