ABDUL JALAL PART 2

ABDUL JALAL PART 2

Godiya mara iyaka ga members na kungiyar mu me tarin Albarka Perfect writers association, Allah yakara haďa kanmu.
Abdul Jalal Novel Fans❤️???? kaunarku a ruhina take, inajin dadin comments dinku hada wakokin da’ake reramin????????????
Masu bina private suna min comment kokuma bani karfin gwiwa, da masu biyoni suna neman littafina da masu karantawa wanda bansansu ba ina godiya Allah yasaka da alkhairi Allah yabar kauna.

Share please
I want comments not stickers or just thanks
Daga alkalamin Aysher cool
????️????️????️????️????️????️????️????️????️????️

What’s app only 07063065680.

    ????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????


             *ABDUL JALAL*

Story and writing
By
AISHA HUMAIRA
( Daddy’s girls)

PERFECT WRITER’S
ASSOCIATION????

(???????? ????????ℕ’???? ℙ????ℝ????????ℂ???? ???????????? ????????’ℝ???? ????????????????????????, ????ℝ????????ℕ???? ????????ℝ ???????????????? ???????? ???????????????????????????????? ????ℕ???? ????ℕ????????ℝ????????????ℕ ????????ℝ ℝ????????????????ℝ????????)

/https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/

         *P.W.A*✍️


PART 2         
                      _PAGE  4️⃣0️⃣93

Bismillahirrahmanirrahim, da sunan Allah me rahama me jinkai, Allah yakara tsira da aminci ga shugabanmu Annabi muhammadu salallahu alaihi wassalam.
Bayan haka bazan gajiba da mika gaisuwata da godiya ga yan uwa da abokan arziki ba, bayan haka
Banyarda a juyamin littafi ba ko amfani da wani bangare ba tareda izinina ba.
Domin gyara, shawara ko sharhi, za a iya tuntubata akan what’s app number dina
07063065680
Or email address @ www.humaira17@gmail.com
Watpad @Ayshercool7724

      _MY FIRST NOVEL _

Tsayawa Mummy tayi tana kallonsa, yace “ki dauka kiduba mana, kika tsaya kina kallona, ganin da yayi Mummy bata da niyyar taba jaridar yasashi yasa hannu ya bude ya ajiye mata a gabanta,
Hoton Kabir ne da Jeje da wasu mutane da bindigogi agabansu, tittle din ta karanta, da hanzari jikinta na rawa ta dau jaridar tafara dubawa, an yankewa Kabir zaman gidan yari na shekaru goma sha biyar sakamakon saida makamai da fataucin miyagun kwayoyi, sannan an yanke masa shekaru Ashirin a prison saboda Yunkurin kisan kai, da kuma shekaru goma sha hudu sakamakon lalata da kanan yara mata.
Sekuma su Jeje da’aka yankewa hukuncin shekaru ashirin2 a gidan prison.
Daddy ne yasa hannu ya karbi Jaridar shima ya duba, Jalal yace
“Mummy Allah yakawo karshen mutumin da dasa hannunsa a lalacewata, shiyabada kwangilar koyamin shaye2 saboda ya huce takaicin abunda kikayi masa akaina, kalli keda laifi nida karbar hukunci”
Daddy yace
“Jalal kai waya gayamaka shiya bada kwangilar hakan?”
“ba gayamin akai ba, Jeje abokina yaronsa ne, idan nagaya muku wanda yayi sanadiyar kama Jeje da uban gidansa har nasan wannan lamarin kila karyatani zakuyi, sanin hakan bashida Amfani, Mummy yakamata ki zubar da makamanki kikoma ga Allah tun kafin kema ya dankeki, Kabir makiyinane na boye bansan dashiba sedaga baya, nasan makiyana na fili, suma ina nan nasasu a Addu’a very soon Allah ze yimin maganinsu”
Yasa hannu ya dauke Jaridar ya fice.
Daddy yaja ajiyar zuciya yace “Khadija lokuta da dama bana ganin laifin yaron nan, ba wai ina goya nasa bayane ba, amma kinmasa laifuka masu tarin yawa, ba kya duba haka se wanda yakemiki, anyway Ansamosa aikinyi na gwamnati wanda muke saka ran ze dauke masa hankali daga kan shaye2”
Kallon Daddy tayi tace “bangane ansamosa aiki ba, wani irin Aiki? Me Jalal yanema yarasa da zeyi wani aiki, ina kamfaninsa na sarrafa robobi meyasa bazaka bashi abunsa ya rike ba?”
“ba an samomasa aiki ne dan wani abuba, ansamo masa ne dan hakan zesa yayi kokarin dena shaye2, kuma bazan iya cewa wanda yasamo masa din A’a ba, kuma nima naga dacewar hakan”
“wai waye ya samo masa?” ta tambaya cikin kosawa
“General Abdurasheed ne”
Dan zare ido tayi tace “Ina yasanshi daze bashi aiki, sannan wani irin aikine haka? Dan dana baze aikin soja ba”
“Eh ya gayamin Jalila ce tace tanason yasama masa aiki a NDLEA, hakan ze temaka masa wajen dena shaye2”
Hade rai tayi sosai tace
“Baze yuwu ba, baza’a mayar minda ďa bawa ba,
Akan mene? Meye hadinta dashi dazata sa a samo masa aiki, banda cin mutunci tasan yana shaye2 shine zatace yayi aiki a hukumar yaki da shaye2 salon tasaka akama shi, kokuma taji dadin juya shi yadda takeso ko? Dama yanzu na fuskanci maganarta yakeji akanta ba irin wulakancin daba yawa Ilham, to bata isaba da raina babu yarinyar dazata juyamin ďa, baze yuwu in haifi ďa wata ta juyamin shiba”
Mikewa daddy yayi tareda yin murmushi yace “Eyya kin makara khadija, duk abunda kayi se an maka, ki gode Allah da yarinyar ba cutar dashi take ba, dan ta damu da halin dayake cikine hartasa a sama masa aiki, nayi farinciki da hakan, kuma batun kice baza’a juya miki ďa ba daga baya kenan aikin gama ya gama” be jira yaji martanin da zatayi ba ya shige bedroom ya kulle kofarsa.

Jawwad ko sallama basuyi da Jalal ba suka tafi bauchi shida Abba.
Maama kam a sukwane take tambayar Jalila “me Abba ke nufi, me kika gaya masa haka? Sannan wa zeje nemawa Aure?
“niba abunda nagaya masa, yaushe rabon da in zauna dashi balle ince masa wani abu, nibansan waze nemawa aure ba be gayamin ba”
A fusace Maama takoma dakinta tana tunanin yazata bullowa lamuran.

Jalila takoma daki suka dinga murna itada Nana, Jalila tace “Nana ban taba zaton Abba ze yadda da abunda nagaya masa ba”
Dan bata rai Nana tayi tace “Jalila nayi mamakin abunda ya fusata Abba haka, har yayi fushi yake ikrarin abar masa gida, nayi mamaki sosai be taba hakaba fa”
“to yanayi na rayuwane Nana, tunda kikaga haka akwai abunda ya bata masa raine, sannan akwai dalilin dayasa yayi haka”
Nana ta dan numfasa tace “Jalila nifa damuwata naji Abba yana batun akawo kudin Aurena, Allah yasa ba dana Yaya Jawwad za’a hadamin ba, nan da wata hudu da ‘yan kaifa kenan”
Nana takarasa maganar kaman zatayi kuka
Jalila tace “to meye aciki? Keda rabin rankine fa Mahmud zaku kasance inuwa daya”
“To Jalila karatun fa? Kinsan Mahmud a kasar waje yake nasa karatun tayaya abun ze yuwu?”
“ze yuwu mana, kicigaba da naki karatun a can riba biyu, Allah sarki Rayuwa hajiya Nana za’a zama matan Aure, bari in lissafa yaushe zaki haihu”
Hade rai Nana tayi “Ke Jalila komai sekin sako wasa a cikine? Inamiki maganar serious kinamin wasa, ke yanzu akace za’ayi aurenki nan da watanni hudu kin shiryane? Ni yanzu ma meyasa Abba bece a hada dake ba”
Dariya Jalila tayi tace “gidan Ahmad yana bauchi, shi yana aiki a maiduguri, ni ina karatu a kano tayaya kike zaton inyi Aure yanzu, se nagama tukuna”
Wayar Jalila tafara ringing, ta kalli Nana tace “Excuse me, let me pick the call”
Nana ta daga mata kai, Jalila ta amsa wayar tareda yin sallama
Amsamata yayi sannan ya dora da “Babyna kwana biyu kin gujeni you are not picking my calls, ina fatan ba laifi nayi miki ba?”
Cikin siriyar muryarta na shagwaba tace
“Ohh no ni bakamin laifi ba, bana dan jin dadine kawai, amma yanzu Alhamdilillah naji sauki”
“Ya salam amma baki gayamin ba, yau zan shigo kano dama shiyasa na kiraki, in kin amince zanzo in ganki”
“Babu damuwa my one, ina fatan in ganka nima am missing you”
“Like serious, karkisa inyi Ihu attention din mutane ya dawo kaina”
Murmushi tayi tace “ba sekayi ihuba, aini yakamata inyi, kwana nawa zakayi a kano?”
“zanyi sati daya Insha Allah, zanyi wani assignment ne”
“Shikenan Allah yakawo ka lafiya”
“Ameen my queen, bazaki tambayi Antynki ba?”
Dan yamutsa fuska Jalila tayi tace “Ainasan tana lafiya tunda najika haka”
Murmushi yayi yace “Queen da alama kinada kishi sosai, anyway sena shigo, idan nazo da wuri zaki ganni yau, in ban shigo da wuri ba se Allah ya kaimu gobe”
“to shikenan Allah ya kaimu, take a good care of your self”
“Ok Baby i will Insha Allah” ta katse wayar, Nana ta zuba mata ido tana kallonta, Jalila tace “Madam lafiya kuwa?”
“Lafiya mana, nina kasa gane inda kika dosane, gane lamarinki se Allah mutum baya taba ganeki, gaba daya rayuwarki zigza ce”
Sosai Nana tabawa Jalila dariya tace “rayuwartawa ce zigza, lallai ma Nana bakida dama, Rayuwata normal ce kaman ta kowa”
“A’a ban yadda ba, Allah yasa ayi miki aure kafin ayiwa Yaya Jawwad”
“Ba Ameen ba, back to sender muguwa kawai”
“eh amma ni kikayimin fata saboda son kai”
Wayar Jalila ce takuma daukar ruri, ta kai hannu ta dauka tana dubawa taga Hanan ce dan haka ta kashe wayarta.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122 123 124 125 126 127 128 129Next page

Leave a Reply

Back to top button