ABDUL JALAL PART 2

ABDUL JALAL PART 2

Jalila na zuwa Hanan tafara yimata tambayoyi “Jalila wai waye Yaya Yusuf yace kinyi bako?”
“ke kyaleni dan Allah wani ne nina manta sunansa ma, Hanan satin nan, maybe nan da kwana uku zankoma Kano”
“Jalila meyasa? Saboda Yaya Yusuf?”
“A’a Hanan Akwai matsala ne, dole inkoma”
“Matsalar mene haka? Jalila kar mutan gidan nan su zargi ko wani lefi sukayi miki”
“bahaka baneba Hanan, Ankoma makaranta sannan ina bukatar zuwa gida”
Hanan tace “hmm ko dai saboda Jalal ne? Gayamin wani abune yafaru dashi ne?”
Cikin damuwa Jalila tace “Hanan dagaske Jalal yake in yabar kasar nan baze dawo ba, wai anyi masa wani abu a gidansu, fitarsa kasar waje hatsari ne” Jalila ta boyewa Hanan batun kai kudin Auren Jawwad kar Hanan ta damu.
Hanan taso ta tsokani Jalila amma ganin ta in serious mood yasa ta fasa tace “gaskiya yakamata kikoma bari daddy ya dawo se muyi masa magana”
Yusuf ne yayi knocking kofar dakin nasu sannan ya shigo da sallama ya kalli Jalila yace “Jalila yaya kun gaisa da Captain Ahmad?”
“Eh yaya Mungaisa”
“to bazamuyi miki dole ba, kigaya masa abunda ke ranki, inkinada wanda kikeso kigaya masa tun wuri”
“tana da wanda takeso fa, tana jin nauyin kane bata fada ba”
Yusuf yace “inkika kuma magana sekinyi tsallen kwado sau sittin a gurin nan, dake nake magana?”
Shiru Hanan tayi yacigaba da cewa “Jalila banason mu cutar dake gidan nan ba’ayi wa kowa dole, nayiwa daddy maganar, in ba kyasonsa ki gaya masa kinji”
Jalila ta gyada kai, yace to seda safenku.
Yusuf na fita Hanan tace “ke Jalila captain Ahmad ne dama, to tun wuri kice masa bakya sansa, har sunkai magana gurin daddy Yaya Yusuf baya wasa, wallahi dagaske suke, in Baba ya tambayeki kice be mikiba ba kya sonsa, kinada wanda kike so”
“Haka nace miki bana sonsa? Wanake dashi a yanzu danake so? To ni yayi min”
“karya kikeyi wallahi, Jalal shine kike so, ba wani aranki seshi”

Ina yinku ABDUL JALAL group irin sosai din nan fa ???????????? inajin dadin Comments dinku, kuna Comments kana karamin kaimi typing duk bayan kwana biyu, kuna bari ina lalaci posting duk sati ????????????

Share please
I want comments not stickers or just thanks
Daga alkalamin Aysher cool
????️????️????️????️????️????️????️????️????️????️
What’s app only 07063065680.

???????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????? ???? ????

          _ABDUL JALAL (2020)_

   _Story and written by_
  AISHA HUMAIRA (daddy's girl) 

PART 2
_PAGE 3️⃣4️⃣87

Bismillahirrahmanirrahim, da sunan Allah me rahama me jinkai, Allah yakara tsira da aminci ga shugabanmu Annabi muhammadu salallahu alaihi wassalam.
Bayan haka bazan gajiba da mika gaisuwata da godiya ga yan uwa da abokan arziki ba, bayan haka
Banyarda a juyamin littafi ba ko amfani da wani bangare ba tareda izinina ba.
Domin gyara, shawara ko sharhi, za a iya tuntubata akan what’s app number dina
07063065680
Or email address @ www.humaira17@gmail.com

      _MY FIRST NOVEL _

Tsaki Jalila tayi, taje ta dakko trolley tafara zuba kayanta, A daren Jalila taje tasamu dadyn Hanan tace masa zata koma gida jibi saboda sunkoma makaranta, daddy beji dadi ba yacewa Jalila da kansa ze maida ita gida.
‘yan gidansu Hanan sunji babu dadi batun tafiyar Jalila, sun mata Alheri sosai, Inna ma taji babu dadi, tace itama wataran zatasa akaita kano gurin Jalila, ranar da Jalila zata koma tun safe tagama shirinta tsaf, karfe goma na safe daddyn Hanan da kansa yasa Jalila a mota ya tafi kai Jalila gida, suna tafe suna hira.

Jawwad yayi duk yadda zeyi ya hana Jalal tafiya amma wannan karon Jalal ya dage, yayi rantsuwa yace seya tafi sannan yaki gayawa Jawwad hakikanin abunda akayi masa a gida, Jawwad ya tafi gidansu Jalal yasamu daddy bayan sun gaisa yace
“daddy me akayiwa Jalal ne yace in yatafi baze sake dawowa ba, bansan me akayi masa ba”

Nan daddy yagayawa Jawwad abunda yafaru. Jawwad yace
“Amma daddy meyasa kake zargin Jalal akan wannan, daddy zan iya rantsuwa da Alqur’ani Jalal baya neman mata, koma wacece sharri take masa daddy”

“Jawwad se daga baya naga nima ban kyauta masa ba, ka bashi hakuri, yadena fushi da daddyn sa, amma kokana da masaniyar dalilin dayasa Jalal ya tsani Ilham, ko tayi masa wani abun ne?”

Jawwad yayi Jim sannan yace “A’a daddy nima bansaniba, ban san metayi masa ba”
“Anya kuwa Jawwad zan yadda bakasan komai ba?”
“daddy dagaske nake bansan komai ba”
“to shikenan, amma Jawwad dan Allah kahana Jalal tafiyar nan, nasan yana fushi dani, amma karya tafi ya bar daddyn sa”
“Insha Allah daddy zanyi kokarin yin hakan”

Jawwad ya tashi ya fita, tun lokacin da Abba yayiwa Jawwad zancen kai kudin Auren Naja yake rashin lafiya amma be gayawa kowa ba, ga kuma tension din Jalal, yakoma daki ya tarar Jalal yanata hada kaya, ya zura masa ido, yarasa mema zece masa, kansa ne yake sarawa sosai ya kwanta akan doguwar kujera ya lumshe ido, yanata sakawa yana kwancewa.

Nana tasan da dawowar Jalila dan haka tanata murna, tana shirye2 itakuma Naja so take Jalila ta dawo ta kuntata mata rai.
Karfe biyu na rana Su Jalila suka iso kano, Nana ta fito ta taresu ta rungume Jalila suka dinga murna, Abba baya gari, ya tafi da Maama lagos, kwanansu uku da tafiya, dan haka Jalila ta budewa daddy sitting room ya zauna.
Nana ta dauki kayan Jalila ta shiga dasu cikin gida, ta kawowa daddy ruwa da lemo da Abinci.
Duk abun nan, Jawwad besan su Jalila sun dawo ba, Jalila da kanta ta tafi part din Jawwad tana shiga palourn sa ta tarar da Jawwad a kwance akan kujera ya lumshe ido Jalal kuma yasa TV a gaba amma sam ba tv yake kallo ba tunani yakeyi.
Sallama Jalila tayi, sallamar tata ce ta dawo dashi daga dogon tunanin da yakeyi, be taba zaton kafin ya tafi zega Jalila ba, seda suka danyi seconds suna kallon kallo, dauke kanta tayi ta nufi gurin da Jawwad yake kwance,

“Yaya Jawwad” ta kira sunansa amma be amsaba, hannu takai ta dafa goshinsa yayi zafi sosai da sauri tace “Subhanallah” dan girgiza shi tayi,
A hankali ya bude ido yana kallonta murmushi yayi mata yace “Baby saukar yaushe haka ba Labari?”
Cikin kulawa tace “Yaya Jawwad baka da lafiya ne haka”?
Mikewa yayi zaune yace “kai amma nayi murna da dawowarki, munyi missing girkinki da kiriniyarki”
“Yaya Jawwad keep jokes aside ka rame sosai baka da lafiya, nakira layinka baka dagawa, Hanan ma ta kiraka amma bata shiga, yanzu daddyn Hanan ne ya kawoni, yana son ganinka”
Jawwad yace “Shikenan bari inje”
Jalal ya kalli Jawwad yace “dagaske baka da lafiya? Meyasa baka gayamin ba?”
Jawwad yace “meye Amfanin gaya maka banida lafiya? Kaika gayamin dalilin dayasa zaka bar kasar nan? se dazu daddy ya gayamin abunda yafaru, kuma matakin da kake shirin dauka shine ya dace? Gaba daya hankalina a tashe yake Jalal, ni bakasan a matsalar danake ba, gashi kaikuma da maganar dakazomin, gaba daya hope din iyayenka akaina yake, bakaga magiyar da daddy yakemin akan kar inbari ka tafi ba narasa yadda zanyi ba dole rashin lafiya ta kamani ba, gaba daya narasa meyake min dadi” gaba daya tausayin Jawwad yakama Jalila
Jawwad Ya mike ya fice a dakin ba tareda Jalal yace masa uffan ba, Jalila ma bayan Jawwad tabi.

Ba karamin tausayi Jawwad yabashi ba, shikansa yana tunanin yin rayuwa ba tareda Jawwad ba, amma yana daga cikin dalilansa na son barin kasar nan yanaso Jawwad yasamu kwanciyar hankali, ya karbi Aiki ya hutawa ransa dawainiyar daya dingayi masa tsawon shekaru a ganinsa wannan ce kawai hanyar dazewa Jawwad halaccin abunda yayi masa.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122 123 124 125 126 127 128 129Next page

Leave a Reply

Back to top button