ABDUL JALAL PART 2

Ilham dake labe a kofar dakin sedata kusa rusa ihu, da gudu ta tafi dakinta ta rufe kofa tana sintiri, nashiga uku idan Dagaske Jalal yafara neman mata ina na kama, menene makomata? Kan bala’i hakan na nufin lalacewar komai fa? Amma wacece tazo gurin nasa? Ina baze yuwu ba, idan har Jalal yafara neman mata bazamu samu komai ba gaba daya shirinmu ze lalace ne, dole inje inga umma a yau din nan jakarta ta dauka ta zuba kudi tayi waje da sauri tafita ta tari napep ta nufi gidansu.
A sukwane Ilham taje gidansu, ta tarar da mamanta a tsakar gida tana tankade, “Umma akwai matsala ajiye tankaden nan ki tashi”
A sukwane tace “ke lafiya kike wannan rawar jikin?”
“nikam ki ajiye tankaden nan kitaso akwai matsala”
Jan hannun mamanta tayi sukayi daki ta zauna a gefen gado tace “Umma akwai gagarumar matsala, mahaifin Jalal yace yafara neman mata, wai wata yarinya tazo neman Jalal, be fadi me tace masa ba, amma yace yana zargin yafara neman mata, idan haka ta faru mu menene makomarmu?”
“ki kwantar da hankalinki kitashi kikoma tun kafin su gane wani abu, ki bar komai a hannuna gobe da kaina zanje gidan malam, ya bincikamin tsawon shekaru mutumin nan yana mana aiki, bamu taba samun matsala ba dan haka bana tunanin za’a samu wannan matsalar “
” gara dai kije da gaggawa kar asamu matsalar wannan karon, dan ina cikin matukar tashin hankali “
” bakomai ki tashi ki tafi”
Sukayi sallama Ilham ta taho.
Gaba daya hankalin daddy yagama tashi, yarasa nutsuwa gaba daya, yana murna yana ganin Jalal yafara rage wasu abubuwan amma kawai ace wannan mummunan tashin hankali da abun kunya na gabato family dinsu. Ganin duk ya tashi hankalinsa yasa Mummy tasame shi tace
“Hayatee wannan damuwar ba iyace mafita ba, nasha gaya maka abaya Yakamata ayiwa Jalal Aure, Namiji ne me cikakkiyar lafiya dole ya bukaci abokiyar rayuwa, amma wakake tunanin zebawa Jalal Auren ‘yarsa a wannan halin nasa, shiyasa nace tunda Ilham ta nuna tana sonshi a haka kima’ yar uwassa ce, kayadda a hada Auren nan, shine rufin Asirin mu, kila ma kaga ya dena abunda yake”
Daddy yai ajiyar zuciya yace “bakin Auren Ilham da Jalal nake ba, ina gudun abunda ze biyo baya ne, kinsan halinsa inbayason abu, yace baya son yarinyar nan, tunda yace bayaso ko anyi Auren nan wahala zata sha”
“Haba Hayatee kafison yadakko maka magana atukuna, a wajene yake cewa bayaso, da anyi abun zakaji shiru sun zauna lafiya amma kayi tunani, ina tunanin ayiwa Jalal Aure shine mafita, tunda banajin ma yanada wata wadda yakeso giyarsa ce kawai ta dameshi, inaga yiwa Jalal Aure shine mafita”
“to shikenan zanga abunda Yakamata nayi, Amma hankalina tashi sosai”.
Bayan sallar magariba Jawwad yasa Jalal agaba da mita
“Gaskiya Jalal bana son wannan zaman gidan da kakeyi kadena walwala, kadena farinciki kullum a daki, bana son hakan, inaga zan duba mana wani business mufara kadena wannan zaman, dan haka zanyi tunani business zamu fara”
Jalal yai murmushi yace “Dama ina son yimaka magana, Daddy yacemin yasamomaka aiki amma kaki yadda katafi, karka damu dani Jawwad ka karbi aikinka ka tafi senafi kowa murna, Saura kuma muzo musha bikinka da Hanan, ko angon Hanan?”
Ajiyar zuciya Jawwad yayi yace “Jalal nina rasa mekemin dadi ma, Maama ta matsamin akan Auren Naja, kullum yarinyar nan setayi abunda zatajamin fada a gurin Maama, narasa yadda zanyi da ita”
“Kaine bakayi maganinta ba”
“Kamar yaya kenan?”
“Keje kasamu Abba ka gayamasa yanema maka Auren Hanan mana”
“Taya Jalal? Jalila tana sona idan na Auri Hanan ban kyauta ba Jalal”
“kana maganar kana son ta tana sonka amma meye makomarta agurin mahaifiyarka da danginta?”
Jawwad yai ajiyar zuciya yace
“Kasan wani abu makuwa?”
“A’a seka fada”
“Hanan tace min wai soyayyar ‘yan uwantaka ce tsakanina da Jalila, Akwai wani a zuciyar Jalila, amma kana ganin hakan ze iya yuwa?”
Jalal ya dan kalli Jawwad yace
“Hmm Maybe, nidai fatana kaje ka karbi aikin nan kawai da daddy yasamo maka in bahakaba nida kaine”
Jawwad yai murmushi yace “Jalal kenan sedai mutafi tare”.
Abbaa ya kira Jawwad dakinsa, gashi ga Mummy Jawwad ya shiga ya zauna yana fatan Allah yasa ba wani laifi yayi ba.
Abba yace
“Yayana na kaina, Maamanka tazomin da wani batu, shine nace yakamata ingaya maka kafin in aiwatar”
Jawwad yace
“to Abba na ina jinka”
“Yawwa Jawwad, Maamanka tace tanason hada Aurenka da Kanwarka Naja, kuma nan da sati biyu takeso akai kudin Auren, sannan ka karbi aikin da’aka sama maka, in anyi Auren se ku tafi can tare”
Duk wata jijiya ta jikin Jawwad seda ta dan tsaya na wucin gadi, gaba daya jikinsa yayi shock, cikin dakiya yace
“To Abbana, Allah ya tabattar mana da Abunda yafi Alkhairi gaba daya”
Maama tayi murmushi tace
“in ankai kudin banason asa fiye da wata shida”
Jawwad yace “to Maama Allah ya temakemu”
Abba yace “ina fatan dai ba’a matsa maka ba, inkana da magana ka fito kayi”
Jawwad yace “A’a Abba babu wata damuwa”
“to shikenan Allah yamaka Albarka”
Haka Jawwad yafito daga dakin jiki ba kwari ya tafi dakinsa ya kwanta
Jalal yayi mamaki jin shiru Jawwad bezoba yau, dan haka ya mike domin yaduba Jawwad, daddy ya kirashi a waya yace yana son ganinsa a cikin gida.
Cikin gidan ya nufa, ya nufi palourn daddy amma yana zuwa ya tarar da
Daddy, Mummy, dakuma Ilham turus yayi ya tsaya yana kallonsu daya bayan daya, yasan akwai wata kulalliya
Ina yinku ABDUL JALAL group irin sosai din nan fa ???????????? inajin dadin Comments dinku, kuna Comments kana karamin kaimi typing duk bayan kwana biyu, kuna bari ina lalaci posting duk sati ????????????
Share please
I want comments not stickers or just thanks
Daga alkalamin Aysher cool
????️????️????️????️????️????️????️????️????️????️
What’s app only 07063065680.
. ???????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????? ???? ????
_ABDUL JALAL (2020)_
_Story and written by_
AISHA HUMAIRA (daddy's girl)
PART 2
_PAGE 3️⃣3️⃣86
Bismillahirrahmanirrahim, da sunan Allah me rahama me jinkai, Allah yakara tsira da aminci ga shugabanmu Annabi muhammadu salallahu alaihi wassalam.
Bayan haka bazan gajiba da mika gaisuwata da godiya ga yan uwa da abokan arziki ba, bayan haka
Banyarda a juyamin littafi ba ko amfani da wani bangare ba tareda izinina ba.
Domin gyara, shawara ko sharhi, za a iya tuntubata akan what’s app number dina
07063065680
Or email address @ www.humaira17@gmail.com
_MY FIRST NOVEL _
Kara hade rai yayi ya shiga palourn ya zauna becewa kowa komai ba ya zauna, daddy ya kalleshi yace “son ka tashi lafiya”
“Alhamdilillah” daddy yai murmushi yace “Masha Allah, kayi breakfast ne?”
“A’a ina jiran Jawwad ne kuma bezoba”
“bari a hada maka anan kaci” daddy ya kalli Ilham yace “Ilham hadawa yayanki Abinci mana”
Jiki na rawa ta mike ta nufi dining din daddy ta hado masa kayan breakfast ta kawo ta ajiye, shidai be kulata ba ya zauna yafara cin Abincin sa, daddy suka cigaba da hirarsu shidasu Mummy, shidai Jalal bece musu uffan ba, yana kammala cin Abincin sa ya mike ze fita, daddy ya dakatar dashi ta hanyar cewa “Ina kuma zakaje? Zamuyi magana ne ai”
Dawowa yayi ya zauna yana kallon daddy, daddy yace “Jalal kaga zamanka haka baze yuwu ba, tunda ansamu degree daya da kyar, kaga shekarunka sun fara Ja daga kai har Jawwad zuwa yanzu yakamata ace ansama maka abokiyar rayuwa a matsayinka na namiji, amma bantaba jin kacemin ga budurwarka ba, ko akwai wata bansaniba “
Wani irin kallo Jalal yayiwa daddy sannan yace” dan Allah adena wannan zancen, in lokacin Auren yazo za’ayi, amma dan Allah for now a kyaleni”
“A’a Jalal babu batun a kyaleka, banason cigaba da ganinka a haka ba Aure, bakasan Aure shine cikar mutum ba, inma baka da budurwa ne ga Ilham tace taji ta gani tana sonka a haka, meye laifin Ilham? Dan haka nakiraka tunda kaida Ilham duk dayane”
“A zato na a baya munyi wannan Maganar ta wuce? Wannan tamkar maida hannun agogo bayane, nace bana sonta, bana sonta akan me za’a takuramin, kuma ai naga Aure ba wajibi bane, balle ace in banyiba nayi laifi, dan haka a kyaleni bana sonta bazan Aureta ba”
A fusace Mummy tace “Baka isa ba wallahi, da abun kunyar da kake shirin jawomana gara aimaka Aure, kokana so kobakaso Aure se anyi shi”
“Abun kunya na nawa kuma? Koke har yanzu abubuwan da nakeyi basu isheki kunya ba? Nagama magana ba wanda ya isa yamin Auren dole wallahi, duk duniya natasani wannan yarinyar natsani duk wani abu da yashafeta, Aurene bazan Aureta ba”
Ilham ta rushe da kuka tace “Nashiga uku Mummy, menayiwa Yaya Jalal haka?”
Mummy tace “rabu dashi, Aurene babu fashi, tunda yasan yafara biye biyen mata, har karuwai sufara biyoshi gida, rashin mutuncin sa ya wuce yaje ya samesu a can, se yafara kawosu gida, ai dole a dau mataki akansa”
daddyn Jalal yaso ya hana Mummy karasa maganar amma seda ta karasa, Jalal dake shirin fita ya tsaya cak ya juyo
“Niza kiyiwa sharri dan nace bana son wannan shashashar, Nine nakebin mata, kirasa dame zaki alakanta ni se wannan mummunan Aiki, to wallahi da in Auri Ilham gara a dauramin Aure da Akuya, Nagode da sharrin da kika yimin a matsayinki na uwata”
“Ba sharri tayi maka ba Jalal, gaskiyane” juyowa yayi inda daddy ke magana, nan da nan idonsa ya canza ya harzuka matuka yace
“daddy da bakinka? Kaima ka yadda zannemi matan banza? Ka yadda ni Jalal zan kawo karuwa cikin gidan nan? Ka yadda ni Jalal ina neman matan banza, lalacewata bata kai haka ba” daddy yace
“Ya isa Jalal, ba sharri akayi maka ba, ni yarinyar tasamu a waje tace gurinka tazo, ita tacemin Akwai alakar dake tsakaninku wadda bata kamata inji ba, kuma lallai insaka Aureta shine kawai hanyar tsira da mutuncinta da naka, ka gayamin meye hakan inba neman mata kake ba?”
Shiruu Jalal yayi ya marasa meze ce, mamaki gaba daya ya kamashi, a iya tunaninsa babu wadda zatayi masa haka, su Jeje ne kuma zuwa yanzu suna hannu kodai duk shirin Mummy ne haka? Amma a tunanin sa be cancanci daddy yayi masa wannan mummunan zargin ba, ba tareda yayi bincike ba ana alakanta shi da dabi’ar dayafi tsana a rayuwarsa wato zina.