ABDUL JALAL PART 2

Maama takasa zaune takasa tsaye, Naja batasan budurin da’akeba dan lokacin da Abba yayi wannan maganar bata nan tafita yawonta, harta dawo Maama tarasa ta inda zata fara mata bayani.
Jalila na fitowa taga Jalal ya dawo a mota, yana kokarin shiga gida, ganin da yayi ta tsaya ta ki tafiya ta kura masa ido yasan akwai magana a bakinta, tsayawa yayi agaban ta yayi parking, yana tsayawa ta zagaya inda yake, ďan ďage mata gira yayi alamar meke faruwa?
Ďan kallonsa tayi tace
“daga ina?”
“kin aikenine?” ya tambayeta
“Ohh No Allah yabaka hakuri”
Yace “Ina Jawwad ne? Na duba baya nan ban san inda ya tafiba?” hade rai tayi itama tace
“ka duba shi mana, kokabani ajiyarsa ne?”
Kallonta yayi, wato ta rama kenan
Yace “A’a ban baki ajiyarsa ba”
“dama..” sekuma tayi shiru
“Dama me?”
“inada magana ne”
“fadi ina jinki”
“toka fito daga motar mana”
“In fito kuma? Gaskiya ni yunwa nakeji, zuwa zanyi in kwanta, naje neman Abinci narasa me zanci, dama in kin bawa Jawwad nake ci nima amma yanzu baya nan nasan bazan samuba”
“Hmm to kace Ilham tabaka mana”
Hade rai yayi sosai yana Kallonta, sunkuyar da kai tayi tana dariya kasa2
“Yi hakuri, ai yanzu mundena faďa ka jirani a part din Yaya Jawwad zan kankaro maka kanzo in za kaci” tayi maganar tana dariya, tana matukar kyau idan tayi dariya, gyaďa kai yayi ta juya ta tafi, yabi bayanta da kallo harta shige gida, sannan yaja motar ya shiga da ita gida.
Gida takoma taje ta ďakko masa breakfast ďin Jawwad da yatafi beci ba, dayake da zafinsa a cikin flask, tana zuwa ta tarar dashi a zaune a palourn Jawwad yana jiranta, ta shiga tayi sallama amma be amsaba, seda tazo kansa ta tsaya takuma yimasa sallama ya ďago ya kalleta ya amsa a hankali, ta ajiye tray din tace
“Yana daga hakkin musulmi akan musulmi in yayi sallama ka amsa masa, kadinga amsa sallama please”
Shiru yayi yaki kulata, Jalila tarasa wane irin miskilin mutum ne Jalal, koma tace ďan rainin hankali kana masa magana yana jinka amma yayi maka banza dan tsabar wulakanci,
ta aje masa Abincin ta zauna a kujerar dake kallonsa. Ta danne fushinta
Ya hada Abincinsa yafara ci, can yace “Me ya kai Alqur’ani dana baki hannun Ilham?” yai tambayar kamar bashi yayi ba
“ďauka tayi” tabashi amsa a takaice
“Ya’akayi ta ďauka baki hanata ba?”
“Ina bauchi aka aikota taganshi shine ta ďauka”
Bekuma cewa komai ba yacigaba ds auna loma, can Jalila tace
“Ya akai kasan yana gurin ta?”
Kallonta yayi ya danyi murmushi
“in kinaso in dawo miki dashi, yana gurina, amma bakiga abunda na ajiye a cikiba ko?” ďan yatsina fuska tayi sannan tace
“Nifa tsawon lokacin da yayi a gurina banga komai a ciki ba”
“zan dawo miki dashi kikuma dubawa”
“to naji zan duba”
Ya cigaba da cin Abincin sa, can ta ďan nisa tace
“An baka aiki ance kaje interview kaki why?”
Ďagowa yayi ya kalleta, “dama nayi tunanin kece kikasa aka nemamin wannan aikin, tayaya ina shaye2 zakice asamomin aiki a hukumar dake yaki da shaye2, amfanin me zanyi ko nima so kike a kamani?”
“calm down let me explain, mezesa in so akamaka? da hakane naso akamaka da nasa an ka maka kaida abokinnaka jeje ai”
ďagowa yayi ya haďe rai kaman be taba dariya ba
“Am sorry banyi hakan da wata manufa ba, sedai inkana aikin na farko ze rage maka yawan damuwa, sannan ze sa ka kara kokarin kadena shaye2 kaima, at least in kana da gurin zuwa ze kara dauke hankalin ka daga kan Shaye2”
Zuba mata ido yayi yana tunani daban2 akanta, ta damu dashi dayawa, she’s so simple and calm, matsalarta kawai taurin kai da rashin kunya, Amma tanada zuciya me kyau.
Tsarguwa tafara yi da kallon dayake mata tace
“Ya dai?”
“meyasa kika damu dani haka?”
Shiru tayi dan bata san mezatace masa ba, basarwa tayi tace
“dan Allah kaje interview din nan karka watsamin kasa a ido”
“Senayi shawara” yabata amsa
“shawara kuma, dan Allah mene kuma na wani shawara dan Allah Yaya Jalal kaje please karkasa inji kunya” da shagwaba takarasa maganar
Bude baki yayi tareda yin murmushi kaman karta dena magana
“Nine Yaya kuma yau, yarinyar bakida kunya fa”
“Aida ďinma dan muna fada ne amma yanzu mundena faďa, dan Allah kaje ba dan halina ba, kaji Yayana ďan gidan daddy abokin Yaya Jawwad, badan halina ba” murmushi yayi ya ďan girgiza kai yace
“Aikuwa kinsan indan halinkine bazaniba, innayi tunani zan gaya miki”
“to Allah yasa inji alkhairi”
Be amsaba ya kai hannu ya dauki cup ya kai bakinsa amma jikinsa yafara rawa yakasa kaiwa
“lafiya menene kuma?”
Ajiye cup din yayi, yai shiru yana rintse ido”
Da sauri ta mike ta nufi inda yake tana faďin “Subhanallah meyafaru?”
Dagowa yayi idonsa yayi jawur yace
“Gi.. Giy….. Giya,…. Giya zansha, ita nakeson sha”
“giya kuma? Meyasa zaka sha giya?”
Numfashi yake ja ya mike tsaye ya nufi hanyar fita, idonsa yayi jawur jikinsa se rawa yakeyi da sauri ta sha gabansa
“dan Allah Jalal karka sha giya, meyasa idan kuma kasha ka bugu daga nan ka mutu mezaka cewa Allah? Dan Allah karka sha kayi hakuri zaka ji bakason sha”
Tureta yayi ze fita, takuma tare kofa tana masa magiya, yasa hannu ya hankadata jikin kofa ta bige kafaďa ta faďi a gurin shikuma ya fice kaman wani horrorn dayake bukatar jini.
Godiya mara iyaka ga members na kungiyar mu me tarin Albarka Perfect writers association, Allah yakara haďa kanmu.
Abdul Jalal Novel Fans❤️???? kaunarku a ruhina take, inajin dadin comments dinku hada wakokin da’ake reramin????????????
Masu bina private suna min comment kokuma bani karfin gwiwa, da masu biyoni suna neman littafina da masu karantawa wanda bansansu ba ina godiya Allah yasaka da alkhairi Allah yabar kauna.
Share please
I want comments not stickers or just thanks
Daga alkalamin Aysher cool
????️????️????️????️????️????️????️????️????️????️
What’s app only 07063065680.
????????????????????????
ABDUL JALAL
????????????????????????
PERFECT WRITER’S
ASSOCIATION????
(???????? ????????ℕ’???? ℙ????ℝ????????ℂ???? ???????????? ????????’ℝ???? ????????????????????????, ????ℝ????????ℕ???? ????????ℝ ???????????????? ???????? ???????????????????????????????? ????ℕ???? ????ℕ????????ℝ????????????ℕ ????????ℝ ℝ????????????????ℝ????????)
/https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/
_*Story, &writing*_
and edited
By
AISHA HUMAIRA
( _Daddy's girl_)
P.W.A✍️
PART 2️⃣
_PAGE 4️⃣1️⃣94
Bismillahirrahmanirrahim, da sunan Allah me rahama me jinkai, Allah yakara tsira da aminci ga shugabanmu Annabi muhammadu salallahu alaihi wassalam.
Bayan haka bazan gajiba da mika gaisuwata da godiya ga yan uwa da abokan arziki ba, bayan haka
Banyarda a juyamin littafi ba ko amfani da wani bangare ba tareda izinina ba.
Domin gyara, shawara ko sharhi, za a iya tuntubata akan what’s app number dina
07063065680
Or email address @ www.humaira17@gmail.com
Watpad @Ayshercool7724
_MY FIRST NOVEL _
Jalila ta bugu sosai, ta rike hannunta tana rintse ido saboda azabar zafi, shikam yasa kai ya fice yabar dakin.
Ta dade a gurin a zaune, sannan ta mike ta koma cikin gida tana yamutsa fuska.
Su Jawwad kam har la’asar sannan suka isa Bauchi, Abba yakira daddyn Hanan a waya yagaya masa sun karaso, aka turo wasu sojoji sukazo suka tafi dasu har estate din, Ba Jawwad ba har Abba seda yayi mamaki irin tsaruwar da estate din yayi sekace barrack duk inda ka juya sojoji ke shawagi a ciki, akai musu Jagora zuwa gidan daya kasance nan ne center.
A dankareren dakin Daddy akayi musu iso, da murna daddyn Hanan ya tarbi su Abba, suka gaisa yai musu barka da zuwa, seda suka fara gabatar da salla sannan daddy yai umarnin akawo musu Abinci.
Wasu matasan ‘yan matane dabasu wuce sa’ anin su Hanan ba su uku suka kawo Abincin suka ajiye, tareda gaida Abba da Jawwad, ďaya daga cikinsu wadda da gani kasan hutu da jin dadi ya ratsata tace
“daddy wannan yana matukar kama da Yaya Yusuf, ko shine sirikin naka?” Jawwad ya sunkuyar da kai saboda kunya
Daddy yace
“kaniyarki yusra, sarkin surutu, tunda kunkawo Abincin kukoma, ki gayawa Inna bakin sun iso zasu shigo anjima su gaisheta”
Murmushi Yusra tayi tace