ABDUL JALAL PART 2

ABDUL JALAL PART 2

Jalila ta fuskanci idan tayiwa Jalal rashin kunya yadda yake a fusacen nan ze iyayi mata ba dadi, dan haka ta kwantar da murya tace
“Shikenan is Ok, samu guri ka zauna zamuyi magana”
Cikin tsawa yace “bazan zaunaba, kibani passport dina”
“Idan baka zauna ba bazan gayamaka inda yake ba, Zauna tukuna”
Seda ya danyi jimm sannan ya zauna, ta zuge jakarta ta dakko ruwan da ta siya zata sha, ta bude ta mika masa, ba musu ya karba ze fara sha tace “Kayi Bismillah” seda ya dan harareta sannan yayi ya shanye ruwan se sauke numfashi yakeyi saboda bacin rai
“Kasan wani abu? Nina ga passport dinka akan center table na dauka, sannan nina saka aka soke maka visa”
Tsareta yayi da ido amma bece komai ba
“banyi haka dan inbata maka ba, nayi hakane dan sama maka mafita, kasan hukuncin me sabawa iyaye, muddin kayi tafiyar nan bada san ransu ba zaka iya samun matsala, Abokin Yaya laifin da mahaifiyar ka tayi maka wannan tsakanin tane da mahaliccinta, Amma abunda kake mata ba dai dai bane ba, kamata yayi ku zauna lafiya cikin hikima ka nunamata kuskuren da take aikawa, na baka misalai wancan karon daka kusa karyamin hannu, inkaji kaddarar wani zakaga taka ba komai bace ba, nima misali ce a gareka, na tashi ba mahaifi Allah ya karbi abunsa inada karancin shekaru, ga tsangwama saboda mahaifiyata daga baya ta musulunta, yanzu itama babu ita bansan a ina take ba, Natashi da kaunar Yayana, amma mahaifiyarsa batasona inaji inagani saboda kar mahaifiyarsa tayi masa baki na sadaukar da soyayyata na hakura “
Ta danyi shiru hawaye nabin fuskarta “ABDUL nasan dacin a tsangwami mutum amma kai da gatanka kana tareda iyayenka, kana da gata, suna kaunar ka wata kaddarace ta gifta dazaka iya gyarata, yau inka dena shaye2 ka gyara tsakaninka da Allah da iyayenka ze wuce kamar bakayi ba, nikuwa fa? Nasani ko Aure nayi se an gorantamin rashin dangin uwa, na ubanma waye Abba ne kawai, tare kuke da Yaya Jawwad kasan komai wani abunma ni bansaniba, Why Jalal, wanda yarasa iyaye yayi kuka, kai kana taredasu amma idonka ya rufe”
Sosai Jalila take kuka, yayinda jikin gogan yayi sanyi gaba saya, Jikin Jalal yayi sanyi matuka, kura mata ido yayi, yana tuno lokacin dasuke mata wasa shida Jawwad yana tuno abubuwa dasuka shude gaba daya tausayinta ya kamashi, handkerchief ya dakko a Aljihunsa, yana goge mata Hawayane yayinda taketa sheshaekar kuka kaman wanda akayiwa dole yace
“kidena kuka please”
“Ni kylaeni bazan dena ba din” tasa hannu a jakarta ta dakko passport din ta aje masa “ga passport dinka nan, seka dawo” tana kokarin tashi seji tayi yace
“Aina fasa” tsayawa tayi tana kallonsa
“Eh dagaske nafasa”
“Meyasa kafasa?”
“da farko kin dakukemin passport, kuma kin lallaba kinsa an sokemin visa daya zan tafi?”
“Kayi hakuri nasan kaji ba dadi abunda nayi, amma zaka iya nema na wani kasar katafi”
“Nafasa amma ya akayi kikasa aka soke visa na”
Ta goge hawayenta sannnan tace “daddy Hanan nagayawa ranar dazamu dawo, shine yace kar indamu zssa a soke”
Jinjina kai yayi ya danyi shiru tace
“nika tashi ka maidani”
“Saboda me?”
“Saboda haka nace, meyasa zaka kawoni inda ban saniba, ga gidan bakowa ni gaskiya ka maidani”
“hmm hakane nan inda baki sani bane, zan maida ke amma sekin gama kukan, nan gidanmu ne na gadon kaya inda aka haifeni, inda nayi rayuwa me dadi, dukda ba me dadi ce yadda nakeso ba, amma nayi Rayuwa dani da Jawwad daddy Rayuwa me cike da jin dadi” ya mike tsaye yace ‘ina zuwa”
Ya hau kan benen ya dan jima sannan yafito da wata Jaka a hannunsa duk ta danyi kura, yadawo yasamu guri ya zauna, har yaje ya dawo Jalila bata dena kukan datake ba, yasa hannu ya dan karkade Jakar sannan ya bude zip din, wasu uban hotuna ne aciki masu tarin yawa, yasa hannu ya debo wasu, ya mikawa Jalila, tasa Hannu ta karba tafara dubawa a tsanake, fuskarta sharkaf da hawaye amma hoton farko data gani yasata yin murmushi, Jalal ne da Jawwad suna kanan basufi shekaru biyar ba sun zazzaro ido suna sanye da kaya iri daya, haka ta dinga kallon hotunan tana dariya, galibin hotunan hada Umminta a ciki kan wani hoto taje, Jalal ya nutsu ya dauki wata Jaririya yana kallon ta,
Tace “Wannan wacece? Kanwarka ce”
“gata nan dai kalleta baki gane wace ba?”
Jinjina kai tayi alamar Eh, karba yayi yakuma duba wani yabata yace “wannan fa” itace batafi shekara biyu ba Idonta duk hawaye Sunsata a tsakiya
Ba karamin dariya hoton yabata ba “Wannan ai nice”
“wancan ma kece ai”
“to a ina kasamu wannan hotunan haka”
“Abee yanada camera da, shiyake mana hotuna in aka wanko daya abawa Ummi daya abani nake tara nawa, wasu kuma a gurin ummi na karbesu, wasu hotunan bani dasu suna gurin Ummi”
“lallai ka iya Ajiya”
Nan tadinga kallon hotunan, har hoton Iyayen Ummi akwai seda ya nuna mata, gaba daya ya manta da fushin dayakeyi, ita kuma ta manta tanada lectures
kan wani hoto ta kai, Ummice a jiki da Abeenta, sunsakata a tsakiya duk sun kalleta suna murmushi, ta tsaya ta zubawa hoton ido, sekuma Hawaye ya shiga zubowa daga idonta kuka sosai
Jalal yai kuri da ido yana kallon ta, hannu yasa ya zare hoton
“Bani tunda kuka zakiyi, ban hotuna na”
Cikin kukan tace “yi hakuri na dena”
“baza’a hakuran ba, bani nan”
Yasa hannu ya tattare su, rikewa tayi “dan Allah kabari in karasa”
Yana kokarin fizgewa ne hotunan suka zube a gurin, idonta ne yakai kan wani hoto dayasa taji hantar cikinta ta kada.
???????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????? ???? ????

          _ABDUL JALAL (2020)_

   _Story and written by_
  AISHA HUMAIRA (daddy's girl) 

PART 2
_PAGE 3️⃣6️⃣89

Bismillahirrahmanirrahim, da sunan Allah me rahama me jinkai, Allah yakara tsira da aminci ga shugabanmu Annabi muhammadu salallahu alaihi wassalam.
Bayan haka bazan gajiba da mika gaisuwata da godiya ga yan uwa da abokan arziki ba, bayan haka
Banyarda a juyamin littafi ba ko amfani da wani bangare ba tareda izinina ba.
Domin gyara, shawara ko sharhi, za a iya tuntubata akan what’s app number dina
07063065680
Or email address @ www.humaira17@gmail.com

      _MY FIRST NOVEL _

Da sauri ta dauki hoton tace “Wannan wacece?”
Karba yayi ya duba sannan yace “bakisan wannan ba? Kakarkuce wadda ta haifi su Abba”
“Wannan ai kakar su Hanan ce”
“kamar yaya?” ya tambayeta cikin rashin fahimta, nan ta kwashe komai tagaya masa na zuwanta bauchi jinjina kai yayi yace “masha Allah, nina san wannan kamar da kuke ba’a banza ba, tabbas abunda kakar Hanan tagaya miki haka yake, Sun baro garinsune saboda hari da ake kaimusu, amma yanzu karkiyi saurin fada, Abba yakamata kifara samu da wannan maganar, ya dade yana bincike ko Allah zesa yasamu wani daga dangin iyayensa, tunda basu san kowa ba daga family dinsu, Inna kawai suka sani da baba”
“Allah yasa gaskene Su Hanan ‘yan uwan su Abba ne, inda suke sunada yawa sosai estate ne guda gaba daya family dayane”
“‘ yan uwankune Insha Allah, bari in mayarda hotunan nan se in maida ke”
Ta gyada masa kai ta jirashi ya mayar ya dawo, ya kalleta yace
“muje ko”
Ta wuce gaba ya biyo ta abaya ta tsaya ta wigo ta kalleshi “dan Allah karkayi wannan tukin, dan Allah” bece komai ba ya bude motar ya shiga, itama budewa tayi ta shiga ya kunna motar, aka bude masa gate ya fita, masu gadi nata daga masa hannu amma yayi musu banza,
“Suna maka magana amma kayi musu banza ba dadi fa”
“to mezan musu? Ko sokike in sauka in tsaya ina surutu?”
“A’a bahakaba at least ko daga musu hannu kayi”
Be kuma kulataba ya cigaba da tukinsa,
Sarkar wuyansa ta kalla, sekace ba ďan musulmi ba, “Kafasa tafiyar dai ko?”
“baki yadda dame na fada bane?”
“A’a ni banceba, Amma dan Allah kadena yi wa Mummy abunda kake mata, dan Allah”
“Waike ba Adda tagaya miki komai game da rayuwata ba mekikeso inyiwa Mummy?”
“Bahaka bane ba, inka mutu tana fushi da kai Allah ma zeyi fushi da kai, kila sanadiyar yafemata kaga Allah ya daidaita maka Al’amuranka, mutane zasu dena kyamarka”
“Anya Al’amurana zasu gyaru? Mutane bazasu taba sakin jiki daniba kowa ya riga ya gujeni se kalilan din mutane”
“Al’amuranka zasu gyaru inkaso mana”
“Ta yaya?”
“I will help you do that, sekowa ya dawo yana sonka”
“how?” ya tamabayeta a takaice
“Just believe me, you Can change, I will help you change your life, trust me”
Kallonta yayi sannan yai murmushi “I have trust you already, ko iya haka you bring a lot of changes in my world, Thank you”
“kasan wani abu daga lokacin da ka kasance tareda abunda kakeso lokacin kake kara samun nutsuwa da kusanci zuwa gareshi, Iyaye abun sone, dakana kokarin ka manta abunda Mummy tayi maka ka kyautata mata wataran zaka manta da komai”
“bazan manta ba kuma ni yadda take kara cusamin Ilham ke batamin rai”
“wai me Ilham tayi maka haka?”
Kallon Jalila yayi irin kin rainamin hankali
“kinsan komai amma kina rainamin hankali, lokacin dana kwanta a Asibiti kikace musu ina bacci, sunsaki baki itada mahaifiyarta naji duk abunda suke cewa kuma kina tambayta me tayimin bansaniba”
Dauke kai tayi ta danyi murmushi.
Suna shigowa bakin layin suka ga wani dattijo yanata tattare ledojin da suka dan bata layin, da Sauri tacewa Jalal ya tsaya
“me zakiyi?”
“Kaga dattijon can zamu tsaya mu gaisar kaimasa Alheri”
“saboda me?”
“Maganar me mukayi dazu, you want change”
Hade rai Jalal yayi “Wannan mutumin ba irin zagin dabemun ba farkon fara shaye2 na”
“kayi hakuri ka nuna masa ka manta please”
Jalal yaja motar suka karasa inda dattijon yake suka gaisa sukayi masa sannu da aiki, sannan Jalal ya dakko dubu daya ya bashi yasa hannu ya karba ya dinga godiya sannan suka wuce,
“Kiduba Ajiyata dana gaya miki”?
Ya jefo mata tambayar, Jalila bata son rigimadsa tasan intace Ilham ta dauka fada zasuyi dan haka tace
“Wace Ajiyar fa?” ta tambayeshi irin ta manta din nan
Ya gano so take ta raina msa hankali dan haka ya kyaleta yayi parking Akan idon Ilham Jalila ta fito daga motar Jalal.
Ilham aranta tace “dama tazo dazan bakantawa Jalila insa a tsanate” dan haka Ilham da gudu ta shiga cikin gida tana kwalawa Mummy kira ta samu Mummy a daki idonta yayi Ja saboda kuka tana lazimi
“Mummy wallahi Jalal bashida mutunci bashida Imani, duk yadda kikayi kina kuka bakyason ya tafi seda ya tafi, gashinan a banza mace tasashi ya dawo yafasa tafiyar, wallahi gaskiyar daddy Jalal neman mata yakeyi”
Cikin rashin fahimta Mummy tace “Ke bangane me kike nufi ba”
“Mummy Jalal yadawo be tafi ba saboda Jalila”
“Kamarya saboda Jalila?”
“Oho musu dai, wallahi gashi can shida Jalila sun dawo, saboda ita yafasa tafiyar”
“ke ya akayi kikasan saboda ita yaki tafiya?”
Ilham ta gyara zama tace “Mummy nifa shiru kawai nakeyi, Allah kadai yasan abunda nake gani a tsakaninsu, bana son yawan bata miki raine”
A fusace Mummy tace “Ilham bana son shirme da shashashanci, kimin bayani yadda zan gane, ban fahimci ke kadai kika san abunda kike ganiba kimin bayani”
“Wallahi Mummy ba tun yauba akan yarinyar nan bakiga rashin mutuncin da takemin ba, kuma wallahi ita take ziga shi yakemiki wani rashin mutuncin, har dakinsa take zuwa gurinsa, Allah kadai yasan me sukeyi”
Mummy tayi shiru tace “lallai yarinyar nan makira ce, agaban idona take bude baki tacewa Jalal mara tarbiyya, Ashe itama mara tarbiyya ce, tunda take biye masa suna lalacewa, wallahi bata isaba dole in nesan tata da dana, dan bazan zuba ido yana ta’amalli da itaba, akan me na yadda da ita ina mata kallon mutuniyar kirki amma zatayi min haka? Gaskiyar dsddynsa yana neman mata kenan inbahakaba uban me take zuwayi dakinsa, kema banda rashin mutunci ubanme ya hana ki gayamin abun tun farko”
” Mummy dan Allah kiyi hakuri, kawai nidai bana son ki tayara da hankalinki ne a zatona zan iya shawo kan abun, tunda naga abunda yafaru yau kalli banbamin dayake miki dankice kar ya tafi, Amma dayake akwai abunda sukeyi ai baze iya hakura ya tafi ba, yanzu ki kwantar da hankalinki kawai dai kiyi kokari ayi mana Aure da shi a wuce gurin “
” Ke kina batun inyi kokari ke wani kokarin kikayi?, tsawon shekaru kina gidan nan amma kinkasa janyo hankalin sa, Amma kanwar kanwarki wannan ‘yar yarinyar hartasan taja hankalinsa duk taurin kansa, da uwar me tafiki? Niba ina nufin ki zubar da mutuncinki ba amma abun ya dauremin kai, ace har taci mutuncinsa agabana amma dayake bashida zuciya har tasamu kusanci dashi fiye dani da kema gaba daya Kinga tashi kibani guri ni raina ya gama baci”
Ilham ta mike ta fita tana zunbura baki, Amma dai tayi Nasara tunda har Mummy tafara daukar zigarta ta harzukata haka yanzu saura next plan dinta.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122 123 124 125 126 127 128 129Next page

Leave a Reply

Back to top button